Fassara

Wednesday, March 23, 2016

Kwankwaso, Ganduje da Siyasar Aika-Aika

18 Ga Maris, 2016


Daga: Amir Abdulazeez

B
abu wanda wannan rikicin siyasar tsakanin Kwankwaso da Ganduje za ta bai wa mamaki sai wanda ba ya bibiyar al’amuran siyasar Jihar Kano da Najeriya ko kuma a’a yana bibiya amma ba ya fahimtar yadda abubuwa suke tafiya. Don haka ba rigimar ce yanzu abin mamaki ba, fara ta da aka yi da sanyin safiya kafin tafiya ta yi nisa shine abin mamaki. Kodayake akwai waɗanda suka so ma ayi wannan rigima tuntuni ma kafin wannan lokaci, to amma masu hasasshe sun tabbatar wa da irin waɗancan mutane masu azarɓaɓi tun a lokacin da gwamna Ganduje ya cika kwanaki 100 a kan mulki cewar rigima fa za a yi ta, sai dai jiran lokaci. Ba wai abubuwan da suka faru a zuwan Kwankwaso ‘ta’aziyya’ ne ya tada rigimar ba, sune dai suka munanata.

Bari mu manta da batun wanene da gaskiya ko kuma wanene ba shi da gaskiya a cikin wannan al’amari, mu manta da waye ya yi butulci ko waye bai yi ba. Kai mu ma manta  da batun wanene zai yi nasara, wanene kuma zai sha kashi. Mu tambayi kanmu da su waɗannan shugabanni biyu masu rigima, shin wannan rikici shi ya kamaci kowannensu a dai-dai wannan lokaci kuma menene sakamakonsa?

Bari mu fara da Gwamna Ganduje. Maigirma gwamna yana da manya-manyan maƙiya guda uku a yanzu kuma duka a cikinsu babu Kwankwaso. Sahun gaba a cikin maƙiyan Ganduje sune masu kiran kansu magoya bayansa waɗanda suka fara yi masa kamfen ɗin tazarce a 2019 tun ma kafin ya cika kwanaki 100 a kan mulki. Wasu daga cikin irin waɗannan ‘magoya baya’ basu ma san da Ganduje ba sai bayan ya samu takara, wasu ma sai bayan ya ci gwamna, amma bambaɗanci da bani-na-iya tasa su suka fi kowa fada yanzu a gurinsa. Duk wani magoyin bayan gwamna na gaskiya ba wai na son zuciya ko rinto ba, kamata yayi ya mayar da hankali wajen taimaka masa da faɗar gaskiya komai ɗacinta, shawarwari da addu’a domin ya sauke nauyin da yake kansa kuma ya samu ya gama zangonsa na farko lafiya cikin nasara ba tare da an samu aika-aika ba.

Maƙiyin Ganduje na biyu shine faɗuwar farashin ɗanyen man fetur wanda ya haddasa masifar ƙarancin rashin kuɗin shigar da shi da takwarorinsa gwamnoni suke ciki. Bayan haka, yunƙurinsa na rage kaifin wannan matsala ta hanyar zafafawa a kan karɓar haraji, ya kawo wa gwamnatinsa baƙin jini da rashin fahimta a gurin mutanen Kano. Ko an ƙi ko an so, wannan za ta dakushe ƙoƙarin gwamnatinsa na ganin ta yi abin kirki. Wannan matsala ita kaɗai ta isa ta hanashi ya wanye da mutanen Kano lafiya wanda tun a yanzu da yawa daga cikinsu sun fara yi masa laƙabi da mai zango ɗaya kuma suke kallonsa a matsayin mai rauni wanda ba zai iya mulkin ba ma.

Matsalar Ganduje ta uku ita ce ƙunshin  da tsarin gwamnatinsa. Kwata-kwata yanayin ƙunshin gwamnatinsa bai nuna cewar so ake yi a cimma wani abu na a-zo-a-gani ba. Mafi yawan naɗe-naɗensa sun fi maida hankali ga biyan bashi ga waɗanda suka wahaltawa kamfen ɗinsa da kuma waɗanda zasu taimakeshi ya yaƙi Kwankwaso ko kuma ‘yan bambaɗanci. Banda haka, fama da rashin kuɗin shiga bai hana gwamnatin yin naɗe-naɗe barkatai marasa kan gado ba. Bugu da ƙari, bayan watanni 10, har yau gwamnatin bata nuna alamun tana da wata alƙiblar da tasa a gaba ba; waɗanne abubuwa ne zata fi mayar da hankali  a kansu; noma, kiwon lafiya ko me? Idan Ganduje ya tsaya faɗa da Kwankwaso ba tare da ya yi maganin waɗannan maƙiya nasa ba, to lallai a ƙarshe za a samu aika-aika.

Bari mu dawo kan Kwankwaso. A yanzu Sanatan Kano ta tsakiya, babu abin da ya kamata mu yi masa sai jaje kuma mu ji tausayinsa saboda dalilai da yawa, amma ga kaɗan daga cikinsu. Na farko dai, Kwankwaso yana girma amma lamurransa suna ƙara lalacewa. A matsayinsa na wanda yake tunkarar shekaru 60 da haihuwa a duniya, ya kamata a ce ya haƙura da mugunyar aƙidarsa ta ba-zai-bi-ba, sai dai a-bi-shi. Kullum gani yake shine mai sawa da hanawa kuma a haka zai dauwama. Tunaninsa, shi ya kafa kowa, ya kuma manta cewar shima kafa shi aka yi. Taƙamarsa shi babbane kuma jagora, amma abubuwan da yake yi wani sa’in, masu baki da kunu da ‘yan aika-aika ma baza su yi ba.

Abu na biyu da ya kamata  a yi wa Kwankwaso jaje a kansa shine tsananin matsawa kansa da yayi sai ya zama Shugaban ƙasar Najeriya. Ba wai muradin zama shugaban ƙasar ne laifi ba, yadda yake ƙaddamar da muradin nasa ne matsala. Duk wanda baya goyon bayan takararsa, to ganinsa yake kamar maƙiyinsa ne, me yiwuwa shi a ganinsa ƙila dole ne kowa ya goyi bayansa sai kace kowa bawansa ne. Ya manta dimokraɗiyya ake yi ba wai aika-aika ba.

