Fassara

Sunday, December 11, 2016

Wane Irin So Muke Wa Manzon Allah (SAW)?

10 Ga Disamba, 2016

Daga: Amir Abdulazeez

A
llah (SWT) cikin hikimarSa da SahalewarSa Ya ƙara zagayo damu wata shekarar kuma mun riski watan Rabiul Awwal, wanda a cikinsa ne aka haifi fiyayyen halitta Annabi Muhammadu (SAW). Kusan kamar yadda ya kan kasance a mafi yawan shekaru, taƙaddama ta kan kaure a kan halaccin maulidi ko rashin halaccinsa, dacewa ko fa’idarsa da rashinsu. A cikin masu wannan taƙaddama kowanne yana da madogara ko hujjarsa da yake ganin ita ce karɓaɓɓiya. Abin farin cikin dai shi ne, kowanne ɓangare yana son Annabi Muhammadu, saɓanin kawai shi ne hanyar da za a bi wajen nuna soyayyar. To amma, duk ba ma wannan ba tukunna, tambayar da ya kamata mu tsaya mu yi kanmu a matsayin al’umma, ita ce wane irin so muke wa Manzon Allah kuma me aiyukanmu suke cewa game da son da muke cewa muna masa?

Wannan tambaya ta zamar mana kusan wajibi duba da yadda kullum son Annabi yake ƙaruwa a baki a cikin al’ummarmu, amma kuma kullum bijire wa koyarwarsa take ƙara hauhawa. Yanzunnan za ka ga an yi kare-jini-biri-jini da mutum a kan halacci ko rashin halaccin maulidi, amma anjima kaɗan in ka ba shi amana sai ya ci, in kai alƙawari da shi sai ya saɓa, in yai magana sai yai ƙarya. Ko kuma yanzu mutum zai ɗauki littafin Sahihul Bukhari ƙato ya tafi karatu, ya shafe awanni ana biya masa hadisan Manzon Allah, amma a kan hanyarsa ta dawowa zai fara cin naman mutane.

Kowacce shekara guraren yin maulidi ƙaruwa suke yi, guraren karatuttukan hadisan Manzon Allah ƙara yawa suke yi, masu waƙe ko bege na yabon manzo ƙaruwa suke yi, amma kuma kullum lalataciyyar mu’amala da munanan halaye irin waɗanda Manzon Allah ɗin ya hana sai ƙara samun gindin zama suke yi. Tambayar da ya kamata mu yi wa kanmu, wai shin son Manzo Allah ɗin ba shi da alaƙa da koyi da shi ne?

A wannan al’ummar da muke ciki, akwai waɗanda suke ikirarin sun yarda da alƙur’ani amma basu ma yadda da fassarar da Manzon Allah Ya yi wa alƙur’anin ba wato hadisai, kuma suna nan a tsakaninmu suna kiran kansu masoya Manzon Allah. Mutanen dai da ka ce sun yi ƙarya da suka rawaito hadisi, sune dai suka adana ƙur’anin har ya zo gareka; ko kuwa a gun Manzon Allah ka samu ƙur’anin kai tsaye? Mutumin da baka yarda da fassarar da ya yi wa alƙur’anin da aka saukar masa ba sai fassarar da ka yi wa kanka, shi ne kake ƙauna? Wacce irin ƙauna ce wannan? A wannan al’ummar ne, ake zagar wa Manzon Allah iyalansa, abokansa, shaƙiƙansa, amintattaunsa da masoyansa a filin Allah. Masu yin hakan suna nan a tsakaninmu kuma wai su ma masoyansa ne.

A wasu sassa a ƙasar Hausa, al’ada ta fi sunna daraja domin sai al’ada ta hana aure, sunna ba ta hana ba. Duk mu’amalar da ka ɗauka a wannan zamanin da muke ciki sai ka ga mafi yawancin yadda ake gudanar da ita ya saɓa da tsagwaron abin da Annabi ya koyar. Tun daga kan aure, kasuwanci, zamantakewa, mu’amala da sauransu. Ba wai ana nufin babu nagari ba ko babu masu koyi da Annabi a aikace ba; a’a, ana nufin gamayyar halayyar al’umma.

Wani babban kuskure da masu yawa daga cikin al’ummar Musulmi, musamman na ƙasar Hausa suke yi shine, na ɗauka da suke yi cewar son Allah da Manzonsa a baki shi ne kawai abin da ake buƙata, to amma akwai sauran abubuwa na aiki masu tarin yawa da matuƙar amfani, waɗanda rashin kiyayaesu zai iya kawo babbar alamar tambaya dangane da nagarta ko ingancin son da kake wa Allah ko manzonSa.

A abubuwan da Manzon Allah ya siffanta da su na kyawawan  halaye, kaɗan daga cikinmu ne suke ƙoƙarin kamantawa. A abubuwan da yake fushi da su, kaɗan daga cikinmu ne basu tsunduma tsamo-tsamo a cikinsu ba. Wannan shi ne halin da muke ciki.

Masana binciken halayya da ɗabi’un ɗan Adam sun yi ittifaƙin cewar ‘yan Najeriya musamman Hausawa suna daga cikin mutane da suka fi kowa nuna son Annabi a fili a Duniyar Musulunci, an yarda cewar Hausawan Arewacin Najeriya suna daga cikin waɗanda suke ƙoƙarin yin maulidi da hidindimu. To amma kuma sai dai kash! Idan da za a auna, da sai a gano cewar miyagun halaye da gurɓataciyyar mu’amala ta yi mana katutu. Wannan ƙalubale ne ba ƙarami ba a kanmu domin kuwa duk wanda yake ikirarin abu, to alamun wannan abun gaskiya ne, shi ne a gan shi a aikace.

Gurɓacewar mu’amalarmu da yanayin zamantakewarmu a yanzu ta kai ta kawo muna zaune cikin rashin ‘yan uwantaka. Idan jifa ya wuce kanka, to ya faɗa kan kowa. Ba ka gudun ka yi wa mutane abin da kai baka so a yi maka. Muna zaune kullum neman juna muke da sharri ba alkhairi ba. Kowa so yake kowa ya aikata kuskure ya yi ta faman yamaɗiɗi, amma idan an yi alkhairi sai ka ji gum. Kowa tsoron yin harkar kuɗi yake yi da  kowa. Wannan masifa har ina? Koyi da Manzon Allah a haƙiƙance ba a baki ba, shi zai yi mana maganin wannan.

A cikin jama’a, idan ana zaune, har ƙagara ake yi mutum ɗaya ya tashi a saka faifansa, a fara zaginsa ana cin namansa. Ƙarya kuwa ta zama ita ce mafi akasarin zancenmu. Duk maganar da aka faɗa, kowa zai karɓe ta ne cikin shakku da zargi. Idan an faɗa maka farashin abu a kasuwa, gani kake cutarka za a yi. Babu aminci a tsakaninmu. Cin amana a kasuwanci, zamantakewa, aiki, maƙotaka, abota, duk ba wani baƙon abu ba ne a cikin mu’amalar mutanen wannan zamani.

Da ka taɓa mutane, sai su ce sun fi kowa son Annabi, amma kuma a halayyarsu babu irin ta Annabin. Annabi Muhammad (SAW) shi ne mutumin da ya fi kowa iya mu’amala a tarihin duniya, kuma shi Musulmi ne, da shi aka ce Musulmi su yi koyi. Ina koyin yake?

Idan muna buƙatar son da muke yi wa Annabi ya zamo abin gaskatawa da amfanarwa, to sai mun gyara zuciyoyinmu, addininmu, halayenmu da zamantakewarmu ta hanyar yin koyi da dukkan halayensa da kuma ƙauracewa abubuwan da ya hana. Idan ba haka ba, yawan maulidinmu ko sauraron wa’azinmu ba zai kaimu ko’ina ba. Allah ya bamu ikon gyarawa.

Shafin Mallam Amir a Twitter shi ne: @AmirAbdulazeez  

Wednesday, October 12, 2016

Siyasar Bambaɗanci da Makomar Matasanmu

06 Ga Oktoba, 2016

 Daga: Amir Abdulazeez

C
ewar babu abinda ɗan siyasar wannan zamani ba zai iya yi ba saboda buƙatarsa, kullum ƙara bayyana yake yi a fili ƙarara. Ba wai sata, ƙarya, munafirci, rashin kunya ko maguɗi ba, a’a da yawa daga cikin ‘yan siyasarmu na wannan lokaci, a shirye suke su lalata rayuwar ‘ya’yan da ba nasu ba wajen ganin sun samu biyan buƙata ko kuma an ci gaba da kare musu muradinsu ko ta wane hali kuma komai lalacewar hanyar da za a bi wajen kare musu muradan nasu.

Duk mai lura da yadda al’amuran yau da kullum suke gudana, zai fahimci cewa an samar da wani sabon salo na wofantar da matasa da mayar dasu mabarata ko maroƙan ƙarfi-da-yaji. Irin waɗannan matasa suna shiga gidajen rediyo da sauran kafafen yaɗa labarai, amma dandazonsu ya fi yawa a shafukan sada zumunta na yanar gizo; shafukan da suka haɗa da Facebook, Twitter da dai sauransu. Irin waɗannan matasa basu da aiki sai tumasanci da bambaɗanci ga ‘yan siyasa da masu mulki. Irin wannan salo na tumasanci, kusan bamu taɓa ganin irinsa a ƙasar Huasa ba; ko maroƙanmu irin na da waɗanda basu da sana’a sai roƙo basu yi irin abinda ake sa waɗannan matasa suke yi a yanzu ba.

