Fassara

Saturday, August 22, 2020

Mutanen Duniya da Rabe-Rabensu

 Daga: Amir Abdulazeez

 

GABATARWA

A ƙiyasin da aka yi na shekarar 2013, aƙalla akwai yawan mutane sama da biliyan bakwai a faɗin wannan duniya da muke ciki. Waɗannan mutane suna nan a warwatse a cikin nahiyoyi da kuma ƙasashe a bayan ƙasa. Ko ba a gaya wa mutum ba, idan ya kalli fuskoki da ƙirar halitta ko yanayin halayyar mutane, zai tabbatar da cewa akwai bambance-bambance na asali, ƙabila, al’ada, addini da kuma tarbiyya ko tsari a tsakanin jama’ar duniya.

Duk da cewa za mu iya alaƙanta waɗannan bambance-bambance na halitta da ɗabi’u kai tsaye zuwa ga ƙudurar Ubangiji Mahalicci mai yin halitta yadda ya so, amma a ilmance ko a kimiyyance, za mu iya cewa waɗannan bambance-bambance sun samo asali ne daga irin muhallin da irin waɗannan mutane suka samu kansu tun daga kan zamanin kakannin kakanninsu. Muhalli, abinci, sana’a da auratayya na tsawon shekara da shekaru  sun taka muhimmiyar rawa ƙwarai da gaske wajen bai wa mutane daban-daban kamanninsu da ɗabi’unsu da suke da su  a yanzu. Misali, idan mu ka lura da launin fatar jikin waɗanda suke zaune a garuruwan da suke da nisa da ikiwaita (layin tsakiyar duniya wanda ya raba ta gida biyu), ta fi haske  a kan ta mutanen da suke zaune a kusa da ikiwaitar.

Wani abin lura shi ne, daga cikin abubuwan da suke kawo bambance-bambance a tsakanin mutane, akwai dalilai na halitta waɗanda Allah SWT ko dai ya samar a tattare da Ɗan Adam ɗin ko kuma a muhallinsa; akwai kuma dalilai na ƙirƙira, waɗanda Ɗan Adam ɗin ya samar da su domin samun damar yin irin rayuwar da ta dace da tunani da buƙatunsa ko kuma don ya samu damar yin rayuwa a inda ya samu kansa. Misali, mutanen da suke rayuwa a ƙuryar duniya daga Arewa wato kamar Russia, Canada da Norway, guraren da suke da matuƙar sanyi,ba za su iya rayuwa a gurare masu zafi kamar Mali, Sudan, Venezuela da sauransu ba, sai dai idan hakan ya zamar musu dole kuma a hakan ma sai sun ɗauki lokaci mai tsayi kafin su saba. Wani misalin kuma shi ne mutum mazaunin Yammacin Turai ko Amurka wanda ya gina rayuwarsa a kan abubuwa na fasahar zamani, ba zai iya wata rayuwar kirki a inda babu waɗannan abubuwa ba. Ko kuma mace da aka haifa ko aka raina a ƙasar Saudiyya (inda da ba a barin mata ko mota su tuƙa), za ta ji kunyar yin rayuwa a inda matan suke rayuwa rabin jikinsu a waje ba tare da jin kunya ba.

ƘABILUN MUTANEN DUNIYA

Masana daban-daban sun yi yunƙurin karkasa mutanen duniya izuwa ƙabila-ƙabila bisa la’akari da asalinsu, kamanninsu, launin fatar jikinsu, wani lokacin ma har da ɗabi’unsu. Sai dai kuma karkasa mutane bisa la’akari da launin fatar jikinsu shi ya fi shahara. Bisa hakan za mu ga cewar akwai baƙaƙe, jajaye da fararen mutane. A baƙaƙen ma akwai baƙaƙe wuluk, akwai kuma baƙi-baƙi da dai sauransu. Hakan ya samo asali daga canje-canjen guraren zama game da auratayya a tsakanin ƙabilun.

Idan aka dunƙule binciken masana waje ɗaya, za mu iya cewar baki ɗayan mutanen duniya sun kasu  izuwa ƙabila biyar kamar haka; ƙabilar baƙaƙen fata (Negro) da galibinsu ke zaune a Nahiyar Africa (banda Arewacin ta) da kuma Nahiyar Kudancin Amurka, ƙabilar jajayen fata (Indian) da mafi yawansu Indiyawa ne da tsofaffin mazauna Nahiyar Amurka, ƙabilar fararen fata (Caucasian) wanda da yawansu Turawa ne, ƙabilar masu launin fata ruwan ɗorawa (Mongolian) wanda mafi yawancinsu suke a Nahiyar Asiya da kuma sauran ƙabilu (Samolds, Esquimaux da Tartars).

ƘIDIDDIGAR YAWAN JAMA’AR DUNIYA:

Ƙiyasin yawan mutanen duniya na shekarar 2013 ya nuna cewa  akwai mutane biliyan bakwai da miliyan casa’in da biyar da dubu ɗari biyu da sha bakwai da ɗari tara da tamanin (7,095,217,980) a faɗin duniya. Idan muka yi la’akari da cewar yawan mutanen duniya ya na karuwa 1.1% a duk shekara wanda hakan na nuna cewar ana samun ƙarin yawan mutane miliyan 76 (kusan rabin yawan mutanen Najeriya) a kowacce shekara, za mu iya cewa yanzu hakan adadin mutanen duniya ya kai kusan biliyan 7.6.

Hukumar tsaro da bincike ta ƙasar Amurka (CIA) ta ƙiyasata cewar a duk minti daya, ana haihuwar mutane 255 a duk faɗin duniya, wato sama da mutane huɗu a kowacce daƙiƙa kenan. Sannan kuma hukumar bisa bayanai daga mafi yawancin ƙasashen duniya, ta ƙiyasta cewar mutane 107 ne suke mutuwa a kowanne minti a bayan ƙasa, wato kusan mutum biyu kenan a kowacce daƙiƙa. Idan muka ɗebe adadin yawan masu mutuwa daga adadin yawan waɗanda ake haifa a kowanne minti, za mu samu ragowar mutane 148. Wannan shi ne adadin  mutanen da duniya ta ke ƙaruwa da su duk bayan minti ɗaya.

A yanzu haka ƙasar China ita ta fi kowacce ƙasa yawan jama’a (Duba teburi na 7.1), yayin da ƙasar Birnin Vatican ta fi kowacce ƙasa ƙarancin jama’a.

Teburi na 1 : ƙasashe mafi yawa da ƙarancin jama’a

SN

KASA

YAWAN JAMA’A

NAHIYA

SHEKARAR DA AKA GINA ƘIYASIN A KAI

Ƙasashen da suka fi yawan jama’a

1

China

1,349,585,838

Asia

2013

2

India

1,220,800,359

Asia

2013

3

United States

316,668,567

America ta Arewa

2013

4

Indonesia

251,160,124

Asia

2013

5

Brazil

201,009,622

America ta Kudu

2013

Ƙasashen da suka fi ƙarancin jama’a

5

San Marino

31,817

Turai

2011

4

Palau

20,956

Oceania

2011

3

Tuvalu

10,544

Oceania

2011

2

Nauru

9,322

Oceania

2011

1

Vatican City

826

Turai

2011

 * Nigeria ita ce ta takwas a duniya da ƙiyasin yawan mutane 174,507,539.

A ɓangaren jinsi kuma, mafi yawan bincike-bincike da ƙididdiga sun nuna cewa mata sun fi maza yawa a duniya, to amma hakan ya danganta daga Nahiya zuwa Nahiya. A ɓangaren shekarun haihuwa kuma, matasa sun fi kowa yawa a duniya. Mutanen da shekarunsu ya kama daga 25-54 sun fi kowa yawa inda suke da 40.6% na yawan mutanen duniya (duba teburi na 2). Idan aka kalli jadawalin da ke teburin, za mu ga cewa dattawa waɗanda shekarunsu suka kai 65 zuwa sama ba su da yawa a duniya inda da kaɗan suka haura 8% na yawan mutanen duniya.

A duniya, masu shekarun haihuwa 29 zuwa 30 sun fi kowa yawa. A tsakanin maza, masu shekarun haihuwa 28 zuwa 29 sun fi kowa yawa, yayin da a tsakanin mata, masu shekarun haihuwa 30 zuwa 31 sun fi kowa yawa a cikin jimmillar mutanen duniya.