Abin jaje na uku ga Kwankwaso shine duk da farfaganda, surutai dan nuna yafi kowa iyawa da yayi ta yi  a lokacin mulkinsa, sai gashi gwamnatinsa ta ƙare da zarge-zarge da kuma yawan bashi da ba a taɓa jin irinsa ba a tarihin Kano. Har yanzu Sanata Kwankwaso ko magoya bayansa sun kasa yi wa jama’ar Kano cikakke kuma gamsasshen bayani a kan zarge-zargen da ake yi masa na wawashe kuɗaɗen ƙanannan hukumomin Kano da rana tsaka tare da yin kamfen ɗin takararsa ta shugaban ƙasa dasu. Daga an tayar da wannan magana sai magoya bayansa su fara yi wa jama’a labarin irin aiyukan da ya shimfiɗa, sai kace yin aiki wani lasisi ne da mutum kuma zai ɗebi kuɗin jama’a. Idan da nine Kwankwaso, zan mayar da hankali ne wajen wanke kaina daga waɗannan zarge-zarge domin karsu zamarmin tangarɗa a 2019, a maimakon yunƙurin nuna wa Ganduje cewar bai isa ba, nine isasshe.  Kai ko ba don 2019 ba, zan yi hakane don gudun kada waɗannan zarge-zarge su lalata min tarin aiyukan alkhairin dana yi a mulkina kuma ta yadda ba zan bari sunana ya shiga cikin tarihin waɗanda ake zargi da yin aika-aika da kuɗin Kano ba. Sannan kuma ba zan ci gaba da kallon Kano kaɗai kamar ita ce zata bani shugaban ƙasa ba, Najeriyar zan dinga kalla gabaɗaya.

A ƙarshe, akwai shawarwari, duk da dai cewar faɗa ko rikicin siyasa irin wannan ba a cika samun wani sulhu mai ma’ana a cikinsa ba, amma dai kowa akwai hanyar da zai bi don kada ya zamo abin dariya a gurin mutane. A mayar da makamai na zahiri, a ci gaba da yin faɗan ta-ciki-na ciki a baɗini.

Ya kamata Gwamna Ganduje yayi amfani da tarin ƙwarewarsa da hangen nesansa da kuma haƙurinnan da aka sanshi da shi wajen taka-tsantsan a wannan rigima. Ko ba komai, shi ne wanda nauyin jama’ar Kano yake kansa ba wai Kwankwaso ba, ya dubi illar da rigimar za ta iya yi wa wannan nauyi da yake kansa. Sannan kuma gwamna mai ci yanzu, ya tuna cewar fa ya bamu labari a baya cewar duk nasarorin da tsohon maigidansa ya samu, tare suka samu; mai zai hana ya rungumi aika-aikar da suka yi tare?

Kwankwaso! Kwankwaso! Kwankwaso! Sau nawa na kira ka? Lokacinka ya wuce, ka gode wa Allah; kaf  a tarihin siyasar Kano babu wanda ya kai ka sa’a da samun ni’imomi. Ganduje ko Buhari duk baza su hana ka zama shugaban ƙasa ba, idan Allah Ya so, faɗa ko rashin faɗanka dasu ba zai sa ko ya hana komai ba. To wai me neman Shugaban ƙasa ma, ina shi ina wani faɗa? Ganduje kuma, ba kai zaka cireshi ba, ka barshi da mutanen Kano domin su suka ɗaukeshi aiki. Idan ka ci gaba da faɗa da shi, akwai fa tarin aika-aikar da zai iya bankaɗowa wacce mai yiwuwa ba zaka so jinta ba, kai shima baza ta yi masa kyau ba. Idan kuma kana ganin ka yarda da kanka kuma zaka iya kare kanka, to ga fili ga mai doki.

‘Yan uwana talakawa, wannan rigima ce ta ‘yan siyasa, kada mu yarda su raba mana kawuna ko kuma magoya bayansu su raina mana hankali, duk maganace ta buƙatar kai da son zuciya, ba don mu ake yi ba. Irin haka ta faru ba sau ɗaya ba sau biyu ba, ya kamata mu ɗauki darasi, idan kuma mun ƙi, to zamu ga aika-aika.


Twitter: @AmirAbdulazeez   

Friday, February 12, 2016

Ta Yaya Zamu Farfaɗo da Darajar Naira?

12 Ga Fabrairu, 2016.




T
un bayan gama Yaƙin Duniya na Biyu a shekarar 1945 tare da bayyanar ƙasashen Amurka da Rasha a matsayin mafi ƙarfin-faɗa-a-ji a duniya, Dalar Amurka ta fara kuma take ci gaba da gauraye duniya. Lokacin kuwa da yaƙin cacar baki wanda aka fi sani da Cold War tsakanin ƙasashen Rasha da Amurkar ya zo ƙarshe a shekarar 1991 tare da bayyanar ƙasar Amurka a matsayin ƙasa ɗaya tilo mafi ƙarfi a duniya, tuni Dalar Amurka ta game ko’ina a faɗin duniya; ta zama takardar kuɗi ta ƙasa da ƙasa, sannan kuma ma’aunin darajar sauran kuɗaɗen ƙasashen duniya. Kodayake takardar kuɗi ta Euro wanda ake amfani da ita a Nahiyar Turai da Pound Serling to Ingila sun fi ta daraja ta fuskar tsada, amma basu ko kama ƙafar ta ba wajen hada-hada da karɓuwa ba.

Ɗaya daga cikin matakan da gwamnatin Shugaba Yakubu Gowon ta ɗauka tun bayan kammala yaƙin basasa shine na ƙirƙiro da takardar kuɗi ta Naira a shekarar 1973. Kafin wannan lokacin, Najeriya tana amfani ne da takardar Pound Sterling ta Africa ta Yamma wacce take da kwatankwacin daraja ɗaya da Pound Sterling ta Birtaniya a wancan lokaci, kusan ma babu wani bambanci tsakaninsu. Ita kanta Nairar da aka ƙirƙiro daga baya, kusan darajar su ɗaya da Pound Sterling ta birtaniya, har akwai lokutan ma da ta ɗara ta a daraja a lokutan da aka fuskanci tsadar ɗanyen man fetur wanda Najeriya take kan ganiyar haƙowa a wancan lokaci. A tsakanin shekarun 1978 zuwa 1982, akwai lokacin da sai mutum ya bayar da Dalar Amurka biyu sannan za a bashi Naira ɗaya; ma’ana, Naira ta ninka Dala a daraja a wancan lokaci.