Rahotanni masu tushe sun bayyana cewar ‘yan siyasa a jihohin Arewacin Najeriya har ma da kudancin, yanzu sun ɗauki ɗabi’ar saya wa matasa wayoyi ko komfutoci da basu kuɗi lokaci bayan lokaci domin sanya kati domin su dinga shiga yanar gizo suna yi musu bambaɗanci da tumasanci wai da sunan tallatasu ko yabonsu. A cikin irin matasan da aka ɗora a kan wannan wulaƙantacciyar hanya, babu ‘ya’ya ko jikokin su ‘yan siyasar ko masu mulkin. Abin takaici ne matuƙa a ce wai a wannan ƙarni na 21 da kowa yake ƙoƙarin bai wa matasa ilimi da damammakin da zasu zama masu juya duniyar gobe, wasu mutane ko jagorori waɗanda ya kamata su shige musu gaba don tabbatar da hakan, sun koma ɗorasu a kan tafarkin roƙo, kwaɗayi, cin mutunci da wofantar da kai wai da sunan siyasa. Wani abin haushin kuma shine, su ‘yan siyasar masu yin wannan, ba haka magabatansu suka yi musu ba; hasalima, ba dan magabatan nasu sun ɗorasu a kan hanya mai kyau ba, da basu zama abinda suka zama ba a yanzu.

Akwai matasan da  a yanzu dare da rana, basu da aiki sai shiga kafafen sada zumunta suna zubar wa da kansu da gidajensu mutunci wai da sunan tallata masu mulki. Wanda kuma ba ya yin haka kuma ya zaɓi ya kare mutuncinsa, to kallonsa ake yi a matsayin maƙiyi ko ɗan adawa. Kullum kwanan duniya, in dai kana raye a Najeriya, zaka yi ta ganin abubuwa na rashin hangen nesa da sanin ya kamata iri-iri. Wani abin tun kana gane dalilin yinsa har sai kanka ya ɗaure ka koma baka fahimtarsa kwata-kwata. Mun koma, bama son dai-dai kuma bama son gaskiya; wanda ya yi gaskiya ko ya dage sai an yi dai-dai sai a mayar da shi mujiya a cikin tsuntsaye. Haka zamu ci gaba? Muna buƙatar gyara kuwa?

Farko dai dole ne waɗannan ‘yan siyasa su dubi Allah su tuna haƙƙin da yake rataye a wuyansu. A matasyinsu na shugabanni, ci gaban matasannan da dukkan al’umma gabaɗaya ya rataya a wuyoyinsu. Duk lalcewa, in bazasu iya taimakonsu wajen ci gaban rayuwarsu da dogaro da kansu ba, bai kamata su ɗorasu a hanya ta mutuwar zuciya ba. Ya kamata su tsaya tsayin daka su yi aiki tuƙuru wajen kyautatawa al’umma; idan suka yi haka, ba sai sun ɗebi kuɗin jama’a sun biya matasa su yi musu bambaɗanci ba, mutane zasu yaba musu dai-dai gwargwado. Su tuna fa cewar in da a irin wannan tafarki magbatansu suka ɗorasu, to fa da basu zama abinda suka zama ba kenan. Kuma, me zai hana su sanya ‘ya’yansu da jikokinsu su dinga yi musu irin wannan aiki a maimakon ‘ya’yan wasu?

Ya kamata ‘yan siyasa su daina amfani da damar talauci da kuma tsabar kwaɗayi da yake addabar wasu daga cikin jama’ar wannan zamani wajen  mayar da mutane maroƙa wulaƙantattu. Idan kuma ba da amincewa ko saninsu ake waɗannan abubuwa ba, to su taka wa abin burki. Su daina gudun masu faɗa musu gaskiya da basu shawara domin kawo gyara kuma su daina buɗe ƙofa ga ‘yan tumasnci da bambaɗanci.

Matasanmu kuma dole ne fa sai mun yi wa kanmu faɗa mun fahimci manufarmu a rayuwa. Talauci da neman abin duniya ba fa hauka bane; kowa yana son kuɗi amma ba ta kowacce hanya ya kamata a nemesu ba kuma samun kuɗi cikin sauƙi ba shine burgewa ba. Duk mutumin da zai dinga baka ‘yan kuɗaɗe ƙalilan domin ka dinga yabonsa a kafafen sada zumunta, to ba mai ƙaunarka bane. Idan da abin kirki ne ko na ci gaba, to ba kai zai nema ba, ɗansa ko jikansa ko ƙaninsa zai kirawo ba kai ba; ai muna gani sarai ba sai an bamu labari ba. Matasa su fahimci cewar basu da wata martaba a idon ‘yan siyasa ko amfanin da ya wuce irin wannan aiki da ake sakasu kuma da zarar ka gama aikinka, shikenan amfaninka ya wuce.

Tilas ne matasa su fahimci cewar, mai ƙaunar ka ko mai son ɗorewar mutuncinka da ƙimarka ba zai dinga biyanka kuɗaɗe ƙalilan kana zagin wani ko cin mutuncinsa ko kuma shiga wata hanya ta mutuwar zuciya ba. Mu tuna fa mafi yawan waɗannan ‘yan siyasar fa ba finmu suka yi ba, dama ce kawai suka samu, kuma idan da rabo kai ma zaka iya zama kamarsu ko ma ka fisu. Maimakon ka zauna kana yi musu bambaɗanci, mai zai hana ka yi ƙoƙarin zama kamarsu?

Matasanmu su gane cewar babu lokaci mafi amfani a garesu kamar lokacin ƙuruciya ko tashensu; lokaci ne da zasu yi amfani da shi wajen gina kansu da shirya wa ƙalubalen rayuwa, ba wai lokacin da zasu ɓata wajen karewa ko yabon wasu can da ba ci gabansu bane a gabansu. Wannan hanya ba mai ɓullewa bace; idan kunne ya ji, jiki ya tsira!

Twitter: @AmirAbdulazeez  

Monday, August 15, 2016

Najeriya: Sauya Fasalin ƙasa da abin da Gari zai Waya

31 Ga Yuli, 2016


Daga: Amir Abdulazeez
            Twitter: @AmirAbdulazeez

T
un daga shekarar 2007 zuwa yanzu kiraye-kiraye kan a sauya wa Najeriya fasali suke ƙara ƙamari da yawaita har kawo yanzu. Kodayake wannan daɗaɗɗen al’amari ne kusan tun farkon samun ‘yancin kan Najeriya, to amma an yi al’amarin ƙamshin mutuwa a tsawon sama da shekaru 25 da sojoji suka shafe suna mulki, sai dai kuma daga dawowar dimokraɗiyya a 1999, abin ya sake dawowa da sabon salo iri-iri. Mafi yawan masu waɗannan kiraye-kiraye suna ganin cewar fasalin ƙasar a yadda yake a yanzu ba zai bari a samu wani ci gaban a-zo-a-gani ba, waɗansu kuwa suna ganin cewar ƙasar zata ci gaba da tsayawa cak kuma baza ta samu damar magance tarin matsalolin da suke damunta ba har sai an sauya mata fasali.

Duk da cewar kowanne yanki na Najeriya da mutanensa suna da ra’ayoyi da ƙudurce-ƙudurce daban-daban kan maganar sauya fasalin ƙasa, akwai yankuna da kuma wasu ɗaiɗaikun mutane da suka shahara wajen bayyana ra’ayinsu kan wannan batu. Bugu da ƙari kuma, kowa akwai manufarsa da ta bayyana a fili da kuma wacce ya ƙudurce a zuciyarsa dangane da wannan batu. Yayin da waɗansu suke yin waɗannan kiraye-kiraye saboda kishin ƙasa da kuma yaƙininsu na cewa hakan ce kaɗai mafita, wasu kuwa suna yi ne saboda dalilai na son zuciya da ƙoƙarin cin moriyar arziƙin ƙasa da ake samowa a yankinsu su kaɗai ba tare da tsangwama ba.

A gefe ɗaya kuwa akwai waɗandama suke fatan a sauya fasalin ƙasa domin hakan ya kasance wani mabuɗi izuwa wargajewar Najeriya ko ɓallewarsu daga ƙasar. Ko a ƙarshen watan Mayun wannan shekara, ƙungiyar matasan ƙabilar Ijaw sun sanar bayan sun kamala wani taro na kwana guda cewar fafutuka da ta’addanci a yankin Niger-Delta ba zai ƙare ba har sai an samar da damar da zata basu ikon mallakar man fetur ɗin da yake yankinsu. Sanarwar bayan taron ta ci gaba da cewar kodayake tsarin afuwa da tallafi ga tsagerun yankin da Marigayi Shugaba ‘Yaradua ya ƙirƙiro ya taimaka sosai wajen yayyafa wa wutar ruwa, amma wutar ba zata mutu murus ba har sai an sauya fasalin ƙasa.

A Najeriya akwai Gwamnatin Tarayya wacce ita ce uwa-mabada-mama da kuma gwamnatocin jihohi waɗanda Kundin Tsarin Mulki ya sahalewa ‘yancin cin gashin kansu a wasu abubuwa, a wasu kuwa dole ne sai sun yi biyayya ga Gwamnatin Tarayya. Masu son a sauya fasalin ƙasa suna buƙatar a bai wa jihohi ko yankuna cikakkiyar damar cin gashin kansu a siyasance da kuma ta fuskar tattalin arziƙi. Suna so ya zamanto kowacce jiha ita zata sarrafa arziƙinta sannan ta dinga bai wa Gwamnatin Tarayya wani kaso a maimakon tattare arziƙin kasa waje ɗaya a hannun Gwamnatin Tsakiya wacce ita take ɗiban babban kaso kafin ta rarrabashi zuwa jihohi.