Teburi na 2 : Rukunin Shekarun Haihuwar  Jama’ar Duniya da Yawansu

SN

RUKUNIN SHEKARU

KASO CIKIN YAWAN MUTANEN DUNIYA

ADADIN MAZA (Miliyan)

ADADIN MATA (Miliyan

1

0-14

26.0%

953.5

890.4

2

15-24

16.8%

614.6

580.0

3

25-54

40.6%

1,454.9

1,426.8

4

55-64

8.4%

291.5

305.2

5

64 zuwa sama

8.2%

257.1

321.8

Dangane da sana’a, 48% na mutanen duniya sun dogara da kansu yayin da 52% (matasa-39.9%, tsofaffi-12.21%) sun dogara ne da waɗansu su ɗauki nauyinsu wanda suka haɗa da iyayensu, ‘ya ‘yansu, ‘yan uwansu ko kuma gwamnati a wasu ƙasashen. Adadin mazauna birane a duniya ya kai 50.5%, yayin da mazauna ƙauyuka su ka kai 49.5%.

Teburi na 3: Mutanen ƙasashen da suka fi yawan rai da kuma saurin mutuwa

SN

KASA

SHEKARU

NAHIYA

Ƙasashen da suka fi tsawon rai

1

Monaco

89 zuwa 90

Europe

2

Macau

84 zuwa 85

Asia

3

Japan

84 zuwa 85

Asia

4

Singapore

84 zuwa 85

Asia

5

San Marino

83 zuwa 84

Europe

Ƙasashen da mutanensu suka fi mutuwa da wuri

5

Swaziland

31 zuwa 32

Africa

4

Angola

38 zuwa 39

Africa

3

Zambia

38 zuwa 39

Africa

2

Lesotho

40 zuwa 41

Africa

1

Mozambique

41 zuwa 42

Africa

Ƙididddiga da ƙiyasi sun nuna cewar a duk mutane 1000 da aka haifa a faɗin duniya, 37 zuwa 38 suna mutuwa da zarar an haifesu ko kuma kafin su cika shekara ɗaya da haihuwa. Mata sun fi maza taswon rai a mafi yawan ƙasashen duniya. A duniya baki ɗaya, a na ƙiyasta cewar mace ta kan rayu tsawon shekaru 70 zuwa 71 a duniya, yayin da namiji ya kan rayu shekaru 66 zuwa 67 (Duba teburi na 3).

Wani abin da ya kamata mu lura da shi shi ne, abubuwan da su ke sanyawa mutum ya yi tsawon rai a duniya sun haɗa da ingantacce da wadataccen abinci, kyawawan dabarun kiwon lafiya da ingantaccen muhalli da sauran abubuwa masu inganta rayuwa. A ɗaya hannun kuma cututtuka da annoba, ƙarancin abinci, yaƙe-yaƙe da rigingimu da dai sauransu su kan kawo rashin tsawon rai.

Dalilin da ya sa mata su ka fi maza tsawon rai shi ne; kullum maza suna waje wajen nema abinci, rayuwarsu ta na cikin hadari. Yawancin sojoji masu aiki a fagen daga maza ne. Sannan kuma yawancin aiyuka masu haɗari kamar tuƙin jirgin ruwa da na sama, haƙo fetur da ma’adinai da sauransu duk maza sun fi yawa a cikinsa. Sannan kuma mafi yawancin mata a mafi yawan ƙasashe a duniya, mazauna gida ne, da yawa ba su ma da aikin yi, da mazajensu suka dogara.

Akwai wani abu mai muhimmanci da ya kamata mu yi la’akari da shi. Wannan kuwa shi ne dalilai da suke kawo wa a samu yawan jama’a ko ƙarancin jama’a a guri. Akwai dalilai na halitta, akwai kuma dalilai na sababin Ɗan Adam.

Abubuwa kamar yanayi mai kyau wanda bai ƙunshi matsanancin sanyi ko zafi ba, ƙasar noma mai kyau, rashin tuddai masu tsayi ko kwarrai masu zurfi waɗanda ka iya kawo tarnaƙi ga ginin muhalli, rashin matsalolin muhalli kamar zaizayar ƙasa, kwararowar Hamada, rashin ruwa, girgizar ƙasa, aman wuta daga duwatsu da sauransu; duk dalilai ne na halitta masu sanyawa a samu yawan jama’a a wani yanki. A gefe ɗaya rashin Waɗannan abubwa ka iya jawo kauracewar jama’a daga guri. Sai dai kuma ko da guri ba shi da yanayi na halitta mai kyau, akwai dalilai na tattalin arziki da ka iya jawo hankalin mutane zuwa gurin. Misali a shekarun baya, yankin Alaska mai matuƙar sanyi a ƙasar Amurka ba shi da yawan jama’a saboda yawan sanyinsa, amma kuma da aka gano man fetur da wasu ma’adinai a yankin, sai mutane suka dinga komawa domin samun aiyyukan yi da damammaki na bunƙasa arzikinsu. Bayan haka kuma, haka kawai ma Ɗan Adam ya kan yi bakin ƙoƙarinsa wajen ganin ya ɓullo da dabarun zama a yankin da ya samu kansa a ciki komai tsananinsa da wahalar sha’aninsa (Hoto na 1).

Hoto na 1: Yankin Positano kenan a ƙasar Italy inda mazauna yankin suka ɓullo da dabarun yin gidaje a kan duwatsu da tsaunuka domin wajen ya zame musu gida. Wannan dabara tasu sai ta bayar da wata sha’wa da ƙayatarwa ga yanayin gidajen.

Abubuwa kamar wadatar aiyukan yi, masana’antu, zaman lafiya da rashin fitintunu, ingantattun hanyoyin sufuri da na sadarwa, al’adu da kyawun mu’amalar mutanen guri kan jawo hankalin jama’a don su zauna a guri. Yanayin gwamnati da tsarin dokokin ƙasa kan kawo shigowa ko ƙauracewar jama’a a wani yanki. Misali wasu ƙasashe basu da maraba da baƙi saboda dalilai na al’adu, tsaro ko ra’ayi kawai yayin da wasu ƙasashen basu da ƙyamar baƙi ko kaɗan. Wasu ƙasashen ma su kan bayar da dama mutum ya zama ɗan ƙasa na dindindin ba tare da shan wata wahala sosai ba.

ADDINAN MUTANEN DUNIYA

Dangane da addini, za mu iya kasa mutanen duniya gida uku; masu addini tare da yi masa biyayya sau da ƙafa, masu addini amma bai damesu ba, sai kuma marasa addini da waɗanda basu yarda da samuwar Ubangiji ba. Hasashe daban-daban na nuna cewa masu addini a suna kawai amma ba tare da ya damesu ba sun fi kowa yawa a duniya kuma mafi yawancinsu suna zaune a yankunan Europe, Amurka ta Arewa, Australlia, sassan Amurka ta Kudu da wasu yankunan Asia. Misali, Birnin Rome na ƙasar Italy shi  aka ayyana a matsayin cibiyar Kiristanci ta duniya, amma kuma ana lissafa mafi yawan mutanen Birnin Rome ɗin da ma ƙasar Italy baki ɗaya a matsayin waɗanda addini bai dama ba. Hakazalika ana lissafa musulman sassan da ƙasar France ta mulka a Africa, musulman sassan Europe da Amurka har ma da na Africa ta Arewa da wasu ɓangarorin Asia a matsayin waɗanda addinin bai dame su ba a aikace sosai.

Za mu iya kasa addinan duniya kamar haka; saukakkun addinai waɗanda za a iya alaƙanta asalinsu da wani Annabi ko Manzo, misali Musulinci, Kiristanci da Yahudanci. Akwai kuma addinan gargajiya waɗanda mafi yawancinsu suka mayar da hankali kan al’adun iyaye da kakanni kuma suka ƙunshi bautar abubuwa marasa rai ko hankali kamar wuta, rana, dabbobi da sauransu, misalin waɗannan addinai su ne Hindu da Sikh; akwai kuma addinan da aka ginasu a kan hikima, tunane-tunane ko koyarwar wasu mashahuran mutane da suka gabata; misali kamar addinin Taoism wanda aka gina a kan koyarwar Lao Tzu, Cofucism daga babban malamin China Confucius, Bhuddism daga Gautama Siddarta-Buddha. Sai dai kuma wasu daga cikin irin waɗannan mutane su kan yi da’awar cewar sun samu wannan koyarwar tasu daga wani wahayi kamar Buddha. Akwai kuma mutane marasa addini kwata-kwata.

Zai yi wahala a iya tantance yawan aaddinan da suka wanzu a doron ƙasa tun daga lokacin da aka fara rubuta tarihin duniya izuwa yanzu, saboda wasu addinan ma ba a taɓa ko jin labarinsu ba, amma a halin yanzu addinan da suka fi kowanne yawan mabiya a duniya guda bakwai ne (duba teburi na 4)    

Teburi na 4: Manyan Addinan Duniya da Kason Mabiyansu

SN

ADDINI

KASON MABIYA CIKIN YAWAN MUTANEN DUNIYA

1

Kiristanci

33.90%

2

Musulunci

22.74%

3

Hindu

13.80%

4

Bhuddism

6.77%

5

Sikh

0.35%

6

Yahudanci

0.22%

7

Baha’i

0.11%

8

Sauran addinai

10.95%

9

Marasa addini

9.66%

10

Waɗanda basu yarda da samuwar Allah ba

2.01%

Wasu abubuwan da zamu lura da su sune; akwai addinan da suka kasu zuwa ɗarika-ɗarika, akwai kuma addinnan da babu inda zaka samesu sai a ƙasa ɗaya ko biyu. Bayan haka akwai addinan da suka yawaita ko suka yi ƙaranci sannan kuma suke da tasiri ko rashinsa a gurare da yawa saboda dalilai na siyasa ko mulkin mallaka.