Duk da zargin karya tattalin arziƙi da sojoji suka yi wa gwamnatin Shugaba Shehu Shagari, amma har ya bar mulki ana canza kowacce Dalar Amurka ɗaya a kan tsakanin Naira ɗaya zuwa ƙasa da haka. Lokacin da Janar Babangida ya yi wa Janar Buhari juyin mulki, ana canzar kowacce Dalar Amurka ɗaya a kan Naira ɗaya zuwa biyu. A lokacin Babangida ne, Najeriya ta rungumi tsarin gudanar da tattalin arziƙi na Hukumar Bayar da Lamunin Kuɗi ta Duniya (IMF) tare kuma da karɓar maƙudan kuɗaɗe a matsayin rance daga wannan hukuma. Wannan tsari da Babangida ya kawo wanda aka fi sani da SAP, tsarin da tun da farko ya kasa samun shiga a gurin gwamnatin Janar Buhari, shi masana da dama suke ganin ya jefa Najeriya a cikin mawuyacin halin tattalin arziƙin da har yanzu bata farfaɗo ba. Bayan ‘yan wasu lokuta da kankamar tsarin SAP, a shekarar 1991, Dalar Amurka ɗaya sai ta koma Naira goma. Lokacin da Babangida ya tafi a 1993, tuni Dalar Amurka guda ɗaya ta koma tsakanin N22 zuwa N57, ya danganta da alƙaluman gwamnati ko na ‘yan canji. Dalar Amurka ta dinga hawa ba ƙaƙƙautawa a hannun gwamnati da ‘yan canji tun daga lokacin Shugaba Abdussalmi har zuwa lokacin Mulkin Shugaba Jonathan inda ta zama N86, N100, N140 har sama da haka. A yau Dalar Amurka ɗaya a hukumance, ana canzar ta ne a kan N197,  a hannun ‘yan kasuwa kuwa tana kaiwa N310 zuwa N315. Babu wata lalacewa ko taɓarɓarewa da za a iya kwatantata da wannan.

Kafin a san magani, ya kamata a fahimci cuta tukunna. Duk da cewar mafi yawan ‘yan Najeriya suna ɗora alhakin faɗuwar darajar Naira da taɓarɓarewar tattalin arziƙi a kan tsarin SAP na turawan yamma da Shugaba Babangida da Ministan harkokin kuɗinsa na wancan lokacin, Cif Olu Falae, to amma ya kamata mu kalli wasu dalilan da dama bayan wannan. Tun daga shekarar 1973 zuwa 2016, kowanne ɗan ƙasa ya bada gudunmawarsa wajen lalacewar darajar Naira. Akwai laifin gwamnati, shugabanni, ‘yan siyasa, ‘yan kasuwa, ma’aikata da kuma talakawa.

Tun farko dai ƙasashen Afrika ciki har da Najeriya da kuma sauran dukkan ƙasashe masu tasowa sun tafka babban kuskure wajen tunanin cewar ƙasashen Turawa masu ƙarfin tattalin arziƙi zasu ji tausayinsu ko kuma zasu kawo wani tsari wanda zai taimakesu tsakani da Allah ba tare da wani kitso da kwarkwata ba. Kullum hasashen irin waɗancan ƙasashe shine ya za a yi mu dauwama a ƙasa, su suna sama, to ta yaya zasu bamu wani taimako nagari? Ci gaba da taɓarɓarewarmu, ita ce ci gaba da bunƙasarsu; idan muka zama iyayen gidan kanmu, wa zasu mulka balle har su yi masa fankama? Kullum burinsu su dinga tsakuro tallafi suna bamu kamar almajirai ko kuma su bamu rancen maƙudan kuɗuɗe domin mayar damu bayin ƙarfi da yaji. Ƙasashe irinsu China, India da Brazil da suka farga tun da wuri suka yi watsi da dogaro a kan Turawa, yau sun tsaya kai da fata sun ciyar da kansu gaba, kuma sun fita daga ƙangin bauta. A yau ƙananan ƙasashe da dama sun haramtawa kansu amfani da kayayyakin Turawan Yamma domin bunƙasa nasu na gida Dole ne Najeriya ta kama hanyar bin sahun waɗannan ƙasashe koda kuwa a faro zamu sha baƙar wahala kafin mu murmure.

Tsawon shekaru da yawa, Gwamnatin Najeriya a ƙarƙashin shugabanni daban-daban sun ƙyale ƙasar ta dogara da ɗanyen man fetur ba tare da ta maida hankali  a kan noma, kiwo da bunƙasa masana’antu ba. Wannan ta jawo, babu wata muhimmiyar hanya da kuɗaɗen ƙasar waje suke shigo mana sai ta hanyar ɗanyen man fetur, kuma gashi tataccen fetur ɗin sai mun fita wata uwa duniya mun sayo shi tunda mun bar namu matatun a lalace, hakan ya kawo faɗuwar darajar Naira, musamman a yanzu da farashin ɗanyen man ya faɗi wanwar  a kasuwar duniya. Bayan haka kuma, gwamnatoci da yawa da suka shuɗe basu tashi tsaye sun ɗauki takardar Nairar ita kanta da muhimmanci ba balle su kare ta. Ana zargin da yawa daga cikin shugabannin Najeriya da ‘yan siyasarta da wawushe kuɗin ƙasa, kuma abin takaici, maimakon su ajiye su a Najeriya ko kuma su zuba hannun jarin a Najeriya, a’a sai su ɗebi kuɗin su ajiye su a ƙasashen waje. Daga 1999 zuwa 2015, Allah ne kaɗai ya san iya dukiyar da ɓarayi daga cikin shugabannin Najeriya, ma’aikata da ‘yan siyasa suka sata suka kai ƙasar waje, wannan ya taimaka wajen karya tattalin arziƙin ƙasa da kuma karya darajar Naira.

Sana’ar canji, wacce kwata-kwata da ba a san da ita ba a Najeriya sai daga baya ta taka rawa wajen lalata darajar Naira duk da cewar kuma ta taimaka wajen sauƙaƙa samun kuɗaɗen ƙasashen waje tare kuma da samar da sana’a ga mutane da dama. Babbar matsalar ita ce, su ‘yan canji riba ce zalla kuma tsababa kawai a gabansu ba wai makomar darajar Naira ko kishin ƙasa ba. Wannan ce ta kawo lalacewar sana’ar canji kuma a maimakon ta zamo mataimakiya wajen kare martabar Naira, zai ta zamo wata hanyar da ake amfani da ita wajen kassara Nairar tare da ɗaukaka darajar kuɗaɗen ƙasashen waje domin kawai a ci riba. Bayan haka kuma, wasu mutane suna yin amfani da harkar canji ko kuma ‘yan canjin wajen karɓo kuɗaɗen ƙasashen waje a hannun gwamnati kuma su ɓoyesu ko kuma su yi amfani dasu ta hanyoyin da zasu cutar da tattalin arziƙin ƙasa. Dole sai an tsaftace tare da yin garanbawul ga wannan sana’a idan har ana so a samu farfaɗowar darajar Naira.