Rashin haɗin kai da bambance-bambancen siyasa, ƙabila da addini a Najeriya kullum kusan ƙaruwa suke wanda hakan ya fito a fili daga irin fafutukar da matasan yankin Biafra suke yi na ganin sun ɓalle da kuma wanda tsagerun Niger-Delta suke yi na ganin Najeriya ta kasa cin moriyar arziƙin ɗanyen man fetur da ake haƙowa a yankin. Waɗannan matsaloli su suka sanya masu rajin tabbatar da sauya fasalin ƙasa kullum suke ƙaruwa. A baya bayannan, tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Atiku Abubakar ya yi kira da a sauya fasalin ƙasa. Kafinsa, manyan mutane daga yankin Kudu kamarsu Cif Edwin Clark sun jima suna hanƙoron a sauya fasalin ƙasa ta yadda zasu samu ƙari ko cikakken iko a kan ɗanyen man fetur 100%.

Atiku Abubakar, a ƙarshen watan Mayun da ya gabata, ya bayyana cewar Najeriya a yadda take a yanzu, ba ta aiki yadda ya kamata kuma ƙara wa jihohi ‘yanci da ƙarfi ne kaɗai zai magance wannan matsala. A cewar Atiku, Gwamnatin Tarayya ta fiye girma da ƙarfi kuma dole a yi wa tsarin garanbawul idan ana so a cimma manufofi na ci gaba da haɗin kai. Bayan haka kuma ya bayyana cewar ƙarawa jihohi ƙarfi ba yana nufin yunƙurin wargatsa ƙasa bane kamar yadda wasu suke tunani.

Sai dai kuma wannan ra’ayi a kan takamaiman dalilin da yasa za a sauya wa ƙasa fasali na Atiku ya ɗan sha bam-bam da na wasu da yawa daga cikin ‘yan Niger-Delta. Misali, a taron Makomar ƙasa da aka gudanar a watan Oktobar 2014, kusan gaba ɗayan wakilan Niger-Delta sun bayyana ko dai a fili ko kuma a shaguɓe cewar Najeriya tana ƙoƙarin cinye musu arziƙinsu na man fertur ba tare da kasancewar arziƙin na yankinsu ya amfane su kamar yadda ya kamata ba. Sukace kuma wannan ƙarine a kan gurɓata musu muhalli, ruwa da ƙasar noma da aiyukan haƙar man fetur yayi. Saboda haka, yayin da shi Atiku yake tunanin makomar Najeriya, su makomar yankinsu ce a gabansu kamar yadda yake a gurin kowanne yanki-wato kowa ta kansa yake. Ko a tsakanin ‘yan Niger-Delta ɗinma akwai saɓanin ra’ayi; yayin da waɗansunsu suke so a sauya fasalin ƙasa ta yadda zasu daina raba arziƙin man fetur ɗin yankinsu da sauran jihohi kwata-kwata, wasu kuwa suna so ne a basu tsakanin 50% zuwa 75%. Su kansu ‘yan Arewa, rashin sanin tabbacin makomar da yankin nasu zai shiga idan aka daina raba arziƙin man fetur shi yasa al’amarin yake ɗan basu tsoro.

Duk wannan tataɓurzar da ake yi, ita Gwamnatin Tarayya a ƙarƙashin Shugaba Buhari bata nuna alamun wannan batu yana daga cikin abinda yake gabanta ba. Kwanakin baya, Mataimakin Shugaban ƙasa Farfesa Yemi Osinbajo ya fito ya soki lamirin masu kira da sake fasalin ƙasa. Osinbajo ya nuna cewar ba wai sake fasalin ƙasa ne matsalar Najeriya ko kuma matsalar da ya kamata a sa a gaba ba yanzu. Maimakon haka a cewarsa, kamata yayi a goya wa shirin gwamnatinsu baya na kawar da cin hanci da rashawa tare da farfaɗo da tattalin arziƙi ta hanyar noma, haƙowa da sarrafa ma’adinai da rage dogaro a kan man fetur.

Mujallar Mikiya ta yi wannan batu duba na tsanaki tare da duba abubuwan da zasu iya faruwa idan aka sauya fasalin Najeriya da kuma waɗanda zasu faru idan aka ci gaba da zama a yadda ake a yanzu.

Ta Yaya Al’amarin Ya Samo Asali?
A wata muƙala da Shahararren masani Farfesa Itse Sagay ya taɓa gabatarwa a shekraun baya, ya nuna cewar wannan batu ya samo asali tun kafin turawan Birtaniya su miƙa wa Najeriya ‘yancin mulkin kai. Farfesa Sagay ya rawaito Marigayi Firiyam Ministan Najeriya Sir, Abdubakar Tafawa Balewa a shekarar 1947 inda yake cewa : ‘Wanzuwar Najeriya a matsayin ƙasa ɗaya, a kan takarda ne kawai ; amma maganar gaskiya ba ta ma kama hanyar zama ƙasa ɗaya ba balle kuma a yi maganar haɗin kai a tsakanin ‘ya’yanta.’
Farfesa Sagay ya bayyana cewar juyin mulkin da ya yi sanadiyyar kashe su Sardauna a Janairun 1966 da kuma juyin mulkin mai da martani da ya yi sanadiyyar mutuwar su ironsi a Yulin 1966 su suka ƙara rura wutar rashin yarda, rashin amintaka da zaman ɗar-ɗar a tsakanin ƙabilu da yankunan Najeriya. Tun daga wannan lokaci zuwa yanzu, kullum ana ta kiraye-kiraye ko dai a wargatsa Najeriya kowa ya kama gabansa ko kuma a sake mata fasali kowa ya dinga cin gashin kansa.
Tsarin mulkin shiyyoyi da aka gudanar daga shekarar 1960 zuwa 1966 inda yankuna huɗu na Arewa, Gabas, Yamma da Yamma ta tsakiya suke da iko mai yawa yayi tasiri sosai wajen rage matsaloli, amma bai magance matsalar ba baki ɗaya domin kuwa duk da haka gwamnatin tsakiya tana da ƙarfi da tasirin da kowa ƙoƙari yake shi ke da iko da ita.
Kafin bayyanar man fetur a matsayin ƙashin bayan tattalin arziƙin Najeriya, kowanne yanki yana samar da wani abu dai-dai gwargwado wanda zai isa a riƙe ƙasa. Akwai ma’adinan Tin da Kwalambite daga yankin Jos, Gyaɗa da auduga daga can ƙuryar Arewa, Koko da kwakwar manja daga Kudu da sauransu. A wancan lokaci an fi maganar ƙarfin iko na siyasa fiye da maganar rabon arziƙin ƙasa.

Ya Fasalin Najeriya zai Kasance?
A yanzu haka Najeriya tana da jihohi 36 da ƙananan hukumomi 774. Kowacce jiha tana da damar cin gashin kanta a abubuwa da dama amma al’amuran tsaro, haƙowa da rabon arziƙin ƙasa, al’amuran ƙasar waje da na ƙasa da ƙasa da kuma karɓar harajin kan iyaka na Kwastam duk suna hannun Gwamnatin Tarayya. Kowacce jiha tana da ‘yan majalisu waɗanda suke da ikon yin dokokin da suka dace da ita amma da sharaɗin waɗannan dokoki basu ci karo dana Kundin Tsarin Mulki ba.
Kodayake har yanzu babu wata tartibiyar matsaya a kan takamaimai yaya ma ake so a fasalta ƙasar, amma ruɗani kullum sake gaba yake yi. Yayin da wasu suke bayar da shawarar a koma mulkin shiyya-shiyya kamar na lokacin su Sardauna, wasu suna ganin a ƙyale jihohi kawai kamar yadda suke amma a ƙara musu ƙarfin iko. Wasu kuwa suna ganin kawai a rushe jihohi a ƙyale ƙananan hukumomi kaɗai. A can gefe ɗaya kuwa wasu suna kira da kawai a rushe tsarin mulkin shugaban ƙasa da ɓangaren zartarwa, a koma na Firayim Minintsa da ‘yan majalisu kamar yadda Birtaniya, Canada da sauran wasu ƙasashe suke yi.