Kiristanci ya kasu izuwa ɗariku da yawa, amma shahararrun sune kamar haka; Catholic, Protestant, Orthodox da Anglican. Shi kuma Musuluci ya kasu izuwa Sunni da kuma Shi’a, duk da cewa akwai wasu ƙananan dariku ko ɓangarori da basu da wani muhimmin tasiri a matakin ƙasa da ƙasa.

Bisa binciken shekarar 2013, duk duniya babu inda ake da yawan Musulmi kamar Indonesia inda ake ƙiyasin suna da yawan musulmi sama da miliyan 215, sai ƙasar Pakistan wacce take da adadin musulmi kusan miliyan 190, sai ƙasar india mai sama da miliyan 164. Nigeria tana da yawan musulmi sama da miliyan 85. Guraren da suka fi ƙarancin mabiya addinin islama sun haɗa da ƙasashen Arewaci da gabashin Turai, ƙasashen kudanci ko Latin America da yankin Australlia. Ƙasashen da suke da kason musulmi 97-100% su ne Saudi Arabia, Turkey da Afghanistan, iran da Pakistan. ƙasashen da yawan mabiya shi’a ya kai 50% ko yah aura su ne Iraq (65%) da kuma iran (89%).

Inda ya fi ko’ina yawan mabiya addinin kirista a hasashen shekara ta 2013 sune ƙasar Amurka (miliyan 252), Brazil (miliyan 180) sai Mexico (miliyan 106). Yawan kiristocin Nigeria ya kai kusan miliyan 70. Ƙasashen da suke da adadin mabiya addinin kirista daga 97-100% sun haɗa da Belgium, Bolivia, Denmark, Venezuela; guraren da mabiya addinin kirsita suka fi ƙaranci sun haɗa da mafi yawancin Nahiyar Asia sai kuma Arewacin Africa.

Mafi yawan mabiya addinin Hindu a ƙasar India suke inda yawansu a ƙasar ya kai kusan biliyan ɗaya domin sun haura miliyan 995. Ragowar mabiya addinin Hindun sun warwatsu a ƙasashe maƙotan India ɗin da sauran sassan Nahiyar Asia da kuma duniya, sai dai basu da wani yawan a zo a gani. Duk da cewa gwamnatin ƙasar China ba ta ɗauki addini a bakin komai ba, amma akwai mabiya addinin Bhuddha da yawa  a ƙasar da kuma sauran sasaan Nahiyar Asia.

Addinin Yahudanci shi ne wanda mabiyansa suke biyayya ga Annabi Musa kuma suke yin hukunci da littafin Attaura wanda suke ƙira Talmud. Mafi yawancinsu suna zaune ne a ƙasar Israel, duk da cewa akwai su a warwatse a Yammacuin Turai da Amurka. Akwai su a ƙasashe irinsu Germany, France da dai sauransu.

Akwai ƙasashen da basu damu da addini ba, wasu ma har haramtawa ko ƙyamar shi suke yi. Misali ƙasar Russia da sauran ƙananan ƙasashen rugujajajeiyar Tarayyar Soviet, musamman masu biyayya ga tsarin kwaminisanci, basu yarda da addini ba kuma yinsa ma laifi ne. Duk da cewa an samu sauye-sauye a yanzu, to amma har yanzu addini ba shi da tasiri a irin waɗannan ƙasashe. A ƙasar China kuwa, ba hana addinin aka yi kai tsaye ba, amma al’amuran ƙasa da kishin ta gaba yake da addini a al’amuran ƙasar. Ba ka da ikon ka bar ofishin gwamnati ka tafi masallaci ko wajen bauta, amma ka iya yin bautar ka a wani lokacin daban. Su kuwa ƙasashe irinsu America da mafi yawancin Nahiyar Turai, mafi yawan mabiya addinai a ƙassahen, suna yi ne kawai a suna ko a baki. Misali zaka iya samun mabiyin addinin kirista ya haura shekaru goma bai je coci ba amma wai sunan shi kirista ne. Sannan kuma addininsu ba ya hanasu duk wata irin baɗala da fitsara, kai a taƙaice ma wasu basu ma san koyarwar addinin ba kwata-kwata. A irin waɗannan ƙasashe ‘yancin mutum ya yi abin da ya ga dama shi ne gaba da komai.

Mulkin mallaka ya taimaka ƙwarai da gaske wajen yaɗa addinin Kiristanci a yankunan Africa, Amurka ta Arewa da ta Kudu da kuma wasu sassan Asia. Yanayin kasuwanci da hijirar mutane ta taimaka wajen yaɗa addinin Musulunci a Africa ta Yamma.

YARUKA DA AL’ADU

Aƙalla yarukan da ake amfani dasu a duniya a yanzu sun kai kimanin 7,100. 80% ko kuma guda 5,680 daga cikin waɗannan yaruka, bai wuce mutum 100,000 ne zuwa ƙasa suke amfani da kowanne ɗaya daga cikinsu ba. Yaruka 50 daga ciki, mutane ƙalilan ne sosai kawai suke jinsu. Misali garuruwa da suke keɓe daga wasu garuruwan sakamakon manyan tsaunuka da tsuburai, dazuka da sauran abubuwa su kan ƙirƙiri yarukansu daban- ƙasar Papua New Guinea misali ta na da yaruka daban-daban har 836 sakamakon irin haka. Harsuna 150 zuwa 200 suna da sama da mutum miliyan guda mai jin kowannensu. Ana amfani da kimanin yaruka 2300 a Nahiyar Asia, 2150 a Africa, 1300 a Pacific, 1060 a nahiyoyin Amurka ta Arewa, Kudu da tsakiya, sai kuma 280 a Nahiyar Turai.

Dangane da amfani da yare, a kan kasa harshe gida biyu; yaren asali ko na haihuwa da kuma yare na biyu wanda aka koya daga baya kuma ake amfani da shi akai-akai. A matakin ƙasa kuwa akwai yaren ƙasa wanda gwamnatin ƙasa ta yarda da shi, kamar misalin Turanci a Najeriya.

Dangane da yaren haihuwa na asali, harsunan da suka fi yawan masu amfani da su a duniya sun haɗa da; Mandarin Chinese (12.44%), Spanish (4.85%), Arabic (3.25%), Hindu (2.68%), Bengali (2.66%), Portugese (2.625), Russian (2.12%), Japanese (1.8%), German (1.33%) Javanese (1.25%).

Yarukan da aka fi amfani da su a duniya baki ɗaya ko da kuwa ba lallai su kasance yarukan asali ga masu amfani da su ɗin ba sun haɗa da yarukan Majalisar Ɗinkin Duniyar nan guda shida- Arabic, Chinese, English, French, Russian da kuma Spanish. Waɗannan harsuna guda shida sun kasance yaren asali ko yare na biyu ga kusan rabin mutanen duniya kuma sun kasance yaren gwamnati a sama da rabin ƙasashen duniya.

SAURAN ABUBUWA

Karatu da rubutu: ƙiddiddiga ta nuna cewa, sama da mutane miliyan 6,700 na duniya sun iya karatu da rubutu wato 84.15% na adadin yawan mutanen duniyar baki ɗaya. Adadin waɗanda basu iya karatu da rubutu ba bai kai miliyan 800 ba a cewar Hukumar Ilimi Ta Majalisar Ɗinkin Duniya (UNESCO).

Kashi 75% daga cikin mutanen duniya kusan miliyan 800 da basu iya karatu da rubutu ba, sun fito ne daga ƙasashe 10 (India, China, Pakistan, Bangaladesh, Nigeria, Ethipia, Egypt, Brazil, Indonesia da kuma DR Congo). Kashi 65% na waɗanda basu iya karatu da rubutu ba mata ne. Bincike ya nuna cewa babu inda jahilci ya fi katutu a duniya kamar a tsakanin mazauna Kudanci da Yammacin Asia da kuma yankin Africa Kudu da Sahara.

Cututuka: aƙalla kusan mutane miliyan 35 ne ke dauke da cutar HIV/AIDS  a duniya a yanzu. Kuma daga ɓullar cutar zuwa shekarar 2009, cutar ta hallaka mutane sama da miliyan biyu a cewar hukumar lafiya ta duniya (WHO).