Mafi yawan ‘yan kasuwarmu, kullum tunaninsu shine su fita ƙasar waje su sayo kaya, a maimakon su maida hankali wajen samar da fasahar ƙera kayan a nan gida Najeriya da kansu. Kusan kowa yafi son daga-buhu-sai-tukunya, kawai ya sayo kaya ya sayar ya ci riba a karan kansa, koda ƙasar za ta mutu. Bugu da ƙari kuma, mafi yawan ‘yan kasuwar basa biyan haraji balle gwamnati ta ɗan ƙaru da wani abu. Wannan tasa mun wayi gari kusan komai da muke amfani da shi, shigo dashi ake daga ƙasar waje, hatta tsinken sakace. Mu kusan babu mai shigowa ya sayi namu kayan, amma kullum muna kan hanya wajen sayo kayan wasu; wannan ta taimaka wajen faɗuwar darajar Naira. Mafi yawan ‘yan Najeriya babu kishin ƙasa a gabansu, kowa burinsa kawai ya gamsar da kansa ko ya biya buƙatarsa, babu ruwansa da makomar ƙasa. Wannan ita tasa mafi yawancin mutane, burinsu su sayi kayayyakin ƙasashen waje,  a dalilin haka ne ma kayayyakin da aka sana’anta a Najeriya suke yin kwantai kuma waɗanda suke yinsu suke watsarwa suna koma sayo na ƙasar waje. Kullum tunaninmu wai kayan ƙasar waje yafi kyau, to ta yaya namun zai yi kyau, idan bama saya? Munata rage wa kanmu ƙarfi muna ƙarawa masu ƙarfi ƙarfi; wannan ta kawo faɗuwar darajar Naira.

Idan da barci muke , to ya kamata yanzu mu farka. Takardar kuɗin ƙasa wata aba ce mai martaba da ƙima wacce take nuna irin darajar tattalin arziƙi da kuma darajar ƙasar ita kanta. Yanzu Naira ta hau kan wata turbar taɓarɓarewar da ba a taɓa gani ba kuma idan muka zuba ido cewar gwamnati ce kaɗai za ta gyara ta, to kuwa zamu sha mamaki. Idan muka yi wasa sai mun wayi gari Naira ta koma bata da amfanin komai sai zubarwa. Duk da cewar wannan matasala ta kwararo a cikin shekaru sama da 40 baya, amma idan muka haɗu a kan manufar kawo gyara, to Naira zata farfaɗo ko da kuwa ba yanzu yanzu ba.

Tun da farko dai dole gwamnati ta maida hankali a kan harkar noma tare da samar da isasshiyar wutar lantarkin da  zata bai wa masana’antu dama domin su farfaɗo su dinga aiki ka’in da na’in. Banda haka, dole ne a tsaurara matakan ladabtarwa a kan masu satar dukiyar ƙasa suna zuba hannun jari  a ƙasashen waje. Dole ne gwamnati ta zage damtse wajen dawo da dukkan kuɗaɗen Najeriya da aka sace daga ƙasashen waje. Kodayake Turawan yamma da sauran wasu ƙasashe baza su so a janye wannan ɗimbin dukiya wadda take ƙarawa tattalin arziƙinsu ƙarfi ba, amma wannnan ya zama dole in har muna so mu cigaba. Bayan haka, idan gwamnati tana so ‘yan Najeriya su sayi kayayyakin da aka ƙera acikin ƙasar, to sai ta zamo abin koyi. Dukkan abin da zata saya, ita ma ta dinga sayen na cikin gida kuma ta rage bai wa kamfanunuwan ƙasashen waje kwangila sai ya zama dole. Bayan haka ta duba yiwuwar kafa dokar hana shigo da rukunin wasu kayayyakin da za a iya ƙerawa a nan gida ko kuma ta sanya haraji mai tsanani  a kansu.

Dolene ‘yan siyasarmu, musamman na 1999 zuwa 2015 su karɓi alhakin ɗaiɗaita mana tattalin arziƙi da jefamu a cikin mawuyacin halin da muke ciki da suka yi. Wajibine a kawo ƙarshen siyasar kuɗi domin guje wa ɓarnatar da dukiyar ƙasa. Yanzu ‘yan siyasarmu saboda tsananin rashin kishin ƙasa, idan zaɓe ya matso, duk wata Dalar Amurka da manyan kuɗaɗen ƙasashen waje dake cikin Najeriya sai sun sayesu domin su saya ko su ƙwaci zaɓe, saboda suna so su dauwama a kan mulki, alabashi ita kuma ƙasa taje can ta shiga halin da zata shiga babu ruwansu. Naira ta yi musu rashin daraja da yawa, don haka Daloli suke rarrabawa domin su ba sai an yi kayansu ba niƙi-niƙi. Dalolin da ya kamata a sayar wa da ‘yan kasuwa domin su saro kaya, ‘yan siyasa da masu mulki duk sun sayesu; wacce take hannun gwamnatinma kuma sun yi amfani da alfarmarsu sun saye, a wasu lokutanma sun sace su kai tsaye. Ta yaya Naira ba zata lalace ba?

Wajibi ne ‘yan kasuwar mu su haɗu a kan yadda zasu dinga ƙera kaya da kansu a maimakon sayosu daga ƙasashen waje. Babu shakka, wannan wani abu ne mai wahala, amma idan suka sa kansu zasu iya, kuma a kwana a tashi, zasu saba har su zama ƙwararru. Yanzu ga Aliko Dangote nan, ai bai zama mai kuɗin Africa baki ɗaya ta hanyar shigo da simiti ba, ya zama ne ta hanyar sana’antashi ya fitar zuwa wasu ƙasashe ko kuma a biyoshi har inda yake a saya. Mu kuma talakawa da mafi yawan masifa take ƙarewa a kanmu, mu yafi kamata ma mu tashi tsaye. Kowa ya yi duba na tsanaki a kan kansa ya ga shin yana sayen kayan da aka ƙera a Najeriya?  Idan akwai abin da ake ƙerawa a Najeriya, to ka ƙyale na ƙasar waje. Idan kana ganin na ƙasar wajen yafi na gida kyau, to sayensa da kake yi ne yasa yafi na gidan kyau, idan ka koma sayen naka, shima zai yi ingancin da watarana zai fi na ƙasar wajen.

Wednesday, January 6, 2016

Shekaru 50 Bayan Sardauna: Ko Mazan Yau Zasu Yi Kamar na Jiya?

4 Ga Janairu, 2016



S
hekaru hamsin bayan juyin mulki na farko a Najeriya wanda ya yi sanadiyyar kashe Sir Ahmadu Bello, Sardaunan Sokoto da Sir Abubakar Tafawa-Balewa, har yanzu waɗannan mutane sune abin misali a Arewa, Najeriya da ma wasu sassan Afrika baki ɗaya. Shekaru hamsin da kwanta damarsu, har yanzu kusan an kasa cike giɓin da suka tafi suka bari, musamman ma ta ɓangaren Sardauna. Dama-dama ma Tafawa-Balewa, an samu wasu gwarazan shugabannin a matakin ƙasa, irinsu Marigayi Murtala Ramat Muhammad da suka kwatanta yin jagoranci bisa jajircewa da adalci kamar irin nasa, amma har yanzu Arewacin Najeriya ta kasa samun wani shugaba kamar Sardauna.