Taron Makomar ƙasa na Shekarar 2014
Wannan ruɗani na rashin sanin takamaiman ma ya ake so a fasalta ƙasar shi ya sanya tsohon shugaban ƙasa Goodluck Jonathan ya kira taron nema wa ƙasa makoma a shekarar 2014. Taron, wanda shugaban ƙasar ya bayyana aniyar samar da shi tun ranar ɗaya ga watan oktobar 2013, bai fara gudana ba kusan sai a tsakiyar shekarar 2014. Taron, wanda aka shafe sama da watanni uku ana yi, ya samu wakilai sama da 400 daga dukkan jihohin Najeriya, ƙungiyoyi, ƙabilu da addinai. Duk da lashe sama da naira biliyan bakwai da taron ya yi, mutane da dama suna ganin bai samar da nasarar da ya kamata ya samar ba.
Taron wanda a wasu lokutan da ake gudanar da shi, ya kan tashi baran-baran, ya fitar da rahoto mai kusan shafuka 900 a ƙarshensa. Taron ya bayar da shawarwari masu yawa a kan abubuwan da suka shafi noma, albarkatun ruwa, ‘yancin ‘yan ƙasa da baƙi, harkar shige da fice cikin ƙasa, ci gaban matasa, ƙungiyoi, rabon iko a tsakanin sassan gwamnati da sauransu. Amma dangane da sauya fasalin ƙasa kuwa, taron ya bada shawarar a rage wa Gwamnatin Tarayya kason da take samu daga arziƙin ƙasa daga 52.68% zuwa 42.5%, a ƙara wa jihohi kasonsu daga 26.72% zuwa 35% sannan a ƙara wa ƙananan hukumomi nasu daga 20.60% zuwa 22.5%. Dangane da ikon sarrafa arziƙin da kowanne yanki yake da shi, taron ya yi kira da a ƙara yin duba na tsanaki a kan 13% da ake bai wa jihohi masu arziƙin man fetur. Taron ya nemi a sake fasalta tsarin Gwamnatin Tarayya duba yiwuwar ƙirƙiro ƙarin jihohi.
Taron ya fara fuskantar tangarɗa ne tun farko a lokacin da wasu ‘yan Majalisun Tarayya da na Dattawa na wancan lokaci suka nuna adawarsu da shi tare da bayyana rashin hallaccinsa. A cewarsu, Kundin Tsarin Mulkin Najeriya, su kaɗai ya bai wa dama su sake wa ƙasa fasali ko dokoki, kuma a matsayinsu na masu wakiltar kowannne ɓangare na Najeriya, su yakmata su yi alƙalanci a kan batutuwan da suka shafi jama’ar ƙasa da makomarsu. Kodayake gwano bay a jin warin jikinsa, amma kusan sai a ce gazawar ‘yan majalisun a aikinsu daga 1999 zuwa yanzu ya taka muhimmiyar rawa wajen shiga wannan ruɗani da ake ciki.
Tun daga lokacin da kwamitin ƙoli na wannan taro ya miƙa wa Shugaba Jonathan rahotansa mai shafi 897 a shekarar 2014, har yanzu babu wanda ya sake jin ɗuriyar wannan rahoto.

Tsugunu bata ƙare ba?
Yana da ‘yar wahala a iya tantancewa kai tsaye ko gyaran fasalin ƙasa zai magance matsalolin Najeriya. Haka zalika ba za a iya riƙo da hasashe a mtsayin madogarar ko wane irin tasiri zai yi ba, mai kyau ko mara kyau. To amma sanin kowane cewar abin da yafi damun Najeriya shine rashin shugabanci nagari a dukkan matakai da aka daɗe ana fama da shi na tsawon shekara da shekaru. Wannan rashin shugabanci nagari shi ya ƙara dagula al’amuran jihohi wanda dama can sun zama cima-zaune. Abin ya zamo kamar gaba-kura-baya-sayaki; a ƙyale jihohi a yadda suke, su ci gaba da zama kaska-raɓi-mai-jini, a basu ‘yancin kansu, wasunsu su ruguje saboda rashin kuɗin shiga da lalataccen shugabanci.
Mai yiwuwa sai an samu kyakkyawan shugabanci tun daga kan ƙananan hukumomi har zuwa Gwamnatin Tarayya da majalisu da ma’aikatun gwamnati na tsawon wani lokaci kamar shekaru 5 zuwa 10 sannan ne zamu tabbatar da cewar ko matsalolin Najeriya masu gyaruwa ne ko ba masu gyaruwa bane, koko a’a dole sai an sauya fasalin ƙasa sannan ƙasar zata gyaru ko kuma ba sai an sauya ba.
Duk wannan na nufin cewar dai ko da an sauya fasalin ƙasa, akwai alamun cewar tsugunu bata ƙare ba. Matsalolin ƙabilanci, addini, ɓangaranci ba lallai su kau ba. Misali, a jihohi irinsu Adamawa, akwai ƙabilu kusan guda 30. Koda ka bai wa jihar ‘yancin cin gashin kanta, ba lallai ne a samar da wani gamsasshen tsari da zai kula da buƙatun dukkan ƙabilun ba. Saboda haka, akwai yiwuwar za a sake samun danniya da babakere daga manyan ƙabilu a kowacce jiha.
A Jihar Delta misali, yankin kudancin jihar ne suke da arziƙin mai kuma a nan mafi yawan arziƙin jihar yake, nan ne ƙabilun Urhobo da Itsekiri suka fi yawa. Arewacin jihar wanda da dama daga cikinsu Inyamuraine basu da wannan arziƙi na mai. Mikiya ta bibiyi wani zauren tattaunawa na yanar gizo inda wasu masu bada gudunmawa a cikinsa kuma ‘yan  jihar ta Delta suke cewa ba abun mamaki bane idan an bai wa jihar ‘yancin cin moriyar arziƙinta,‘yan kudancin jihar su mayar da ‘yan arewacin jihar saniyar ware. Ma’ana dai, yaƙin da a da ake yi da ‘yan waje, yanzu kuma zai komo na cikin gida.

Man Fetur da sauran arziƙin ƙasa
Binciken masana harkar albarkatun ƙasa, siyasar duniya da tattalin arziƙi sun nuna cewar da wahala a samu ƙasar da take da albarkatun man fetur ba tare da wannan mai ya zame mata sila ta rigima, ɓarna, rashawa, shantakewa da kuma watsi da sauran al’amura kamar noma da kiwo ba. Wani rahoto na ci gaban ƙasashen Afrika da aka wallafa a shekarar 2007 ya sanya Najeriya a jerin ƙasashen da man fetur ya zame wa alaƙaƙai a maimakon sinadirin ci gaba. Mafi yawan ƙasashen da basu da ko ɗigo ɗaya na fetur sun dame Najeriya sun shanye ta fuskar more rayuwa da ci gaba. Rahoton ya nuna cewar in banda tsirarun ƙasashen yankin Larabawa kamar su Kuwait da UAE, da wahala a samu ƙasashen da man fetur ya zamo wa alkhairi.
Bayan haka, wannan man fetur da Najeriya take ta taƙama da kuma rigima a kansa, kullum duniya ƙara rage buƙatarsa take yi saboda sababbin fasaha da ake fito dasu na yin amfani da makamashi mai arha kuma mara gurɓata muhalli. Manyan ƙasashen duniya suna taƙama ne da fasahar ƙere-ƙere, ilimi da bincike, kasuwanci da masana’antu. A duk jerin manyan ƙasashen duniya, babu wata wacce ta dogara da man fetur ko arziƙin da ake haƙowa a ƙasa.

Makomar Arewacin Najeriya
Wani babban abun mamaki shine yadda mutanen Arewacin Najeriya waɗanda a can shekarun baya suka fi kowa nuna shauƙi da buƙatar cin gashin kansu, yanzu kuma su suka fi nuna baya-baya da hakan. Duk mai lura da yadda al’amura suke kasancewa zai ga cewar mutanen Arewacin Najeriya kusan sun kasu kashi biyu dangane da wannan batu na sauya fasalin ƙasa. Kashi na farko sune waɗanda suke adawa da wannan batu; kashi na biyu shine waɗanda suka yi shiru amma suma da alama basa goyon bayansa. Waɗanda suke goyon bayan, da alama, basu da yawa.
Me ya kawo haka? Mutanen Arewa sun jima suna barci, basu shirya ba kuma suna tsoron abinda zai kasance bisa rashin tabbacin tattalin arziƙi da hanyar samun kuɗin shiga idan kuɗaɗen man fetur ɗin da ake haƙowa daga Niger-Delta ya daina shigo musu daga Gwamnatin Tarayya. Mai yiwuwa basu taɓa tsammanin za a wayi gari a irin wannan yanayi ba. Kididdigar da aka yi a shekarar 2015 ta nuna cewar abinda jihohon Arewa 19 gabaɗayansu suke iya samu na kuɗin shiga a ƙashin kansu a shekara guda bai kai abinda Jihar Lagos take iya samu ita kaɗai ba. Banda jihohoin Kano da Kaduna, babu wata jiha guda ɗaya kaf faɗin Arewa da take iya samun kuɗin shigar da ya kai naira biliyan 1.5 a kowanne wata.
A lissafin talauci, jihohin Arewa sune sahun gaba; a lissafin jahilci da rashin aikin yi, jihohhin Arewa sune sahun gaba; a lissafin dogaro da Gwamnatin Tarayya, jihohin Arewa ne kan gaba. An yi watsi da noma da kiwo, rashin kantarki ya kashe masana’antu, kasuwanci ya ja baya, ilimi ya taɓarɓare, an bar shugabanci a hannun marasa kishi; idan aka fasalta ƙasa kowa ya koma cin arziƙinsa, shin Arewa me ta tanada?