Teburi na 5: Cutar HIV a Duniya

 

SN

KASA

NAHIYA/YANKI

KASO CIKIN YAWAN MUTANEN ƘASA

Ƙasashen da suka da mafia yawan kaso na masu cutar HIV/AIDS

1

Swaziland

Kudancin Africa

26.50% (Kowanne mutum ɗaya cikin hudu)

2

Lesotho

Kudancin Africa

23.10% (Kowanne mutum ɗaya cikin hudu)

3

Botswana

Kudancin Africa

23.00% (Kowanne mutum ɗaya cikin hudu)

4

South Africa

Kudancin Africa

17.90% (Kowanne mutum ɗaya cikin biyar)

5

Zimbabwe

Kudancin Africa

14.70% (Kowanne mutum ɗaya cikin shida)

Ƙasashen da suke da mutane da yawa masu dauke da HIV/AIDS

1

South Africa

Kudancin Africa

6,070,800

2

Nigeria

Yammacin Africa

3,426,600

3

India

Kudancin Asia

2,085,000

4

Kenya

Gabashin Africa

1,646,000

5

Mozambique

Kudancin Africa

1,554,700

Ƙasashen da aka fi samun asarar rayuka a dalilin HIV/AIDS

1

Nigeria

Yammacin Africa

239,700

2

South Africa

Kudancin Africa

235,100

3

India

Kudancin Asia

135,500

4

Tanzania

Kudancin Africa

80,000

5

Mozambique

Kudancin Africa

76,800

 

 

A KULA: Dukkan wannan bayanai an samesu ne daga tarin bincike daga rahotanni da wallafe-wallefen da yawansu ba zai bari a zayyanosu a nan ba. Amma dai wallafe-wallefen da kasashen da aka ambata suka samar da kansu da kuma na Majalisar Dinkin Duniya suna daga ciki.

 Twitter: @AmirAbdulazeez   

Tuesday, June 5, 2018

Ina Dimokraɗiyyar Take?


29 ga Mayun 2018


Daga: Amir Abdulazeez

M
afi yawancin mutanen Najeriya su kan fahimci cewa Ranar Dimokraɗiyya ta zagayo ta hanyar kafafen yaɗa labarai musamman a jaridu. Kamar kowacce shekara, wannan lokacin ma shafukan jaridun ƙasar nan sun cika taf, wasu ma ba masaka tsinke da saƙonnin taya juna murna da ‘yan siyasa suke wa junansu ko kuma ‘yan korensu da masu neman gindin zama a wurinsu suke yi. Wani abin la’alkari ma shi ne, mafi yawan masu taya murnar da wasu waɗanda ake taya wa murnar ma, ko dai basu fahimci ma manufofin dimokraɗiyyar ba, ko kuma aƙidu da aiyukansu sun yi hannun riga da manufofinta.

Lokacin da rahotanni suka fita a kwanakin baya kan ƙin bayyana da Babban Sufeton ‘yan sanda na ƙasa gaban Majalisar Dattawa ta ƙasa ba tare da wani ƙwaƙƙwara ko karɓaɓɓen dalili ba, da yawa sun shiga ruɗani a kan ko dimokraɗiyya tana aiki a ƙasar nan. Idan har babban mai tabbatar da doka da oda na ƙasa zai yi irin haka, ko ma bisa wacce irin hujja ko uzuri ya yi hakan, dole a dinga samun shakku a cikin tsarin da muke tafiya a kai. A kowacce ƙasa, majalisa ita ce zuciyar dimokriyya komai lalcewar ta. Idan har za a wofantar da ita ko a dinga raina ta ta irin wannan sigar, dole a ji tsoron makomar dimokraɗiyyar ita kanta.

An yarda cewa, majalisar ƙasar nan ta zubar wa da kanta mutunci da daraja tuni a cikin shekarun da suka gabata, amma dai a dokar ƙasa, kusan ita ce gaɓar dimokraɗiyya mafi amfani, don haka ta cancanci  a ce tana da girma da ƙarfin da zata iya gayyatar ko da shugaban ƙasa ne a kowanne lokaci, ba ma wani na ƙasa da shi ba ko ma waɗanda ya naɗa ba. Girmama majalisa a matasyin gida ya sha bambam da girmama ɗai-ɗaikun mutanen da suke cikinta. Wai tukunna ma, bai ishi dimokraɗiyyar mu abin Allah wadai ba a ce tsawon shekarunnan, muatanen da ake da shakku a kansu ne kullum suke zama ‘yan majalisu, kuma babu alamun hakan zai kau a nan kusa?

Daya daga muhimman abubuwan da suka faru kafin bikin Ranar Dimokraɗiyyar wannan shekara, shi ne zaɓukan shugabannin jam’iyyar APC mai mulki na mazaɓu da ƙananan hukumomi a faɗin ƙasa a karo na farko tun bayan shekarar 2015. A hankalce, ya kamata wannan ya zama wani ma’auni na irin ci gaba ko ci bayan da dimokraɗiyyarmu take samu. A mafi yawan waɗannan zaɓukan, babu wani abu da ya nuna tasake zani ta fuskar inganci ko tsari. Waɗanda suka shaida yadda zaɓukan suka ƙasance a wasu ƙananan hukumomi zasu iya bada hujjar cewa babu abin da ya gudana sai son zuciya a mafi yawan gurare.

Farko dai, abin da ya faru a zaɓukan shugabancin na APC ba wani abu ne sabo ko baƙo ba, abu ne da aka saba da shi tun ba yau ba. Abin baƙin cikin kawai shi ne, yadda hakan ya ma zama jiki har ake kallonsa a matsayin shi ne ma dimokraɗiyya da ƙa’idojinta a kusan kowacce jam’iyya ta ƙasar nan kuma muke murna muna farin ciki kowacce shekara. Da wahala mutum ya iya tuna wani lokaci da wata jam’iyya a Najeriya ta gudanar da sahihin zaɓukan shugabancinta cikin lokaci da ƙa’ida, gaskiya da adalci a faɗin ƙasa ba tare da kama-karya, son zuciya da saɓa ƙa’idar ita kanta jam’iyyar da hukumar zaɓe ta ƙasa ba.

Wani lokacin idan mutum ya zauna, sai ya dinga tunanin wai shin nawa ne daga cikin mutanen da suka zama shugabannin ƙasa, gwamnoni da ‘yan majalisu daga shekarar 1999 zuwa yanzu idan da ingantaciyyar dimokraɗiyya ake aiwatarwa a Najeriya? Idan da jam’iyyu suna yin zaɓukan fidda gwani na adalci, mutane nawa ne zasu samu takara tun ma da farko? Mutane nawa ne suka ci zaɓe aka ƙwace musu a 2003 da 2007? Idan da doka da oda na aiki yadda ya kamata, nawa ne zasu kammala wa’adin mulkinsu lafiya?

Yayin da muke murna da cikar dimokraɗiyya shekaru 19 a Najeriya, har yanzu gwamnati ba ta bada gamsasshe ko cikakken martani  a aikace kan zarge-zarge daga cikin gida da ƙasashen ƙetare kan bisa yadda sojoji ke cin zarafin farar hula a yayin gudanar da aiyukansu a Arewa maso Gabas ba. Har yanzu muna fama da tuhume-tuhume kan yadda ake saɓa wa umarnin kotuna a wannan dimokradiyyar da muke ta murna a kai. Gidajen bursun dinmu sun zamo wasu gurare da ake wa kallon na cin zarafin bil adama ba are da wani ƙwaƙƙwaran mataki ba. Waɗannan sune kaɗan daga cikin abubuwan da ya kamata dimokraɗiyyar mu ta mayar da hankali a kai.

Me muke wa murna duk shekara? Muna murna ne ga ainihin ci gaban da aka samu a dimokraɗiyyance ko kuwa muna farin ciki ne da ƙarewar mulkin soja? Daga 1999 zuwa yanzu, wane ci gaba muka samu ta fuskar faɗin albarkacin baki, dimokraɗiyyar cikin gida a jam’iyyu, mulki da adalci da gaskiya, bai wa kowanne bangaren gwamnati hakkinsa, gyare-gyaren kundin dokokin zaɓe, daidaito tsakanin ‘yan ƙasa a gaban doka, da sauran rukunnan dimokraɗiyya? Wane ma’uanai muka samar wajen auna ci gaba ko ci bayan da muke samu ta fuskar dimokraɗiyya?