Shin nagartar Sardauna ce ta yi yawan da ba za a iya mai da kamarsa ba ko kuwa lalacewar shugabannin da suka biyo bayansa ne ta kai aka kasa samun magajinsa, ko kuma dalilai biyun ne a haɗe? Ko kuwa a’a, zamani da tsarin da muke ciki a yanzu ne suka canza kwata-kwata daga irin na lokacin su Sardaunan ta yadda zai yi wahala a samu wani ya iya yin irin tasirin da Sardauna ya yi ga mutanen Arewacin Najeriya? Idan muka duba, zamu ga cewar ba wai a Arewacin Najeriya ba, har a sauran sassan ƙasar ma, da yawa suna kukan cewar an kasa maye gurbin shugabannin da suka wuce. Shin an mayar da gurbin Cif Obafemi Awolowo a yankin Kudu maso Yamma da kuma Nnamdi Azikwe a yankin Kudu maso Gabas?

Akwai lokutan da a kan samu wasu shugabanni su kafa tarihin da kusan babu wanda ake ganin zai iya zuwa ya sha gabansu a tarihin al’ummarsu, misalin irin waɗannan mutane sun haɗa da Nelson Mandela na Africa ta Kudu, Kamal Ataturk na Turkey, Mao Zedong na China, Mahatma Gandhi na India, Kwame Nkurumah na Ghana, Julius Nyerere na Tanzania, Thomas Sankara na Burkina Faso, Jamal Abdulnasir Na Masar, Patrice Lumumba na Congo da dai sauransu. A baya-bayannan akwai Lee Kuan Yew na Singapore, Hugo Chaves na Venezuela, Mikael Gorbachaev na Russia da makamantansu. Duk da cewar wasu shugabannin su kan kafa tarihi na din-din-din sakamakon kasancewar sune sahun farko tun a lokacin da ƙasashensu suke tasowa, kuma tsarin da suka bi wajen kafa wannan tarihi yanzu babu shi; misali, yawancinsu sun yi gwagwarmayar kafa ƙasashensu, yaƙin neman ‘yancin kai daga zalunci ko mulkin mallaka, jagorantar wani juyin juya hali ko kuma yaƙin ƙwato ƙasar daga wani mawuyacin hali wanda yanzu kusan duk babu irin waɗannan abubuwa. To amma,  a kan samu wasu nagartattu mutane su biyo bayansu kuma su kamanta irin nasu ƙoƙarin, wani lokacin ma har su kere su. Misali, a ƙasar Ghana, bayan Kwame Nkurumah, an samu Jerry Rawlings wanda ake wa kallon ya bar tarihi mai kyau.  A ƙasar amurka, shekaru masu yawa bayan kashe shugaba abin alfahari Abraham Lincoln wanda ya shiga tarihi, an samu John F. Kennedy wanda shi ma ana ganin an kashe shi ne a tsaka da lokacin da yake kafa tarihi ta hanyar canza Amurka.

A nan Arewacin Najeriya, su waye ake ganin sun kwatanta kamar Sardauna, Tafawa Balewa da Malam Aminu Kano? Akwai dalilai da yawa da suka taru suka bai wa Sardauna wannan kyakkyawan mazauni da yake da shi a tarihin Arewa da Najeriya baki ɗaya. Na farko dai yana daga cikin sanannun masu ilimin zamani na sahun farko a Arewa kuma yana daga cikin waɗanda suka yi gwagwarmayar samo ‘yancin kan ƙasa da kafa siyasu na wancan lokaci. Bayan haka, ya zamo Pirimiyan yankin Arewacin Najeriya gabaɗaya, yankin da yafi kowanne yanki girma da yawan ƙabilu. A wancan lokaci, idan aka haɗa yankunan Yamma, Gabas da kuma Yamma maso Tsakiya da suke a Kudancin Najeriya, duk basu kai girman ƙasa, yawan jama’a da yawan ƙabilun Arewa ba. Bayan haka, Sardauna ya samu nasara ƙwarai da gaske wajen haɗa kan kusan dukkan jama’ar Arewa wajen zama tsintsiya-maɗaurinki-ɗaya, duk kuwa da bambance-bambancen ƙabilu da addini. Banda haka, Sardauna ya gina mutane da yawa daga ko’ina a Arewa, ya ɗaga su a duniya kuma ya jawosu jikinsa sannan kuma alherinsa ya watsu kusan ko’ina ba tare da ya dunƙule shi a waje ɗaya irin yadda shugabannin yanzu suke yi ba. Banda haka, Sardauna wanda dama basarake ne, yana da ƙarfin faɗa-a-ji da tasiri mai yawa a gwamnatin tsakiya ta wancan lokaci wacce take ƙarƙashin Sir Abubakar Tafawa-Balewa, kasancewar jam’iyyarsu ta Mutan Arewa wato NPC, ita ce take da rinjaye a wancan lokaci.

Wani abu da ya ƙara jaddada matsayin Sardauna a cikin tarihi shi ne mutuwarsa a yayin da yake tsaka da bauta wa jama’arsa. Wannan ita tasa shi ya zamo gwarzo na din-din-din. Idan muka bibiyi tarihin duniya, zamu ga mafi yawancin ‘yan gwagwarmaya da jajirtatattun  shugabannin da suka tsaya a kan gaskiya duk kashe su ake. A wancan lokacin, sojoji masu juyin mulkin shekarar 1966 sun kashe Sardauna da Tafawa-Balewa amma ba tare da sun kashe wasu daga cikin takwarorin siyasarsu na kudu ba, musamman ma yankin Inyamurai; duk kuwa da cewa suma suna cikin hamshaƙan masu riƙe da madafun iko a siyasance na wannan jamhuriya ta farko. Wannan, ita tasa har gobe ake yi wa wannan juyin mulki kallon wanda aka yi shi da manufa ta ƙabilanci da ɓangaranci, kodayake waɗanda suka shirya juyin mulkin sun sha musanta hakan tare da nacewa a kan cewa sun yi ne don kishin ƙasa. Abubuwan da suka biyo bayan juyin mulki na farko da kuma na biyu wanda ya yi sanadiyyar mutuwar Shugaba Aguiyi Ironsi watanni shida a tsakani su suka haddasa yaƙin basasar 1967 da ya yi sanadiyyar asarar ɗumbin rayuka da dukiya tare da taɓarɓarewa da lalacewar alaƙa da dangantaka a tsakanin ‘yan Najeriya. Tun daga wannan lokaci zuwa yanzu, har yanzu Najeriya ta kasa hawa kan turbar haɗin kai da ci gaba mai ɗorewa. Ko shakka babu, da ba a yi juyin mulkin farko ba, da yanzu ba haka Najeriya take ba.