Mecece Mafita?
Mutane da dama sun yi mamakin yadda Gwamnatin Tarayya ta kasa fito da wani gamsasshen tsari dangane da ƙudurinta kan kiraye-kirayen sauya fasalin ƙasa duk kuwa da cewa batune da yake ci wa ‘yan Najeriya da dama tuwo a ƙwarya. Tun kafin haka ma, kowa ya san da irin rarrabuwar kawuna da ya biyo bayan zaɓukan 2015. Tun  ma kafin zaɓukan, an fuskanci rabe-raben kawuna da ƙin jinin juna tsakanin ‘yan Najeriya da kusan ba a taɓa ganin irinsa ba tun bayan yaƙin basasar da aka gama a shekarar 1970. An yi zaton cewa ajandar Shugaba Buhari ta farko bayan an rantsar da shi zata zamo yin ƙoƙari a aikace na ɗinke ɓaraka tare da ƙoƙarin haɗa kan ‘yan ƙasa baki ɗaya. Sama da shekara guda da rantsar da shi, har yanzu babu wani abu da ya fito na fili ƙarara cewar akwai alamun yin hakan. Wataƙila wannance ma ta buɗe ƙofa ga ‘yan tawayen Niger-Delta suka dawo da tsagerancin da aka kwana biyu ba a ga irinsa ba da kuma fafutukar ‘yan tawaren Biafra.
Babban abinda zai taimaka wajen magance matsalolin da suke addabar Najeriya shine kawar da cin hanci da rashawa, bunƙasa noma da kiwo, wadatar ilimi da aiyukan yi, bunƙasa tattalin arziƙin ƙasa, tabbatar da tsaro da zaman lafiya, samar da abubuwan more rayuwa da kuma wanzar da kyakkyawan shugabanci a dukkan matakai tun daga sama har ƙasa. Malam Ibrahim Hussaini marubuci kuma masanin tarihi ya shaida wa Mikiya cewar sauya fasalin ƙasa ba shine mafita ba; abinda yake mafita shine a yi komai a kan ƙa’ida. Yace idan ka duba dokoki da daftarin tsare-tsaren ci gaba na Najeriya, sai kaga cewar da za a bisu sau da ƙafa, to da ba a sha wahala ba. Don haka, maimakon a shigo da wani sabon tsarin, a yi ƙoƙari a dinga aikata kyawawan manufofin da aka tsara.
Dakta Garba Kofar-Naisa, masanin albarkatun ƙasa kuma Malami a Jami’ar Gwamnatin Tarayya da take Dutsinma a Jihar Katsina yana ganin cewa ba wai man fetur ne kaɗai arziƙi ba kamar yadda mafi yawan ‘yan Najeriya suka fahimta. Yace shi arziƙin da Allah ya shimfiɗa  a ƙasa ba zai misaltu ba, hatta ƙasar noma mai kyau itama arziƙi ce, sai dai ragwanta irin ta ɗan Adam tasa ya kasa yin hoɓɓasa don cin moriyarasu. Don haka yana ganin koda an daina raba kuɗin ma fetur, duk Jihar da taga dama, to zata iya riƙe kanta ba tare da ta bari ana yi mata yanga ko hantara ba matuƙar bata saka lalaci ba.
Duk da cewa abu ne mai wahala sosai Gwamnatin Tarayya ta ƙyale kowacce jiha ta samu ‘yancin sarrafa arziƙinta a yanzu domin kasancewar hakan barazana gareta, to amma akwai buƙatar a sake wa al’amarin duba na tsanaki. Akwai buƙatar Gwamnatin Tarayya ta kafa wani kwamiti na ƙwararru da gaggawa wanda zai bata shawara kan inda ya kamata a dosa.
  
©Mujallar Mikiya, 2016

Monday, May 9, 2016

Kafafen Tumasanci da Yaɗa Bambaɗanci

09 Ga Mayu, 2016



B
abu kafar yaɗa labarai da mafi yawan talakawan Najeriya suka dogara da ita domin samun bayanai kamar rediyo wataƙila saboda araha wajen mallaka da kuma sauƙin sarrafawa. A gefe guda kuma babu kafar da ake jibgawa kowacce irin shara a Najeriya, musamman ma Arewa, kamar ita rediyon. Akwai tarin matasloli da suke damun sauran kafafen yaɗa labarai irin su talabijin, jaridu da kuma yanar gizo; amma kusan babu kafar da ta kai rediyon fuskantar matasaloli iri daban-daban.

A cikin manya da ƙananan gidajen rediyo kusan guda 150 ko sama da haka da muke dasu a ƙasarnan, sama da 50% mallakar gwamnatocin jihohi  ne da na Gwamnatin Tarayya. Misali, aƙalla kowacce jiha tana da gidan rediyo mallakarta guda ɗaya a zangon AM, wasu jihohin da dama suna da ƙarin tasha ɗaya ko sama da haka a zangon FM. Bayan haka, Gwamnatin Tarayya tana da gidajen rediyo ɗai-ɗai a kan zangon FM a kowacce jiha waɗanda ta buɗe a shekarar 2003 domin faɗaɗa shirye-shiryen da babban gidan rediyo na ƙasa yake gabatarwa daga Abuja zuwa dukkan sassan ƙasarnan. Duk wannan lissafi bai haɗa da gidajen rediyoyi da dama a Najeriya waɗanda suke yaɗa shirye-shiryensu a kan yanar gizo kaɗai ba.

Mallakar kafafen yaɗa labarai a ɓangaren gwamnati ko wasu sassanta ba wani sabon abu bane a duniya kuma ba wani abin damuwa bane. Hasalima wasu manya-manyan kafafen yaɗa labarai da ake taƙama dasu a duniya wajen shahara da ƙwarewa irinsu BBC, Muryar Amurka, da DW duk mallakar gwamnati ne. Abinda yake matsala shi ne idan masu riƙe da madafun iko suna yin amfani da waɗannan kafafen yaɗa labarai domin amfanin kansu da ‘yan korensu. Ba wai an ce kada waɗannan kafafen yaɗa labarai su tallata manufofi da aiyukan gwamnati ba, amma ya kamata su yi abin cikin hikima da ƙwarewa kuma su bayar da cikakkiyar dama ga masu yin adawa da manufofin gwamnatin domin su mayar da martani.

Kafafen yaɗa labarai, musamman gidajen rediyo mallakar gwamnatocin jihohi sun zama kafafen yi wa gwamnoni tumasanci da bambaɗanci. Mafi yawan shirye-shiryensu sun karkata wajen yabon gwamnatin da take mulki komai kuwa irin ta’asar da take aikatawa. Wani lokaci, waɗannan gidajen rediyo su kan gabatar da shirye-shirye masu muhimmanci da zasu ilmantar da kuma faɗakar da al’umma, to amma saboda wannan ɗabi’a tasu mai ban haushi, da yawa an haƙura da shirye-shiryen nasu baki ɗaya. Haka za a ci gaba da tafiya; ana ɗiban kuɗin al’umma wajen gudanar da irin waɗannan kafafen yaɗa labarai, a gefe ɗaya kuma shugaban ƙasa, gwamnoni da muƙarraban jam’iyya mai mulki suna amfani da waɗannan kafafe tamkar mallakarsu na ƙashin kansu?

Wani lokaci ina tattaunawa da wani ma’aikacin gidan rediyo mallakar gwamnati a wata jiha a Arewa maso yammacin Najeriya; sai yake bani labarin wani gwamna da aka taɓa yi wanda a lokacinsa ba a isa a sanar da ko da ɗaurin auren wani ɗan jam’iyyar adawa ko mai alaƙa da shi ta wannan kafa ba. A wasu lokutan da kansa gwamnan yake bugo wa manajan gidan rediyon waya yace a katse kowanne irin shiri da ake yi, a saka masa wata waƙarsa ta siyasa wadda yake so. Wannan kaɗan ne daga cikin irin yadda wasu gwamnonin suke yi wa irin waɗannan kafafen yaɗa labarai mulkin mallaka. A wasu lokutan kuma ba laifin gwamnan bane da kansa, muƙarrabansa ne da ‘yan jam’iyyarsa suke yin uwa da makarɓiya a gidajen rediyon, shi kuma gwamnan sai ya kasa hanasu saboda dalilai na siyasa. Wani lokaci kuma manajan gidan rediyon da gwamna ya naɗa ne yake mayar da gidan rediyon fagen bambaɗanci da tumasanci ga gwamna domin ya gyara miyarsa; shi kuma ƙila gwamnan dama haka yake so.

Kafafen yaɗa labarai mallakar gwamnati su ya kamata a ce sun zamo abin misali ta hanyar fin  kowa nagarta domin su ba kuɗi suke nema ba kamar na ‘yan kasuwa kuma an kafasu ne domin su bauta wa jama’a ba gwamna ko shugaban ƙasa ba. An ƙaddara cewa su mallakar jama’a ne kuma wasu kafafe ne na sadarwa, faɗakarwa, wayarwa da kuma tallata manufofin kishin ƙasa da ci gaba. To amma maimakon haka, sun zama kafafen farfaganda da ɗaukar bangare tare da goyon bayan son zuciya. Wannan ita tasa mafi yawancin jama’a suka ƙaurace musu domin sauraron na ‘yan kasuwa masu zaman kansu duk kuwa da cewar ba finsu ƙwararrun ma’aikata ko iya gabatar da shirye-shirye aka yi ba.

Kafafen yaɗa labarai na talabijin, suma haka gwamnatoci suka lalata al’amarinsu tare da sauke su daga bin ƙa’idojin aikin jarida inda ba abinda ake yi sai tallan masu mulki da kuma hana ‘yan adawa damar faɗar albarkacin baki. To amma, daɗinta ita talabijin ba ma kowa ne yake da ita ba kuma ba dukkan masu itan bane ma suke da isasshiyar wutar lantarkin da zasu dinga kallonta akai-akai ba. Su kuwa jaridu mallakar gwamnatoci, mafi yawancinsu sun durƙushe, gwamnatocin sun kasa riƙe su. Ita kuwa yanar gizo ta kowa ce, babu wani mai mulki da zai iya hana faɗar albarkacin baki a cikinta ko kuma yace sai abinda yake so shi mutane zasu karanta. Matsalar kawai ita ce, yanar gizo tana da matuƙar matsala domin ana yawan yaɗa ƙarya da labaran ƙanzon kurege ta wannan  kafa kuma ana yawan amfani da ita wajen ci wa  jama’a da masu mulki mutunci da yi musu ƙage a inda basu ji ba basu gani ba.