Yayin da muke murna da wannan dimokraɗiyyar, ya zama wajibi mu tuna cewa har yanzu yawan dukiyarka ne abin da ya fi komai tasiri wajen yin nasara a zaɓe; mutane suna cin zaɓe ba tare da wata manufa ba; shugabannin jam’iyyu a dukkan matakai suna samuwa ne ta hanyar nune ba zaɓe ba; iyayen gida su suke juya siyasa ba jama’a ba; mafi yawan ‘yan Najeriya basu da cikakken ilimin siyasa da zaɓe; babu wani hukunci da ake yi wa masu maguɗin zaɓe; zaɓukan ƙananan hukumomi sun koma wasan yara; ana amfani da ƙarfin mulki wajen murƙushe marasa mulki a zaɓe; kotuna da yawa ba sa cikakken adalci ga korafe-korafen zaɓe; hukumar zaɓe ba ta da cikakken ‘yanci, da sauran wasu tarin matsaloli.

Kamar ko yaushe, Ranar Dimokraɗiyya ta wannan shekara ba ta wuce wani lokaci na shugabanni da ‘yan siyasa cika baki kan aiyukan da suka yi  a gwamnatance wanda ma’aikatansu suka tsara musu a rubuce ba. Wasu daga cikin waɗannan aikace-aikace ma maimaita zancensu kawai ake yi kowacce shekara. Kodayake hakan ba aibu bane tunda ranar dama ta kan dace da lokacin da suke bukukuwan cikarsu wasu shekaru  a kan mulki, amma ya kamata lokacin ya fi maida hankali wajen duba ci gaban mu wajen kyautata mu’amalarmu  a ɗaiɗaiku da kuma ƙasa baki ɗaya ta fuskar dimokraɗiyya.

Yin murna da mulkin farar hula na tsawon shekaru 19 a ƙasar da aka yi shekara da shekaru a karkashin mulkin soja ba zai zama kuskure ba, amma ya kamata murna ta wuce gaban bada hutu, gabatar da ƙasidu ko ɓarnatar da kuɗaɗe wajen talla a shafin jaridu. Ya kamata ta zama wani yanayi na duba yadda wannan mulki na farar hula ya kawo ci gaba wajen bai wa mutane dama ba tare da nuna bambanci ba.

Ba wanda zai tsammaci dimokraɗiyyarmu ta zamo ba ta da wata matsala ko aibu ba a cikin shekaru 19 kacal , amma dai ya kamata a tashi tsaye. Wane yunƙuri muka yi a cikin waɗannan shekaru? Waɗanne nasarori muka samu? Ina kura-kuran suke?

Twitter: @AmirAbdulazeez

Wednesday, November 15, 2017

Ganduje, Masu Shayi da Makomar Jihar Kano

15 Ga Nuwamba, 2017



Daga: Amir Abdulazeez

L
okacin da aka rawaito cewar Gwamnatin Jihar Kano ta kashe Naira miliyan 208 wajen tallafa wa masu sana’ar shayi da burodi guda 5,200 a faɗin Jihar Kano, mutane da yawa sun tofa albarkacin bakinsu. Wasu da yawa sun kushe ko sun yaba wa abin saboda dalilai na siyasa, wasu kuwa saboda wasu manufofi masu kyau da suke ganin hakan ya saɓawa ko ya yi dai-dai da su. Amma babban abin la’akari shi ne, mu manta da waɗanda suka samar da tsarin ko jam’iyyarsu, mu kalli tsarin a ƙashin kansa, mu ga ta ina zai samar wa da Jihar Kano ci gaba? Kar mu manta fa yanzu ba irin da bace da gwamnati take da kuɗi faca-faca da zata yi wadaƙa dasu.

Farko dai, irin wannan tsarin na tara mutane a raba musu tallafi da kuɗin gwamnati, ba baƙon abu bane a Jihar Kano. Mafi yawan masu kushewa saboda dalilai na siyasa, su ma nasu gwanayen sun yi irinsa a baya. To amma, ya kamata mu yi tunani, wane irin ci gaba Jihar Kano ta samu a tsawon wannan shekaru ta dalilin biliyoyin kuɗaɗe da aka kashe wajen yin wannan tallafi? Tun farko ma, menene tabbacin cewa waɗanda ake bai wa irin wannan tallafi sun cancanceshi?

Misali, ta yaya zamu gane cewa waɗanda Gwamna Ganduje ya tallafawa kwanakin da suka wuce masu shayin ne na gaske, ba wasu ‘yan koren siyasa aka zaɓo ba? Menene tabbacin cewar ba zamu kuma ganin fuskokin waɗancan masu shayi ba gobe idan za a bada tallafi ga masu gyaran babura? Kowanne mai shayi ake tallafawa, ko kuwa sai wanda ba shi da jari kuma yana so ya haɓɓaka sana’ar tasa da gaske? Wane tanadi gwamnati ta yi don sa ido wajen ganin an yi amfani da kayan da ta raba maimakon sayar da su? Shin gwamnati za ta dinga bin kowacce sana’a ne tana bai wa masu ita tallafi? Shin menene haƙƙin waɗanda suma masu shayi ne kuma ‘yan Kano mabuƙata kuma basu samu wannan tallafi ba?

Shin rabawa masu shayi kayayyaki ne zai gyara sana’ar ko kuwa tsayawa a kalli tushen me yasa tattalin arzikin ya kai lalacewar da har sai an tallafa musu ya kamata? Shin gwamnati ta sallama cewar bata da wasu manufofi ingantattu da zasu inganta tattalin arziki ta yadda kowa zai tallafi kansa ba tare da an bi mutane ana raba musu kuɗaɗe da kayan tallafi ba? Ina muka kwana kan burin gwamnati na ganin mutane ne zasu zamo masu tallafar gwamnati da kuɗin shiga a maimakon ita ta ɗebi kuɗaɗenta tana raba musu? Wannan rabe-raben tallafi, da wace manufar ci gaban Kano mai ɗorewa ya dace kuma ta ya zamu auna nasararsa ga wannan manufa a yanzu ko a nan gaba?

Da zarar mutum ya yi ƙoƙarin nemo amsoshin wannan tambayoyi sai ya ga gabaɗaya abin ba shi da wata muhimmiyar manufa ta ci gaba a gajere ko dogon zango. Muhimmiyar manufarsa ita ce siyasa. Tsirarun da Allah Ya taimaka suka yi amfani da nasu tallafin ta hanya mai kyau, nasu ya ɗore. Ba za ce gwamnati ta daina bada tallafi ba duba da irin yanayin al’ummarmu; to amma ba kara zube barkatai ba don siyasa. A tsaya a kalli abin bisa manufa ta ci gaba mai ɗorewa kuma a yi abin a muhallinsa ga waɗanda zai amfanar.

Jiha kamar Kano wacce aka yi wa nisa kuma take da burin ganin ta cimma takwarorinta irinsu Lagos, Ogun da Rivers, ya kamata a ce tana da wani tsarin ci gaba mai ɗorewa wanda babu siyasa a cikinsa maimakon a same ta tana kashe Naira Miliyan 208 wajen rabawa ‘yan koren siyasa da aka kira da masu shayi ba.

Kimanin watanni biyar baya, wani bincike ya kai mu ga zagaya wasu muhimman madatsun ruwa na Jihar Kano. A yayin binciken wanda ya ƙunshi wasu malamai da ɗalibai masu sha’awar nazari kan harkokin ruwa  da tusarrufinsa daga Jami’ar Bayero, ya maida hankali a cikin abubuwa da dama, wajen gano gazawar madatsun ruwanmu wajen biyan buƙatun Jihar Kano na tattalin arziki da kuma na yau da kullum duk kuwa da yawansu da kuma girmansu.

Kididdiga ta nuna  cewar duk Najeriya, babu Jihar da take da yawan madatsun ruwa kamar Kano. Jihar tana da kimanin madatsu 26 wanda girman kowanne ya kama daga ‘yan hektoci zuwa aƙalla hekta 17,800. Wasu daga cikin madatsun kamar Watari, Tiga, Challawa-Goje, Bagauda, Tomas, Karaye, Pada, da sauransu, suna daga cikin mafi girma a Najeriya. To amma duk da haka, gwamnati ba ta zuba isasshen jari ko yin wani tsari nagartacce da zai sa noman rani ya mamaye ƙananan hukumomi 38 na wajen birni da muke dasu ba. Duk da wannan ni’ima da dama, matasan Kano suna zaune cikin rashin aikin yi ta yadda a yanzu jihar ana ƙaddara ta a matsayin kan gaba wajen mafi yawan masu shaye-shaye a faɗin Najeriya.