Mai yiwuwa masu juyin mulkin Janairun 1966 sun ɗauka cewar kisan da suka yi wa Sardauna da Tafawa Balewa tamkar sun tozarta su Sardaunan ne, amma basu san cewar sun share musu fagen shiga tarihi bane. Domin lokutan da suka biyo bayan kashe sun, duk lokuta ne kusan na rikici da lalcewar al’amura waɗanda garama a ce basu riskesu ba. Cif Awolowo ya rayu kusan shekaru 20 bayan kashe Sardauna kuma sau biyu yana takarar shugaban ƙasa tare da Shagari amma ba ya samun nasara. Dakta Nnamdi Azikwe ya rayu shekaru 30 bayan kashe su Sardauna kuma shima ya jarraba zama shugaban ƙasa amma abin ya ci tura kuma tun yana da rai ma sai da Ojukwu da tsohon mataimakin shugaban ƙasa Alex Ekweme suka dusashe farin jininsa da tasirinsa a tsakanin al'ummarsa ta Igbo a lokuta daban-daban. Su Sardauna, Allah bai rayasu sun kai wani zamani da za a dinga labarin wani basu ba. Wannan ce tasa har gobe ake labarinsu.

Daga Arewacin Najeriya, bayan Sardauna da Tafawa-Balewa, an samu wasu nagartattun mutane waɗanda suka shahara duk da cewar basu kai kamar su Sardaunan ba. Akwai Malam Aminu Kano, Hassan Usman Katsina, Murtala Ramat Muhammad da Janar Muhammadu Buhari. Labarin salon siyasa, hikima, ƙaunar talakawa da iya mu’amala irin ta Malam Aminu Kano, babu inda bai game ba a faɗin Najeriya. Yunƙurin kawo gyara da gaggawa, tsayuwar daka da jajircewa, rashin amincewa da wargi ko rashin gaskiya irin na Murtala Muhammad, babu wanda bai ji labarinsu ba. Masana tarihi su kan kwatanta watanni shidan da ya yi yana mulki a mastayin masu matuƙar amfani da tasiri ga Najeriya. Mutuwarsa ta girgiza kowa ba ma a Nejeriya kawai ba, har a faɗin Afrika baki ɗaya. Yaƙi da zamba, cin hanci, rashawa da cin amanar ƙasa; ƙoƙarin kawo tsarin ɗa’a da martaba gwamnati da kuma farfaɗo da tattalin arziƙi irin na Janar Buhari a 1984 sun sa kowa shiga taitayinsa. Shigarsa siyasa a 2002 da kuma rawar da ya taka a cikin ta, ta sanya shi zamowa ɗaya daga cikin ‘yan siyasar da ya fi kowa yawan magoya baya talakawa zalla a tarihin Africa. An yi ittifaƙin cewar banda  Nelson Mandela, da wahala a samu mutum ɗaya tilo da ya kai Buhari farin jini a tarihin siyasar Africa.

A wannan zamanin da muke ciki, mafi yawan shugabanni a Arewacin Najeriya a dukkan matakai, basu damu da kafa wani tarihi ba. Abin da suka fi damuwa dasu sune tsananin kwaɗayin mulki, fafutukar samun muƙami ko ta halin ƙaƙa, tara ɗumbin dukiya ta hanyar sata da zamba, murƙushe ‘yan adawa, bautar da talakawa, kewaye kansu da ‘yan bani-na-iya da bambaɗanci, haɗa ƙarya da gaskiya ba kunya ba tsoron Allah, da kuma ƙaƙaba ‘ya’yansu da ‘yan korensu a kan muƙamai na siyasa. Wannan shine halin da muka samu kanmu.  A wannan halin, ta yaya za a taɓa samun magadan Sardauna, Tafawa-Balewa, Aminu Kano, Murtala Muhammad da Janar Buhari? A wannan halin, ta yaya Najeriya da Arewa zasu gyaru? A wannan halin, ta yaya talakawa zasu shaƙi iskar ‘yanci da fahimtar makomarsu da ta ƙasarsu? A wannan halin, ta yaya shugabanni zasu samu irin girmamawa da karramawar da su Sardauna suka samu? A wannan halin, wane mai kyakkyawan hali ne zai yi kwaɗayin shiga a dama da shi a harkar gwamnati?

Allah sarki, bayan tafiyar Sardauna, Arewa ta zama koma baya; Najeriya ta zama abin tausayi; mulki ya koma wasan yara; talakawa da mabiya sun koma kwaɗayayyu masu tarewa a gindin masu muƙamai a maimakon masu kishin ƙasa da neman ci gaba. Wasu daga cikin irin shugabannin yanzu, nagartarsu ba ta kai a basu koda masinja ba a lokacin su Sardauna, yau sune gwamnoni, ministoci, ‘yan majalisu, ciyamomi, kansiloli, kai har ma da shugabannin ƙasa. Waɗanda burinsu su saka riga su kece raini, babu talakawa kwata-kwata a gabansu, yau sune masu faɗa-a-ji a ƙasarmu Najeriya. Yau an wayi gari, an fi buƙatar a yi amfani da sunan Sardauna fiye da a yi koyi da shi. Yau an wayi gari, shugabanni basa tuna Sardauna sai sabgar siyasa ta tashi.  

Kungiyar haɗa kan Arewa wato Arewa Consultative Forum (ACF) tayi yunƙuri daban-daban wajen farfaɗo da daraja da martabar Arewa tare da haɗa kan mutanenta tun lokacin da aka kafa ta, amma abin ya ci tura. Ai ƙungiya ba gwamnati ba ce. Mafi yawan gwamnonin Arewa masu riƙe da madafun iko, siyasa ce kawai a gabansu, ba wai haɗin kan Arewa ba. Ba damuwar mafi yawancinsu bane a samu zaman lafiya, a bunƙasa ilimi kuma a haɓɓaka tattalin arziƙin Arewa ba. Wasu daga cikinsu ma da su aka yi amfani aka rusa Arewar da sunan siyasa.

Allah Ya ji ƙan Sir Ahmadu Bello, Sardaunan Sokoto tare da sauran mazan jiya; ba rabo da gwani ba, mayar da kamarsa.

Shafin Mallam Amir a Twitter shine: @AmirAbdulazeez  

©Mujallar Mikiya, 2016. A nemi izini kafin a sarrafa.  

Friday, October 23, 2015

Musulunci a Ibada; Kafirci a Mu’amala

23 Ga Oktoba, 2015

Daga: Amir Abdulazeez

W
ani babban kuskure da masu yawa daga cikin al’ummar Musulmi, musamman na ƙasar Hausa suke yi shine, na ɗauka da suke yi cewar Kalmar Shahda, Tsayar da Sallah, Azumtar Watan Ramadan, Bayar da Zakka ga mai dukiyar da ta kai nisabi da kuma zuwa Aikin Hajji ga mai iko, sune kaɗai Musulunci. Tabbas, waɗannan sune shika-shikan Musulunci, to amma akwai sauran abubuwa masu tarin yawa da matuƙar amfani, waɗanda rashin kiyayaesu zai iya kawo babbar alamar tambaya dangane da nagarta ko ingancin Musuluncin mutum komai yawan ibadarsa.