Kasancewar halin da kafafen yaɗa labarai mallakar gwamnati suka samu kansu, mutane da yawa sai suka ƙaurace musu, suka koma na ‘yan kasuwa. Idan bamu manta ba, har a shekarar 1999 babu gidan rediyo mallakar ‘yan kasuwa ko ɗaya da yake aiki ka’in da na’in a Arewacin Najeriya, sannan waɗanda suke a kudanci basu fi a ƙirge su ba. Yanzu irin waɗannan gidajen rediyo sun mamaye ko’ina amma har a yanzu haka akwai tsirarun jihohin da basu da gidan rediyo masu zaman kansu ko ɗaya, sai dai na gwamnati. Irin waɗannan jihohi suna fuskantar cikas sosai wajen faɗin albarkacin bakinsu. Matsalar a nan ita ce, su ‘yan kasuwa kuɗi suke nema domin sun zuba maƙudan kuɗaɗe wajen samun lasisi da kuma kafa injina. Bayan haka suna kashe maƙudan kuɗaɗe wajen samar wa da kansu wutar lantarki, biyan haraji da albashin ma’aikatansu. Wannan ce ta sa, mafi yawancinsu kuɗi sune abinda suka fi nema ido rufe. Sakamakon haka, sai ‘yan siyasa da sauran jama’a suka yi amfani da wannan dama wajen mayar da su gurin zubar da kowacce  irin shara suka ɗebo. A wasu lokutan, matuƙar kana da ‘yan kuɗinka a aljihu, sai kaje ka biya a barka kai ta faɗar irin sakarcin da kake so da sunan siyasa; mutane su yi ta faɗin ƙazantar bakinsu amma wai su kira shi da faɗin albarkacin baki. Waɗanda basu da ilimi ko ƙwarewar da ya kamata su yi magana a sauraresu, sai su shiga gidan rediyo mai zaman kansa su yi ta soki burutsu wai su ga masu ‘yanci, banza ta faɗi.

Lokacin da ministan yaɗa labarai da ci gaban al’adu na gwamnatin Shugaba Buhari, Alhaji Lai Mohammed ya kama aiki kimanin watanni shida da suka wuce, ya yi alƙawarin cewar Gwamnatin Tarayya zata yi wa kafafen yaɗa labaranta garanbawul domin su amfani dukkan ‘yan kasa ba wai waɗanda suke mulki ko ‘yan jam’iyya mai mulki kaɗai ba. Daga wancan lokaci zuwa yanzu, alamu sun nuna an ɗan soma samun canji kaɗan ba da yawa ba musamman a kafafe irinsu NTA, FRCN, NAN da dai sauransu. Ya kamata jihohi su bi sahu wajen kawo gyara ga kafafen yaɗa labarai. Yana da kyau masu mulki su fahimci cewar aikin da suka yi ko suka ƙi yi wa talakawa shi zai yi musu alƙalanci ba wai mallake kafafen yaɗa labarai ba. Kan mutane yanzu a waye yake; idan sun yi abu mai kyau ko mara kyau, za a samu kafar da za a faɗa, koda sun hana a faɗa a kafar gwamnati.

Yana da kyau, ƙungiyar ‘yan jaridu ta ƙasa, NUJ ta dinga yi wa ma’aikatanta masu aiki a irin waɗannan kafafen yaɗa labari na gwamnati bita ta musamman tare da fahimtar dasu cewar aikin jama’a suke yi ba na mai mulki ba kuma ‘yan siyasa basu da ikon tilasta musu  kauce wa dokokin aikin jarida don kawai suna masu mulki. Su nuna musu cewar, idan suka haɗa kansu, za su iya bin duka matakan da suka dace domin tsaftace aikinsu da ƙin yarda a lalata musu shi. NUJ ta fahimtar dasu irin zubewa da ƙimarsu da mutuncin aikinsu yake yi wajen  yi wa masu mulki bambaɗanci da tumasanci a rediyo da sunan yaɗa labarai ko aikin jarida.

Majalisun dokoki na jihohi da na tarayya, ya kamata su kalli wannan matsala  tare da duba yiwuwar yin dokokin da zasu hana gwamna ko shugaban ƙasa ikon naɗa ko tuɓe shugabannin gidajen yaɗa labarai mallakar gwamnati domin samar musu da ‘yancin kansu.

Sunday, April 17, 2016

Shekara ɗaya a Gwamnatin APC: Ko Kwalliya ta Fara Biyan Kuɗin Sabulu?

10 Ga Afrilu, 2016


Daga: Amir Abdulazeez

R
anar 28 ga watan Maris aka gudanar da zaɓen shugaban ƙasar da ya kafa tarihi a Najeriya. Zaɓen da ya yi sanadiyyar kawar da jam’iyya mai mulki ya kawo jam’iyyar adawa kan mulki a karo na farko a  tarihin dimokraɗiyyar Najeriya. Haƙiƙa irin wannan ba ta cika faruwa ba a Nahiyar Afrika tun daga lokacin da turawan mulkin mallaka suka bai wa ƙasashen nahiyar ‘yancin kai har zuwa yau. Hasalima, kullum al’amuran zaɓuka ƙara lalacewa suke yi saboda ƙudurin da mafi yawan shugabannin Afrika suke da shi na dauwama a kan mulki.

Jam’iyyar APC ta ɗare kan mulki bayan tsawon shekaru 12 da jam’iyyun adawa suka shafe suna fafutukar ganin sun kawar da PDP daga mulki ba tare da sun samu wata ƙwaƙƙwarar nasara ba. Bayan kujerar shugaban ƙasa, ta kuma samu nasarar kafa rinjaye a Majalisar Wakilai ta Tarayya da kuma Dattijai ta Sanatoci. Bugu da ƙari, ta samu damar kafa gwmanati a jihohi 23 cikin 36 da ake dasu a ƙasar nan. Saboda haka tun daga sama har ƙasa, sama da 65% na madafun ikon gwamnatocin ƙasarnan a hannun jam’iyyar yake kai tsaye.

Daga kafa gwamnatin APC zuwa yanzu, aƙalla an samu shekara ɗaya; wannan na nufin cewar jam’iyyar ta cinye kashi ɗaya bisa huɗu na wa’adin da ‘yan Najeriya suka zaɓe ta tayi. Sakamakon haka, akwai buƙatar a kalli irin jagorancin da gwamnatin ta APC ta gabatar a tsawon wannan lokaci domin ganin ko kwalliya ta fara biyan kuɗin sabulu. Kafin a yi hakan, akwai buƙatar a yi waiwaye adon tafiya don ganin irin rawar da PDP ta taka a tsawon shekaru 16.

Tsakanin Gyara da Kuma Ɓarnar PDP
A jimlace zamu iya cewar, PDP ta gaza, nesa ba kusa ba wajen ciyar da Najeriya gaba a tsawon shekaru 16 da ta yi tana mulki domin kuwa mafi yawan matsalolin da muke ciki a 1999 a lokacin da jam’iyyar ta fara mulki, sune dai suke damunmu har a shekarar 2015 da ta bar mulki. To amma kuma, duk da tarin ɓarna da lalata ƙasa da mafi yawancin ‘yan Najeriya suke kallon jam’iyyar PDP ta yi, akwai wasu abubuwa na kirki da ta taɓuka. Babu shakka dole mu yarda cewar PDP ta taka rawar gani sosai wajen lalata al’amuran zaɓe da nagartacciyar dimokraɗiyya a ƙasarnan tare da ɗaukaka matsayin cin hanci da rashawa da yi wa doka karan tsaye a Najeriya. To amma ta wani ɓangare, PDP ɗin, musamman  a ƙarƙashin jagorancin Obasanjo da ‘Yaradua, ta taimaka wajen farfaɗo da tattalin arziƙin ƙasa. Misali, lokacin da Obasanjo ya karɓi mulki a hannun sojoji, asusun ajiyar Najeriya na ƙasar waje, abin da yake cikinsa bai wuce  dala biliyan huɗu ba kacal, amma lokacin da ya bar mulki zuwa lokacin  da ‘Yaradua ya rasu, akwai sama da dala miliyan 60 a cikin wancan asusu.
Kodayake ana kallon Jonathan a matasayin wanda yafi kowa ɗaurewa cin hanci da rashawa gindi, amma alokacinsa ne zaɓuka suka fara gyaruwa, abinda har ya kai ga samar da ingantaccen zaɓen da ya kawar da shi daga mulki.
Duk da irin wadaƙa da kuɗin gwamnati da ake kallon PDP ta yi, akwai abubuwa da ta tafi ta bari wanda APC zata iya ɗorawa a kai.