Me ya kawo wannan? Rashin wani tartibin tsari mai ɗorewa na ci gaban jihar wanda za a dinga aiwatarwa cikin shekaru. Ci gaban Jihar Kano a yanzu ya dogara kacokam a kan gwamnan da yake mulki; abinda ya ga dama shi za a yi ko da kuwa akwai dubannan abubuwan da suka fi shi muhimmanci. ‘Yan majalisunmu da sauran masu ruwa da tsaki kuwa sun zama hoto. Idan banda haka, babu wani dalili da zai sa gwamna ya ɗebi biliyoyin nairori ya gina gadar sama ko ya sayi motoci ya dinga rabawa masu ƙarfi ko kuma ya sayi kayayyaki yana rabawa magoya bayansa da sunan masu shayi, bayan asibitocinmu suna zaune babu wadatar magani da isassun ma’aikata, makarantunmu suna zaune babu kujeru da ingantattun malamai, masana’antunmu suna nan a rufe a lalace, sannan dubban matasa suna zaune babu abin yi ba.

Mun ga lokacin da gwamnati ta dinga ware biliyoyin Naira tana fasa tituna masu kyau da sunan rabasu biyu a ƙananan hukumomin da babu asibiti ko kuma ake da asibitocin da ba zaka sayesu Naira miliyan guda ba. Magoya baya kuma suna tafi suna murna. Gudanar da ci gaban Kano kusan ya dogara kacokam a kan siyasa. Kowanne gwamna idan ya zo burinsa ya shimfiɗa sabon tsarinsa wanda yake cike da burin gina siyasarsa da ta magoya bayansa fiye da burin gina jiharsa da al’umma. Ya ishi gwamnoninmu abin kunya a ce daga 1999 zuwa yanzu, a irin albarka da tagomashin da Allah Ya yi wa Kano, amma wai ba zamu iya biyan albashi ba ba tare da mun jira kuɗi daga Gwamnatin Taryya ba.
  

Twitter: @AmirAbdulazeez   

Tuesday, July 4, 2017

Ɗanmasanin Kano: Ba Rabo da Gwani ba!

04 Ga Yuli, 2017



Daga: Amir Abdulazeez

A
na gobe ƙaramar Sallah, na kai wa wani yayana da yazo Kano daga Abuja ziyara, sai muke tattaunawa kan dalilin da yasa sauran yankunan Najeriya suka fi Arewa ci gaba irin na zamani duk kuwa da cewa akwai mashahuran mutane da suka samu damammaki daban-daban a yankin fiye ma da na kowanne yanki a tarihin Najeriya. Bayan mun koka kan yadda almajiranci, jahilci, talauci, gurɓatacciyar siyasa da sauransu suke neman kassara yankin na Arewa, sai kuma muka duƙufa wajen gano bakin zaren.

Muhimmin abin da muka cimma  a ƙarshe shi ne mafi yawancin mutanen Arewa basu da sha’awar kafa tarihi ko barin wani abu da za a dinga tunawa dasu bayan sun mutu. Maimakon haka, yawa-yawansu sun fi sha’awar a tunasu da irin tarin dukiyar da suka mallaka ko kuma irin manya-manyan muƙamai ko sarautu da suka riƙe da kuma irin daular da suka shiga. Ba kasafai za kaga mutane suna da burin a dinga tunasu saboda gaskiyarsu, iliminsu, hikimarsu, riƙon amanarsu, irin sadaukarwar da suka yi kan al’ummarsu ko kuma yawan mutanen da suka taimaka a rayuwa ba. Wannan ce ta sa kusan kowa a cikin masu dama a hannunsu ya kalmashe hannnsa ya zuba wa matsalolin Arewa ido ha tare da nuna damuwa ba, duk kuwa da cewa yankunan Yarabawa da Inyamurai suna ta ƙara ci gaba a dalilin tsari da hoɓɓasa da wasu daga cikin manyansu suke yi musu.

Abin da al’ummar Arewa da kuma Najeriya gabaɗaya ta rasa shi ne yawaitar irinsu Ɗanmasanin Kano, Alhaji Yusuf Maitama Sule, wanda Allah Ya yi wa rasuwa a jiya bayan ya sha fama da rashin lafiya. Daga rasuwarsa jiya zuwa yau, mutane daban-daban sun tofa albarkacin bakinsu a kansa amma babu wanda na ji yace za a yi asararsa ko kuma za a dinga tunawa da shi saboda yawan dukiyarsa ko irin ƙarfin mulki da daular da ya shimfiɗa ba. Za a dinga tunashi ne da irin iliminsa, hikimarsa da kuma yadda ya yi amfani dasu wajen bai wa Najeriya gagarumar gudunmawa shekaru da dama bayan ya bar gwamnati. Duk da irin muƙaman da ya riƙe, amma ba wannan mafi yawan mutane suke kallo ba.

Darasin da zamu koya daga rayuwar Maitama Sule shi ne, duk abin da kake tunanin kuɗi ko mulki zasu baka, to ilimi da ilmantarwa zasu iya baka shi ciklin ruwan sanyi da mafificiyar daraja. Yau duk inda aka ce Ɗanmasani a faɗin duniya ba ma a Najeriya ba, ko ba a ƙara Kano ba, to kowa ya san Maitama Sule ake nufi. Dakta Yusuf Maitama Sule yana daga cikin mutanen da suka fi shahara a duniyarmu ta wannan lokaci.

Daga mutuwarsa a jiya zuwa yau, miliyoyin mutane ne, musamman matasa da basu ma san wani abu da yawa game da shi ba suke ta yabonsa. To amma tambayar a nan ita ce, muna so mu kwatanta zama kamarsa? Ko kuma mu ce, hakan zai ma yiwu kuwa a wannan zamani da kuɗi ya fi gaskiya, siyasa ta fi mutunci kuma burin tara abin duniya ya fi burin barin kyakkyawan baya?

Ɗanmasani mutum ɗaya ne tamkar da dubu. Yayin da ake masa kallon mai iya magana da hikima, akwai kuma abubuwa da yawa da mutane basu sani ba game da shi. Mutum ne mai matuƙar son zaman lafiya. Ya kan kashe maƙudan kuɗaɗe don ganin ya yi sulhu a tsakanin mutane. Idan ya ji ana rigima a kan kuɗi, ya kan fitar da kuɗinsa koda iya su kenan gareshi don ya kashe rigimar kamar yadda makusantansa suka tabbatar. Yana ɗiban maƙudan kuɗaɗe yasa  a kai wa maƙiyansa ko masu alaƙa dasu domin samar da zaman lafiya.

Ɗanmasani mutum ne mai matuƙar kishin al’ada. Akwai wani lokaci a shekarar 1998 ana buga gasar ƙwallon ƙafar cin kofin duniya a ƙasar Faransa, sai Ɗanmasani ya hangi wani mutum shi kaɗai a cikin tawagar magoya bayan Najeriya a cikin talabijin sanye da kayan saƙa na Fulani. Bayan an gama gasar, sai da yasa aka nemo masa shi ya ba shi kyautar Naira dubu ɗari biyar irin ta wancan lokaci.

Ɗanmasani shi ne Ministan man fetur na farko  a Najeriya kuma shi ne mafi daɗewa a kan wannan muƙami amma lokacin da aka yi juyin mulkin 1966 sai da ya ranci kuɗin mota  kafin ya dawo Kano shi da iyalansa daga Lagos. Da ya dawo Kano kuma ba shi da gida sai gidan gado ya koma. Bayan ya gama minista, bai yi girman kai ba, ya amsa roƙon Gwamnatin Kano na ya zo ya yi mata kwamishina tunda shi bauta wa jama’a ne a gabansa. A wannan zamanin, wa zai maka haka?

Watarana Sheikh Dahiru Usaman Bauchi ya yi mafarki ya ga  Ɗanmasani Kano a cikin waɗanda Manzon Allah (SAW) ya zaɓa a matsayin dakarunsa, sai ya taka ƙafa da ƙafa ya je ya sameshi. Ya bayyana masa mafarkin kuma ya tambayeshi, shi kuwa me yake yi haka na bauta ko shi ma ya yi koyi? Sai Ɗanmasani yace shi dai bai san wani abu na musamman da yake yi ba, amma yana da wata al’ada guda ɗaya. Al’adar kuwa ita ce bakinsa ba ya taɓa rabuwa da yi wa Annabi salati ko da kuwa kuna cikin hira da shi ne yana saurarenka kafin ya mayar maka da martani.

Yau mun wayi gari babu Ɗanmasanin Kano. Da wahala mu iya mayar da kamarsa a Kano, Arewa da Najeriya. Wataƙila idan mun yi da gasken-gaske mu samu waɗanda zasu ɗan kama ƙafarsa kaɗan. A ƙasarnan muna na mutane iri biyu; ‘yan kishin ƙasa da kuma ‘yan kishin yankinsu. Maitama Sule kuwa ɗan kishin ƙasa ne kuma ɗan kishin Arewa kuma ya haɗa duka biyun ne cikin ƙwarewa da gogewa. Lokacin da Shagari ya kayar da shi a zaɓen fidda gwanin takarar Shugaban ƙasa na NPN, har ‘yan Kudu sun yi jimami. An rawaito abokin hamayya Cif Awolowo na UPN yana cewar shi da Ɗanmasani NPN ta tsayar takara a maimakon Shagari, to da ko kotu ba zai je ba bayan an kayar da shi domin ya san Najeriya zata faɗa hannun nagartacce wanda dama shi ne burinsa.