Akasarin Musulmai Hausawa, musamman na Najeriya, cikin sani ko rashin sani, sun raini wata fahimta da tunani a cikin ƙwaƙwalwarsu na cewar kyautata alaƙarsu da Allah (SWT) shine kaɗai abin buƙata a addinance, amma ba lallai sai sun kyautata alaƙa da bayinSa ba. Mafi yawan lokuta, mu kan manta cewa bayan haƙƙin Allah (SWT), akwai kuma haƙƙin bayinSa  a kanmu. Bayan haka kuma, abu ne mai sauƙi ka yi wa Allah (SWT) laifi ka tuba, tuba na gaskiya, kayi nadama kuma Ya yafe maka amma kuma ba zai yafe maka haƙƙin bawanSa ba har sai ka mayar masa da haƙƙinsa ko kuma ka nemi afuwarsa kuma ya yafe maka wannan laifi da ka yi masa.

Wani lokaci, na taɓa riskar mutane suna zaune ana hira, sai na shiga cikinsu na zauna. Ana zaune sai hirar wani mutum ta faɗo, nan sai kowa ya yi ta yabonsa yana shi masa albarka. Dukkan yabonsa da ake yi bai wuce a kan halayensa irinsu gaskiya, riƙon amana, kyakkyawar mu’amala da dai sauransu. Wato ba wai yabon bane laifi ko abin mamakin ba, a’a yadda aka dinga shauƙi da bege tare da nanatawa tamkar an yi maganar wani hali irin na Annabi ko Sahabi da kuma yadda suke ganin kamar samun irin wannan mutumin a duniya sai an tona. Ni na san mutumin da ake magana a kai, ba wai wasu halaye bane na daban gareshi, irin dai halayen da Addinin Musulunci ya tarbiyanci kowa  a kai ne.

Nan sai na shiga tunani mai zurfi kan yadda lalacewar al’amura suka mayar damu muke kallon mutanen kirki kamar wasu Mala’iku ba kamar ‘yan Adam irin mu ba. Wato lalacewar al’ummarmu a wannan zamani har ta kai ga cewar aikata abubuwa masu kyau irinsu gaskiya, cika alƙawari, riƙon amana da sauransu sun zama wani abin mamaki da al’ajabi? Wato yanzu idan kana da kyakkywan hali har ka zama wani daban, abin kwatance kuma abin mamaki. Ni da a zatona abubuwa irinsu sauƙin kai, girmama mutane da ganin mutuncinsu, faɗar gaskiya, tausayi; duk abubuwa ne da ya kamata a ce kowa ya dinga yi ba wai ‘yan tsirarun mutane ba. Kamata ya yi a ce ‘yan tsiraru ne a cikin mutane basa yi har a dinga mamakinsu ana kwatance da su saboda ƙarancinsu.

Masana binciken halayya da ɗabi’un ɗan Adam sun yi ittifaƙin cewar ‘yan Najeriya suna daga cikin mutane  da suka fi riƙo da addini. Sannan kuma a Duniyar Musulunci, an yarda cewar Hausawan Arewacin Najeriya suna daga cikin waɗanda suke ƙoƙarin yin ibada mai yawa. To amma kuma sai dai kash! Idan da za a auna, da sai a gano cewar babu waɗanda suke da miyagun halaye da gurɓataciyyar mu’amala kamar mu. Wannan ƙalubale ne ba ƙarami ba a kanmu domin kuwa duk wanda yake ibada domin neman yardar Allah (SWT), to alamun cewar ana karɓar ibadarsa shine a ga ba ya yawan aikata saɓo kuma ya na kyautata mu’amalarsa da bayin Allah. Karɓaɓɓiya kuma ingantaciyyar ibada bata cika haɗuwa guri guda da gurɓataccen hali ba. Idan kana ibada kuma bata hanaka mummunar mu’amala tsakaninka da jama’a ba, to ka binciki ibadar taka. Kodayake idan aka bibiya, mafi yawa daga cikin al’umma ba ma don Allah (SWT) suke yin ibadar ba. Wasu dai suna Sallah da Azumi ne kawai don sun samu kansu a cikin Musulunci kuma don kada su ƙi yi a kafurta su. Shi kuwa Aikin Hajji ma an mayar da shi wani abin kece raini da gasar arziƙi. Tir!! Ita kuwa Zakka da yake abu ce da ta shafi fitar dukiya-abar da Ɗan Adam yake tsananin so da ƙauna-babu ma wanda suka damu da ita sosai. An mayar da ita saniyar ware a cikin shika-shikan Musuluncin. Maimakon in ma gasa da kece rainin arziƙin ake so a yi, ai a Zakka ya kamata a yi ba wai a Aikin Hajji ba. Wani Malami ya na bayar da labari cewar ya ɗauki shekaru ana zuwa wajensa neman fatawoyi amma sai ya yi wata da watanni babu wanda yazo wajensa neman fatawa a kan yadda ake bayar da Zakka; amma neman fatawoyi a kan yadda za a ƙara aure kuwa ,babu magana.

Gurɓacewar mu’amalarmu da yanayin zamantakewarmu a yanzu ta kai ta kawo muna zaune sai kace dabbobi. Idan jifa ya wuce kanka, to ya faɗa kan kowa. Ba ka gudun ka yi wa mutane abinda kai baka so a yi maka. Abinda in kai aka yi wa, zai maka ciwo, ka ji zafi, sai kuma ka dinga yi wa wasu. Muna zaune kullum neman juna muke da sharri ba alkhairi ba. Kowa so yake kowa ya aikata kuskure ya yi ta faman yamaɗiɗi, amma idan an yi alkhairi sai ka ji gum. Kowa tsoron yin harkar kuɗi yake yi da  kowa. Wannan masifa har ina? A haka muke so mu ci gaba da zama muna ƙuntatawa juna zaman rayuwa?

A cikin jama’a, idan ana zaune, har ƙagara ake yi mutum ɗaya ya tashi a saka faifansa, a fara zaginsa ana cin namansa. Ƙarya kuwa ta zama ita ce mafi akasarin zancenmu. Duk maganar da aka faɗa, kowa zai karɓe ta ne cikin shakku da zargi. Idan an faɗa maka farashin abu a kasuwa, gani kake cutar ka za a yi. Wani lokacin ma har ka saya ka taho gida, za kai ta jin a ranka cewar cutar ka aka yi. Babu aminci a tsakaninmu. Cin amana a kasuwanci, zamantakewa, aiki, maƙotaka, abota, duk ba wani baƙon abu ba ne a cikin mu’amalar Hausawa Musulmi.