Halin da APC ta Samu da Najeriya
Jam’iyyar APC ta karɓi Najeriya a lokacin da ƙasar take cikin wani mawuyacin hali. Farko dai akwai rarrabuwar kai da ƙin jinin juna bisa dalilai na addini da ƙabilanci da ya kai matakin ta’azzarar da bai taɓa kaiwa ba tun bayan gama yaƙin basasa na Biafra a shekarar 1970. Bayan haka, akwai faɗuwar farashin man fetur wanwar wanda wani lokaci tsakanin shekarar 2009 zuwa 2013, farashin gangarsa guda ɗaya ta kai dalar Amurka 100 zuwa 140. A kwanakin baya, ganga ɗaya sai da ta kai dala 30, a yanzu ana sayar da ita tsakanin dala 39 zuwa 41. Wannan na nufin cewar kuɗin shigar Najeriya ya ragu da kaso kusan biyu bisa uku. Jam’iyyar APC ta samu Najeriya a cikin badaƙƙaloli daban-daban na almundahana da kuɗin ƙasa, ta samu an yi wa asusun ƙasa wakaci ka tashi tun daga kan matakin tarayya har zuwa jihohi.
Jam’iyyar APC ta gaji babbar matasala wacce ita ce ta harkar tsaro. Daga cikin wannan matsala akwai Boko Haram, fashi da makami, satar shanu, garkuwa da mutane, tada zaune tsaye a yankin Niger-Delta, satar ɗanyen mai, bangar siyasa, faɗan Fulani makiyaya da manoma, rikice-rikicen addini da na ƙabilanci a sassa daban-daban da dai sauransu.
Jam’iyyar ta gaji sauran matsaloli waɗanda suka haɗa da rashin ɗorarren samuwar man fetur, dogaron tattalin arziƙin ƙasa a kan man fetur, durƙushewar noma, rashin wadatacciyar wutar lantarki, rashin ingancin noma da masana’antu da dai sauransu.

A ina APC ta Samu Nasara Cikin Shekara Guda?
Duk da yake ba zai yiwu a ce an ga ƙwaƙƙwaran sauyi a cikin shekara guda ba, amma an ce wai Juma’ar da zata yi kyau, daga Laraba ake gane ta. Abu na farko muhimmi da gwamnatin APC ta fara yi shi ne wajen taimaka wa jihohi 27 da maƙudan kuɗaɗe a matsayin rance domin su samu su biya tarin albashin da ma’aikatansu suke binsu na wata da watanni. Wannan ta taimaka wajen ceto mafi yawan jihohin da ƙananan hukumominsu daga faɗawa mawuyacin hali.
Gwamnatin Tarayya ta APC ta taka rawar gani ta fuskar yaƙi da Boko Haram, duk da dai cewar har yanzu akwai matasalar a Arewa maso gabashin ƙasarnan amma nasarar da aka samu a bayyane take. Sai dai kuma a sauran matsalolin tsaro irinsu satar shanu, rikicin Fulani da manoma, garkuwa da mutane, har yanzu gwamnatin tana da sauran aiki a gabanta.
Jam’iyyar APC ta duƙufa gadan-gadan wajen yaƙi da cin hanci da rashawa musamman wajen tuhumar jami’an gwamnatin da suka gabata. Misali shine yadda gwamnatin ta bankaɗo badaƙƙalar sayen makamai a ofishin Sambo Dasuki da kuma yadda EFCC ta samu wani sabon ƙarfi wajen tuhuma da gurfanar da waɗanda ake tuhuma da satar dukiyar gwamnati a gaban kotu. Sai dai kuma wani hanzari ba gudu ba shine, gwamnatin har yanzu ba ta samu nasarar tabbatar da ko da mutum ɗaya a matasyin mai laifi ba a gaban kotu a tsawon sheka guda. Idan aka tafi a haka, mutum nawa zata samu damar kammala shari’unsu a cikin shekaru huɗu? Bayan haka, ana zargin gwamnatin da ƙyale wasu shafaffu da mai ‘yan jam’iyyar APC tare da maida hankali a kan ‘yan adawa kawai. Sannan kuma ana ganin gwamnatin a wasu lokuta ba ta yin biyayya ga umarnin kotu a wannan yaƙi da take yi.
Duk zaɓukan cike gurbi da aka gudanar a ƙarƙashin Hukumar Zaɓe ta mulkin APC, an kwatanta adalci. Ko jama’iyyar adawa ta PDP zata shaidi hakan. Wannan nasara ce babba.
Wata nasara kuma ita ce, yadda gwanatin take ƙoƙarin tsaftace al’amaura a dukkan matakai na gudanarwa. Banda haka, ƙimar Najeriya ta farfaɗo ƙwarai da gaske a idon duniya a ƙarƙashin jam’iyyar APC, duk da cewa wasu suna sukar Shugaba Buhari a kan yawan tafiye-tafiye da yake yi zuwa ƙasashen ƙetare.

A Ina Matsalolin APC Suke a Shekara Guda?
Gwamnatin jam’iyyar APC ta ɗauki sama da watanni shidan farkon mulkinta tana jan ƙafa da sanɗa; ta shafe tsawon wannan lokaci ba tare da ministoci da sauran jami’an gwamnati ba. Wannan ta taimaka ƙwarai wajen kawo wa gwamnatin cikas a kan tafiyar da aiyukanta. Har kawo yanzu akwai naɗe-naɗen masu muhimmanci da gwamnatin take ta jan ƙafa wajen yinsu.
Bayan haka, gwamnatin tarayya ta APC har yanzu bata yi wani yunƙuri ba a hukumance na ganin ta haɗa kan ‘yan Najeriya duba da yadda kawuna suka rarrabu a kan siyasa, addini, ƙabilanci da ɓangaranci dab da zaɓen shekarar 2015. Wannan rarrabuwar kai har yanzu tananan tana ƙara cigaba, kuma ɗaya daga cikin sakamakonta kuwa shine sabon yunƙurin kafa ƙasar Biafra da aka taso da shi ‘yan satattaki kaɗan bayan kafa sabuwar gwamnatin. Bugu da ƙari, ‘yan Kudu suna yi wa gwamnatin kallon kamar tana fifita ‘yan Arewa.
Babbar matasalar gwamnatin jam’iyyar APC ita ce yadda ta kasa shawo kan matsalar man fetur a Najeriya wacce ake ta fama da ita. Banda haka, ta kasa tsayawa a kan wata tartibiyar manufa dangane da sashen man fetur. Yau ta faɗi wani abu, gobe kuma sai ta canza, jibi kuma sai ta aikata wani abin daban.
Dangane da tattalin arziƙi, gwamnatin ta kasa shawo kan tashin farashin Dalar Amurka da sauran kuɗaɗen ƙara waje da muke tsananin buƙata domin sayo kayayyaki daga waje. A gefe ɗaya kuma, tsadar kayayyaki sai ƙara ta’azzara take yi.    
Kasafin kuɗin 2016 wanda shine na farko da jam’iyyar APC ta yi a mulkinta yazo da kura-kurai da aringizo da yawa-wani abu da ba a yi tsammaninsa a gurin gwamnati mai taƙama da gaskiya da riƙon amana ba.


Me ya kamata APC ta Yi?
Har yanzu jam’iyyar APC tana da sauran shekaru uku a cikin huɗun da aka zaɓeta ta yi; akwai buƙatar ta yi waiwayen watannin da ta shafe  a kan mulki kuma ta yi wa kanta alƙalanci da kanta. Inda ta yi kurakurai, to ta yi ƙoƙari da gaggawar gyarawa, inda ta samu nasara sai ta yi ƙoƙarin ɗorawa a kai.
Maganganu da ƙulle-ƙullen siyasar 2019 da suka dabaibaye jam’iyyar tun kafin a je ko’ina, kamata ya yi a ajiye su waje ɗaya, ‘yan jam’iyyar su haɗa kai don ganin sun sauke nauyin da jama’ar Najeriya suka ɗora musu tukunna.
Yana da kyau jam’iyyar ta bar ƙofarta a buɗe wajen karɓar shawarwari komai ɗacinsu kuma koda daga wurin maƙiyansu ne. Bayan haka kuma ya kamata su sani cewar lokaci ba abokinsu bane a yanzu, dole sai sun zage damtse.


©Mujallar Mikiya 2016

Tuesday, April 5, 2016

Ko Tinubu Zai Tsaya Takarar Shugaban ƙasa?

04 Ga Afrilu, 2016


Daga: Amir Abdulazeez

A
gurin mafi yawan manazarta harkokin siyasar Najeriya, ba wai abin da Tinubu yake buƙata shine abin tambaya ba; wataƙila tambayar ita ce, ko Tinubu zai samu abin da yake buƙata? Kasancewar gwamnatin Shugaba Buhari ta kammala kusan dukkan wasu muhimman naɗe-naɗen muƙamai ba tare da an ji sunansa a ko ɗaya daga ciki ba, alama ce da take nuna cewar akwai wani abu daban kuma babba da Asiwajun yake hari.