Ɗanmasani yana daga cikin tsirarun manyan ƙasarnan da suka haƙura da siyasa suka zama dattawa tun da wuri. Tun bayan jamhuriya ta biyu bai ci gaba da matsawa kansa sai an dama da shi ko kuma dole sai ya samu wani mulki ba, sai dai a roƙeshi yazo ya taimaki gwamnati. To kuma sai ga shi waɗanda suka yi ta hanƙoran sai sun ci zamaninsu sun ci na wasu, basu kama ƙafarsa wajen ɗaukaka ba. Maitama Sule na kowa ne, ba ya shiga shirgin da babu ruwansa, kuma bai yarda an ji kansu da shugabanni ba duk da cewa kuma yana yi musu gyara idan sun yi kuskure da basu shawarwari.

Lokacin da watarana ya farka daga barci ya ga duhu, sai ya umarci matarsa ta kunna fitila. Sai ta ce ai fitilar   a kunne take, to a nan sai ya gane cewar Allah ya jarrabe shi da larurar makanta. Maimakon ya ruɗe ko ya kiɗime, sai ya tashi ya yi alwala yai sallar nafila ta musamman ya gode wa Allah. Ya ce, Allah na gode maka, wannan idon babu abin da bai gani ba na duniya kuma ko a yanzu da ka karɓe shi, babu wani abu da zai rageshi. Bai yi niyyar neman wani magani ba in banda masoyansa irinsu tsohon Shugaban ƙasa Janar Babangida da suka matasa masa lamba sai an je Turai, to amma Allah Ya riga ya yi ikonSa.

Tun daga ƙarshen shekarar 2016 zuwa yanzu ake ta yaɗa jita-jitar mutuwarsa, ashe lokacinsa ne ya matso. Allah Ya ji ƙan Ɗanmasanin Kano!

Twitter: @AmirAbdulazeez  

Sunday, December 11, 2016

Wane Irin So Muke Wa Manzon Allah (SAW)?

10 Ga Disamba, 2016

Daga: Amir Abdulazeez

A
llah (SWT) cikin hikimarSa da SahalewarSa Ya ƙara zagayo damu wata shekarar kuma mun riski watan Rabiul Awwal, wanda a cikinsa ne aka haifi fiyayyen halitta Annabi Muhammadu (SAW). Kusan kamar yadda ya kan kasance a mafi yawan shekaru, taƙaddama ta kan kaure a kan halaccin maulidi ko rashin halaccinsa, dacewa ko fa’idarsa da rashinsu. A cikin masu wannan taƙaddama kowanne yana da madogara ko hujjarsa da yake ganin ita ce karɓaɓɓiya. Abin farin cikin dai shi ne, kowanne ɓangare yana son Annabi Muhammadu, saɓanin kawai shi ne hanyar da za a bi wajen nuna soyayyar. To amma, duk ba ma wannan ba tukunna, tambayar da ya kamata mu tsaya mu yi kanmu a matsayin al’umma, ita ce wane irin so muke wa Manzon Allah kuma me aiyukanmu suke cewa game da son da muke cewa muna masa?

Wannan tambaya ta zamar mana kusan wajibi duba da yadda kullum son Annabi yake ƙaruwa a baki a cikin al’ummarmu, amma kuma kullum bijire wa koyarwarsa take ƙara hauhawa. Yanzunnan za ka ga an yi kare-jini-biri-jini da mutum a kan halacci ko rashin halaccin maulidi, amma anjima kaɗan in ka ba shi amana sai ya ci, in kai alƙawari da shi sai ya saɓa, in yai magana sai yai ƙarya. Ko kuma yanzu mutum zai ɗauki littafin Sahihul Bukhari ƙato ya tafi karatu, ya shafe awanni ana biya masa hadisan Manzon Allah, amma a kan hanyarsa ta dawowa zai fara cin naman mutane.

Kowacce shekara guraren yin maulidi ƙaruwa suke yi, guraren karatuttukan hadisan Manzon Allah ƙara yawa suke yi, masu waƙe ko bege na yabon manzo ƙaruwa suke yi, amma kuma kullum lalataciyyar mu’amala da munanan halaye irin waɗanda Manzon Allah ɗin ya hana sai ƙara samun gindin zama suke yi. Tambayar da ya kamata mu yi wa kanmu, wai shin son Manzo Allah ɗin ba shi da alaƙa da koyi da shi ne?

A wannan al’ummar da muke ciki, akwai waɗanda suke ikirarin sun yarda da alƙur’ani amma basu ma yadda da fassarar da Manzon Allah Ya yi wa alƙur’anin ba wato hadisai, kuma suna nan a tsakaninmu suna kiran kansu masoya Manzon Allah. Mutanen dai da ka ce sun yi ƙarya da suka rawaito hadisi, sune dai suka adana ƙur’anin har ya zo gareka; ko kuwa a gun Manzon Allah ka samu ƙur’anin kai tsaye? Mutumin da baka yarda da fassarar da ya yi wa alƙur’anin da aka saukar masa ba sai fassarar da ka yi wa kanka, shi ne kake ƙauna? Wacce irin ƙauna ce wannan? A wannan al’ummar ne, ake zagar wa Manzon Allah iyalansa, abokansa, shaƙiƙansa, amintattaunsa da masoyansa a filin Allah. Masu yin hakan suna nan a tsakaninmu kuma wai su ma masoyansa ne.

A wasu sassa a ƙasar Hausa, al’ada ta fi sunna daraja domin sai al’ada ta hana aure, sunna ba ta hana ba. Duk mu’amalar da ka ɗauka a wannan zamanin da muke ciki sai ka ga mafi yawancin yadda ake gudanar da ita ya saɓa da tsagwaron abin da Annabi ya koyar. Tun daga kan aure, kasuwanci, zamantakewa, mu’amala da sauransu. Ba wai ana nufin babu nagari ba ko babu masu koyi da Annabi a aikace ba; a’a, ana nufin gamayyar halayyar al’umma.

Wani babban kuskure da masu yawa daga cikin al’ummar Musulmi, musamman na ƙasar Hausa suke yi shine, na ɗauka da suke yi cewar son Allah da Manzonsa a baki shi ne kawai abin da ake buƙata, to amma akwai sauran abubuwa na aiki masu tarin yawa da matuƙar amfani, waɗanda rashin kiyayaesu zai iya kawo babbar alamar tambaya dangane da nagarta ko ingancin son da kake wa Allah ko manzonSa.

A abubuwan da Manzon Allah ya siffanta da su na kyawawan  halaye, kaɗan daga cikinmu ne suke ƙoƙarin kamantawa. A abubuwan da yake fushi da su, kaɗan daga cikinmu ne basu tsunduma tsamo-tsamo a cikinsu ba. Wannan shi ne halin da muke ciki.

Masana binciken halayya da ɗabi’un ɗan Adam sun yi ittifaƙin cewar ‘yan Najeriya musamman Hausawa suna daga cikin mutane da suka fi kowa nuna son Annabi a fili a Duniyar Musulunci, an yarda cewar Hausawan Arewacin Najeriya suna daga cikin waɗanda suke ƙoƙarin yin maulidi da hidindimu. To amma kuma sai dai kash! Idan da za a auna, da sai a gano cewar miyagun halaye da gurɓataciyyar mu’amala ta yi mana katutu. Wannan ƙalubale ne ba ƙarami ba a kanmu domin kuwa duk wanda yake ikirarin abu, to alamun wannan abun gaskiya ne, shi ne a gan shi a aikace.

Gurɓacewar mu’amalarmu da yanayin zamantakewarmu a yanzu ta kai ta kawo muna zaune cikin rashin ‘yan uwantaka. Idan jifa ya wuce kanka, to ya faɗa kan kowa. Ba ka gudun ka yi wa mutane abin da kai baka so a yi maka. Muna zaune kullum neman juna muke da sharri ba alkhairi ba. Kowa so yake kowa ya aikata kuskure ya yi ta faman yamaɗiɗi, amma idan an yi alkhairi sai ka ji gum. Kowa tsoron yin harkar kuɗi yake yi da  kowa. Wannan masifa har ina? Koyi da Manzon Allah a haƙiƙance ba a baki ba, shi zai yi mana maganin wannan.