Yunƙurin Bola Tinubu a kusan tsawon shekaru goma da suka gabata na ganin ya zama Mataimakin Shugaban ƙasar Najeriya, wani abu ne da kusan duk wani mai sanya idanu kan harkokin siyasa yake sane da shi. Wannan yunƙuri nasa, duk da ya jawo masa abubuwa daban-daban na cigaba da kuma cikas, amma ya yi sandiyyar zamansa wani ƙusa kuma jigo a matakin ƙasa. Labari ya yi ta kewayawa cewar, ƙoƙarin da Tinubu ya yi na zama ɗan takarar mataimaki ga tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar a ƙarƙashin tsohuwar jam’iyyar Action Congress (AC)  a zaɓen Shugaban ƙasa na shekarar 2007 shi ya kawo rashin jituwa tsakaninsu wanda har ta kai ga Atikun ya bar jam’iyyar AC ɗin ya koma PDP a shekarar 2008-matakin da har yanzu yake bibiyarsa har kawo yau kuma wasu suke ganin ya taka wata ‘yar rawa wajen rashin nasarar Atikun wajen samun tutar takarar APC a shekarar 2015. An rawaito cewar shi Atiku yana ganin ba a yi adalci ba idan aka bai wa Bayerabe ko ɗan kudu maso yamma takarar mataimakin shugaban ƙasa a dai-dai lokacin da Shugaba Obasanjo wanda yake Bayerabe ne shima yake kammala shekaru 8 a kan mulki. Don haka Atiku sai ya bada mamaki wajen ɗaukar Sanata Ben Obi wanda ba a sani ba sosai daga kudu maso gabashin Najeriya a maimakon Tinubu wanda shi ya yi uwa yai makarɓiya wajen ganin shi Turakin Adamawa ɗin ya samu tikitin AC cikin sauƙi, bayan PDP ta yi masa wulaƙanci.

Rahotanni sun nuna cewar rashin amincewar Buhari na ya ajiye Fasto Tunde Bakare ya ɗauki Tinubu, ita ta kawo rugujewar ƙoƙarin haɗewa ko dunƙulewa tsakanin tsofaffin jam’iyyun CPC, ANPP da ACN a shekarar 2011 domin tunkarar Jonathan da PDP. Daga baya Buhari ya yi masa biyan bashi a 2015 inda ya yi wa Tinubu tayin bashi abinda bai samu damar bashi ba a 2011. To amma Jagaban Borgun yana sane da matsala da tarnaƙin da tsayar da Musulmai zalla za ta iya kawo wa damar da jam’iyyar APC take da shi na cin zaɓen shugaban ƙasa. Tinubu ya bai wa mutane mamaki wajen danne kwaɗayinsa tare da miƙa sunan tsohon kwamishinansa Farfesa Yemi Osinbajo a matsayin ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa. Mutane da yawa suna kallon Osinbajo a matsayin wanda kawai yake riƙe da waccan kujera a madadin jagoran APC ɗin na ƙasa.

Me yasa Tinubu ya dinga fafutukar zama mataimakin shugaban kasa, ba ji ba gani? A tarihin dimokraɗiyyar Najeriya, da wahala a samu wani wanda ya ƙaunaci zama mataimakin shugaban ƙasa kamar sa. Amsar ba wata mai wahala bace; magana ce ta dabarar siyasa, me yiwuwa yana son zama shugaban ƙasa kuma yana so ya bi ta hanya mafi sauƙi, wacce ita ce ya fara zama mataimakin shugabn ƙasa. Tinubu ya samu damar da zai tsayar da kansa ɗan takarar shugaban ƙasar jam’iyyar ACN a shekarar 2011, amma bai yi hakan ba, me yiwuwa saboda ya san ɓata lokaci ne kawai kuma ƙila ba kamar sauran ‘yan siyasa ba, shi ba burinsa kawai  ace ya taɓa takarar shugaban ƙasa ba. Bayan haka kuma bai yi wani yunƙuri na zama mataimakin Nuhu Ribaɗu ba, wanda jam’iyyar ACN ɗin ta bai wa takarar shugaban ƙasa a wancan lokaci. Kodayake hakan bai ba wa mutane mamaki ba.
Dukkan jama’a, ciki har da Tinubu shi kansa sun san cewar zai yi matuƙar wahala ga wani mutum ɗan kudu maso yamma ya zama shugaban ƙasa kai tsaye a nan kusa, duba da cewar Obasanjo ya riga ya yi mulki na tsawon shekaru 8 a cikin 16 ɗin da aka yi da dawowar dimokraɗiyya a madadin wannan yankin. Da alama dai Asiwaju ya sadaukar da burinsa na zama mataimakain shugaban ƙasa a shekarar 2015 domin tabbatar da nasarar jam’iyyar APC, sai dai kuma ba za a fitar da ran cewar kuma a ƙarshe zai tsaya takarar shugaban ƙasar kai tsaye ba a shekarar 2019. Idan Buhari ya yanke shawarar ba zai nemi zango na biyu ba, to tamkar ya share wa Tinubu hanyar zama ɗan takarar jam’iyyar APC ne a 2019.

Idan Tinubu ya samu nasarar zama shugaban ƙasa, hakan zai zamo wani sakamako ko lada na tsawon lokaci da aka ɗauka ana tsare-tsare, haƙuri, surƙullen siyasa, zuba jari da kuma sadaukarwa. Tushen kafuwar sansanin siyasa da ƙarfin faɗa-a-jin tsohon gwamnan Jihar Lagos ɗin wanda yake ƙara faɗaɗa a kullum, ya samo asali ne daga kasancewarsa gwamna ɗaya tilo wanda ba na PDP ba a yankin Kudu maso yamma da kuma ɗaya cikin biyu a yankin Kudancin Najeriya baki ɗaya bayan zaɓukan shekarar 2003 da kuma jajircewarsa da fafutuka wajen ganin an fatattaki PDP daga yankinsa na Yarabawa tare da tabbatar da siyasar adawa a ƙasa baki ɗaya.

Wasu na kallon rashin karɓar wani muƙami a gwamnatin Buhari kawo yanzu daga ɓangaren Tinubu, kamar wani abu ne da zai iya haifar masa da matasala; wasu kuwa suna ganin hakan ma ƙarfi zai ƙara masa. Masu kallon hakan a matsala suna ganin cewar waɗansu mutane da suke cikin gwamnatin Buhari zasu yi amfani da muƙamansu wajen yin aikace-aikacen da zasu birge Buharin ta yadda zai yi tunaninsu a matsayin waɗanda zasu gaje shi domin ɗorawa a kan manufofin gwamnatinsa, hakan kuwa zai kawar da Tinubu daga lissafi. A ɗaya ɓangaren, wasu na ganin cewar rashin karɓar wani muƙami zai sa Tinubu ya mayar da hankali kan siyasarsa kuma zai raba kansa da duk wata badaƙƙala mai alaƙa da aikin gwamnati. Sannan kuma jam’iyyar APC  zata cigaba da jin cewar har yanzu yana binta bashin da baza ta iya biyansa ba. Bayan haka matasayinsa na kafi-sarki zai ci gaba da ɗorewa.

Ko shakka babu, ƙudurin Tinubu na zama shugaban ƙasa, akwai yiwuwar ya gamu da ƙalubale daban-daban. Akwai muhimman mutane da mai yiwuwa su nemi yin takara da shi tun ma daga yankinsa na kudu maso yamma. Muhimman Yarabawa irinsu Babatunde Fashola, Kayode Fayemi ko ma Yemi Osinbajo, duk zasu iya nuna sha’awarsu ga kujerar shugaban ƙasa. Muhimman ‘yan jam’iyyar APC daga yankin kudu maso gabas na Inyamurai kamarsu Chris Ngige, Ogbonnaya Onu da Rochas Okorocha suma zasu iya cewar to idan har mulki zai dawo kudu ne, to kamata yayi a ce kudu maso gabas zai dawo ba kudu maso yamma ba. Duk da irin shahararren gangancin siyasa da ragon azancin da kudu maso gabas suka yi a zaben shekarar 2015, zasu iya kallon Tinubu a matsayin wanda ya hana a basu kujerar mataimakin Shugaban ƙasa kuma zasu tashi tsaye a kansa wajen ganin bai ƙara hanasu wata damar ta samun kujerar mataimakin shugaban ƙasar ba, da ma ƙila ta shugaban ƙasar baki ɗungurugum a shekarar 2019. Wata mishkila da Tinubu zai iya fuskanta ita ce yankin Arewa wanda zai iya cewa idan har Buhari ba zai yi zango na biyu ba, to dole a ƙyale wani daga yankin aƙalla ya ƙarashe mulkin na tsawon shekaru huɗu. Mutane irinsu Atiku Abubakar, Bukola Saraki, Rabi’u Kwankwaso, Nasir El-Rufa’i da kuma wasu gwamnonin APC ɗin da suka gama zangonsu na biyu duk zasu yi yunƙurin gwada damarsu idan hakan ta faru.

Kasancewar mafi yawan jam’iyyar APC a aljihun Tinubu take, zai zamo riba a gareshi sosai, to amma kuma zai iya zamo masa matsala. Ya tara maƙiya da yawa a ƙoƙarinsa na baza ƙarfin ikonsa zuwa ko’ina a cikin jam’iyyar. Babu wani mutum da ya cicciɓa kuma ya sassaka yawan mutane a cikin shugabancin jam’iyya da gwamnati kamarsa, kuma bisa ga dukkan alamu, zai iya samun goyon bayan Buhari. Sai dai kuma, kankanewarsa da babbakewarsa a kowanne bangare da kuma ƙoƙarin zama mai ruwa da tsaki a kan duk wani abu zai iya kawo masa tarnaƙi. Yanzu haka rahotanni sun fara kewayawa cewar, wasu jiga-jigan APC sun fara tunanin barin jam’iyyar saboda irin ƙarfin da Tinubu yake da shi. Kwanakin baya, an kawo masa cikas a yunƙurinsa na ƙaƙaba wa Majalisun Tarayya shugabanci; idan bai bi a hankali ba, ɓangarori da yawa a cikin APC zasu dunƙule waje ɗaya domin su yi masa taron dangi a 2019.

©Mujallar Mikiya, 2016.

Twitter: @AmirAbdulazeez