A cikin jama’a, idan ana zaune, har ƙagara ake yi mutum ɗaya ya tashi a saka faifansa, a fara zaginsa ana cin namansa. Ƙarya kuwa ta zama ita ce mafi akasarin zancenmu. Duk maganar da aka faɗa, kowa zai karɓe ta ne cikin shakku da zargi. Idan an faɗa maka farashin abu a kasuwa, gani kake cutarka za a yi. Babu aminci a tsakaninmu. Cin amana a kasuwanci, zamantakewa, aiki, maƙotaka, abota, duk ba wani baƙon abu ba ne a cikin mu’amalar mutanen wannan zamani.

Da ka taɓa mutane, sai su ce sun fi kowa son Annabi, amma kuma a halayyarsu babu irin ta Annabin. Annabi Muhammad (SAW) shi ne mutumin da ya fi kowa iya mu’amala a tarihin duniya, kuma shi Musulmi ne, da shi aka ce Musulmi su yi koyi. Ina koyin yake?

Idan muna buƙatar son da muke yi wa Annabi ya zamo abin gaskatawa da amfanarwa, to sai mun gyara zuciyoyinmu, addininmu, halayenmu da zamantakewarmu ta hanyar yin koyi da dukkan halayensa da kuma ƙauracewa abubuwan da ya hana. Idan ba haka ba, yawan maulidinmu ko sauraron wa’azinmu ba zai kaimu ko’ina ba. Allah ya bamu ikon gyarawa.

Shafin Mallam Amir a Twitter shi ne: @AmirAbdulazeez  

Wednesday, October 12, 2016

Siyasar Bambaɗanci da Makomar Matasanmu

06 Ga Oktoba, 2016

 Daga: Amir Abdulazeez

C
ewar babu abinda ɗan siyasar wannan zamani ba zai iya yi ba saboda buƙatarsa, kullum ƙara bayyana yake yi a fili ƙarara. Ba wai sata, ƙarya, munafirci, rashin kunya ko maguɗi ba, a’a da yawa daga cikin ‘yan siyasarmu na wannan lokaci, a shirye suke su lalata rayuwar ‘ya’yan da ba nasu ba wajen ganin sun samu biyan buƙata ko kuma an ci gaba da kare musu muradinsu ko ta wane hali kuma komai lalacewar hanyar da za a bi wajen kare musu muradan nasu.

Duk mai lura da yadda al’amuran yau da kullum suke gudana, zai fahimci cewa an samar da wani sabon salo na wofantar da matasa da mayar dasu mabarata ko maroƙan ƙarfi-da-yaji. Irin waɗannan matasa suna shiga gidajen rediyo da sauran kafafen yaɗa labarai, amma dandazonsu ya fi yawa a shafukan sada zumunta na yanar gizo; shafukan da suka haɗa da Facebook, Twitter da dai sauransu. Irin waɗannan matasa basu da aiki sai tumasanci da bambaɗanci ga ‘yan siyasa da masu mulki. Irin wannan salo na tumasanci, kusan bamu taɓa ganin irinsa a ƙasar Huasa ba; ko maroƙanmu irin na da waɗanda basu da sana’a sai roƙo basu yi irin abinda ake sa waɗannan matasa suke yi a yanzu ba.

Rahotanni masu tushe sun bayyana cewar ‘yan siyasa a jihohin Arewacin Najeriya har ma da kudancin, yanzu sun ɗauki ɗabi’ar saya wa matasa wayoyi ko komfutoci da basu kuɗi lokaci bayan lokaci domin sanya kati domin su dinga shiga yanar gizo suna yi musu bambaɗanci da tumasanci wai da sunan tallatasu ko yabonsu. A cikin irin matasan da aka ɗora a kan wannan wulaƙantacciyar hanya, babu ‘ya’ya ko jikokin su ‘yan siyasar ko masu mulkin. Abin takaici ne matuƙa a ce wai a wannan ƙarni na 21 da kowa yake ƙoƙarin bai wa matasa ilimi da damammakin da zasu zama masu juya duniyar gobe, wasu mutane ko jagorori waɗanda ya kamata su shige musu gaba don tabbatar da hakan, sun koma ɗorasu a kan tafarkin roƙo, kwaɗayi, cin mutunci da wofantar da kai wai da sunan siyasa. Wani abin haushin kuma shine, su ‘yan siyasar masu yin wannan, ba haka magabatansu suka yi musu ba; hasalima, ba dan magabatan nasu sun ɗorasu a kan hanya mai kyau ba, da basu zama abinda suka zama ba a yanzu.

Akwai matasan da  a yanzu dare da rana, basu da aiki sai shiga kafafen sada zumunta suna zubar wa da kansu da gidajensu mutunci wai da sunan tallata masu mulki. Wanda kuma ba ya yin haka kuma ya zaɓi ya kare mutuncinsa, to kallonsa ake yi a matsayin maƙiyi ko ɗan adawa. Kullum kwanan duniya, in dai kana raye a Najeriya, zaka yi ta ganin abubuwa na rashin hangen nesa da sanin ya kamata iri-iri. Wani abin tun kana gane dalilin yinsa har sai kanka ya ɗaure ka koma baka fahimtarsa kwata-kwata. Mun koma, bama son dai-dai kuma bama son gaskiya; wanda ya yi gaskiya ko ya dage sai an yi dai-dai sai a mayar da shi mujiya a cikin tsuntsaye. Haka zamu ci gaba? Muna buƙatar gyara kuwa?

Farko dai dole ne waɗannan ‘yan siyasa su dubi Allah su tuna haƙƙin da yake rataye a wuyansu. A matasyinsu na shugabanni, ci gaban matasannan da dukkan al’umma gabaɗaya ya rataya a wuyoyinsu. Duk lalcewa, in bazasu iya taimakonsu wajen ci gaban rayuwarsu da dogaro da kansu ba, bai kamata su ɗorasu a hanya ta mutuwar zuciya ba. Ya kamata su tsaya tsayin daka su yi aiki tuƙuru wajen kyautatawa al’umma; idan suka yi haka, ba sai sun ɗebi kuɗin jama’a sun biya matasa su yi musu bambaɗanci ba, mutane zasu yaba musu dai-dai gwargwado. Su tuna fa cewar in da a irin wannan tafarki magbatansu suka ɗorasu, to fa da basu zama abinda suka zama ba kenan. Kuma, me zai hana su sanya ‘ya’yansu da jikokinsu su dinga yi musu irin wannan aiki a maimakon ‘ya’yan wasu?

Ya kamata ‘yan siyasa su daina amfani da damar talauci da kuma tsabar kwaɗayi da yake addabar wasu daga cikin jama’ar wannan zamani wajen  mayar da mutane maroƙa wulaƙantattu. Idan kuma ba da amincewa ko saninsu ake waɗannan abubuwa ba, to su taka wa abin burki. Su daina gudun masu faɗa musu gaskiya da basu shawara domin kawo gyara kuma su daina buɗe ƙofa ga ‘yan tumasnci da bambaɗanci.

Matasanmu kuma dole ne fa sai mun yi wa kanmu faɗa mun fahimci manufarmu a rayuwa. Talauci da neman abin duniya ba fa hauka bane; kowa yana son kuɗi amma ba ta kowacce hanya ya kamata a nemesu ba kuma samun kuɗi cikin sauƙi ba shine burgewa ba. Duk mutumin da zai dinga baka ‘yan kuɗaɗe ƙalilan domin ka dinga yabonsa a kafafen sada zumunta, to ba mai ƙaunarka bane. Idan da abin kirki ne ko na ci gaba, to ba kai zai nema ba, ɗansa ko jikansa ko ƙaninsa zai kirawo ba kai ba; ai muna gani sarai ba sai an bamu labari ba. Matasa su fahimci cewar basu da wata martaba a idon ‘yan siyasa ko amfanin da ya wuce irin wannan aiki da ake sakasu kuma da zarar ka gama aikinka, shikenan amfaninka ya wuce.

Tilas ne matasa su fahimci cewar, mai ƙaunar ka ko mai son ɗorewar mutuncinka da ƙimarka ba zai dinga biyanka kuɗaɗe ƙalilan kana zagin wani ko cin mutuncinsa ko kuma shiga wata hanya ta mutuwar zuciya ba. Mu tuna fa mafi yawan waɗannan ‘yan siyasar fa ba finmu suka yi ba, dama ce kawai suka samu, kuma idan da rabo kai ma zaka iya zama kamarsu ko ma ka fisu. Maimakon ka zauna kana yi musu bambaɗanci, mai zai hana ka yi ƙoƙarin zama kamarsu?

Matasanmu su gane cewar babu lokaci mafi amfani a garesu kamar lokacin ƙuruciya ko tashensu; lokaci ne da zasu yi amfani da shi wajen gina kansu da shirya wa ƙalubalen rayuwa, ba wai lokacin da zasu ɓata wajen karewa ko yabon wasu can da ba ci gabansu bane a gabansu. Wannan hanya ba mai ɓullewa bace; idan kunne ya ji, jiki ya tsira!

Twitter: @AmirAbdulazeez