Tambayar da ya kamata mu yi wa kanmu ita ce, to ina Musuluncin yake a tattare da mu? Zaman mu Musulmai, wane gata hakan ya zamo wa zamantakewarmu? Mun ma fahimci Musuluncin kuwa? Da haka muke so mu tallata Musuluncin ko kuwa da haka muke so al’ummar Musulumin ta ci gaba? Shin ma Allah (SWT) yana karɓar ibadar da muke yi bisa irin waɗannan munanan halaye namu? Shin waɗannan masifun zamani da suke damunmu, basu da alaƙa da gurɓataciyyar mu’amalarmu?

Turawan Yamma waɗanda ba Musulmi ba kuma ake yi wa kallon fanɗararru sun riƙi koyarwar Addinin Musulunci hannu bibiyu a cikin mu’amalarsu da zamantakewarsu, kuma ga shi nan ƙasashensu sai ci gaba suke yi, mu kuwa gamu nan kullum sai ci baya muke yi, duk kuwa da iƙirarin addinin da muke yi a baki. Turawa sun riƙe adalci, gaskiya, amana, alƙawari, manufa, kyautatawa, ƙa’ida da sauransu. A mu’amalarsu babu cuta babu cutarwa. Mai yiwuwa sakamakon wannan kyawawan ɗabi’u nasu, Allah (SWT) Yake basu a nan duniya.

Kullum Masallatan Juma’a da guraren ibadarmu sai ƙara cika suke maƙil, amma kullum masu gaskiya da riƙon amana sai ƙara ƙaranci suke yi. Kullum yawan alhazai da maniyyata daga Arewacin Najeriya sai ƙara ƙaruwa suke, amma kuma kullum rashin adalci da rashin alƙawari sai ƙaruwa suke a cikin mu. Musuluncinnan fa, Allah (SWT) Ya kallafa mana shi don ya zamar mana gata, alkhairi da salama a tsakanimu. Bautarmu ba zata amfani Ubangiji da komai ba. Idan bamu yi amfani da Musuluncin mun taimaka tare da sauƙaƙa wa junan mu a rauywa ba, bai kamata a ce mun munana ba. Sai ka ga mutum, duk inda mai ƙoƙarin ibada yake ya kai, amma idan ka yi harka da shi, sai ya cutar da kai. Kaico! Da ka taɓa mutane, sai su ce sun fi kowa son Annabi, amma kuma a halayyarsu babu irin ta Annabin. Annabi Muhammad (SAW) shi ne mutumin da yafi kowa iya mu’amala a tarihin duniya, kuma shi Musulmi ne, da shi aka ce Musulmi su yi koyi. Ina koyin yake?

Ya kamata kowa ya yi wa kansa faɗa kuma ya tambayi kansa shin shi Musulmi ne a ibada kaɗai ko kuwa har da zamantakewa? Ta yaya zai yi ya kyautata Musuluncinsa a ibada da kuma a mu’amala baki ɗaya? Ya zai yi ya zama nagartaccen Musulmi wanda sauran Musulmai zasu kuɓuta daga sharrinsa, ba wai Musulmiya ba?

Shafin Mallam Amir a Twitter shine: @AmirAbdulazeez  

Saturday, October 3, 2015

Iftila’in Hajjin Shekarar 2015 da na Sauran Wasu Shekarun

30 Ga Satumba, 2015

Daga: Amir Abdulazeez

F
aruwar haɗarurruka  masu kawo asarar rayuka da jin raunuka a aikin Hajji ba wani  baƙon abu ba ne, amma  tun bayan da adadin yawan mutanen duniya ya haura biliyan 3 tsakanin shekarun 1960 zuwa 1970, sai ya kasance faruwar irin waɗannan haɗarurruka ta ƙara yawaita kuma a duk lokacin da suka faru a kan yi asarar rayuka masu yawa tare da jikkatar alhazai da dama. Yawan mutanen duniya na ƙaruwa, yawan Musulmi na ƙaruwa sannan kuma yawan mahajatta na ƙaruwa. Yanzu haka yawan Musulman duniya ya haura a biliyan 1.6 kuma a dukkan shekara kusan Musulmai miliyan 2 zuwa 3 ne suke zuwa Saudiyya domin sauke faralli.

Daga shekarar 1975 zuwa shekarar 2015 da muke ciki, alƙaluman hukumomin Saudi Arabia sun nuna cewar sama da mutane 4,841 ne suka rasa ransu a dalilin haɗarurruka daban-daban, yayin da wasu dubannai suka samu raunuka. Duk waɗannan alƙaluma basu shafi alhazai waɗanda suke mutuwa ɗai ɗai ko nan da can a dalilin wata rashin lafiya ba. Mafi yawan waɗannan haɗarurruka dai basa wuce turmutsutsu a yayin jifan sheɗan. A cikin muhimman haɗarurrukan da suka wakana a aiyukan aikin Hajji a tsawon shekaru 40, 8 ne daga ciki kawai basu da  alaƙa da turmutsustsu domin sun faru ne a dalilin gobara, ruguzau, zanga-zanga da dai sauransu.

Haɗarurrukan Aikin Hajji a Shekaru 40
Duk da cewar abu ne mai wahala a iya tantance tarihin tun lokacin da irin waɗannan muhimman haɗarruka masu tasiri suka fara faruwa a aikin Hajji, to amma abu ne sananne cewar a duk lokacin da a kan yi wani abu wanda yake tara dubunnai ko miliyoyin jama’a, to dole ne baza a fitar da tsammanni yiwuwar faruwar haɗari, tsautsayi ko jarrabawa daga Ubangiji ba. A mafi yawan lokuta, rundunar dubunnan mahajjata masu tattaki daga wani waje zuwa wani wajen ta kan kawo turmutsutsu wanda ya kan kawo asarar rayuka da jikkata mutane da dama.
A ranar 2 ga watan Julin 1990, turmutsutsu a hanyar wucewar alhazai ta Ma’aisim wacce take fita daga Makkah zuwa Mina da kuma filin Arafah ya yi sanadiyyar mutuwar alhazai 1,426, da yawa daga cikinsu ‘yan ƙasashen Malaysia, Indonesia da Pakistan.  Wannan shi ne haɗari mafi muni a cikin shekaru 40. Turmutsutsu ya yi sanadiyyar rasa alhazai da yawa da kuma jikkkata wasu da dama a shekarun 1994, 1998, 2001, 2003, 2004, 2006 da kuma 2015.
A  ranar 15 ga Afrilun,1997, gobara a tantunan mahajjata, ta yi sanadiyyar mutuwar alhazai 343 da raunata 1,500. Yanzu sababbin tantuna na zamani da ake yi wa alhazai amfani dasu, an sana’antasu ta yadda wuta ba ta iya ƙona su. Haka kuma a shekarun 1975 da 2011, gobara ta kawo asarar rayuka da jikkata wasu da dama a aikin hajji.
A ranar 11 ga Julin, 1991, haɗarin jirgin saman Nigerian Airways mai lamba 2120 wanda ya taso daga Jeddah zuwa Sokoto, ya yi sanadiyyar mutuwar dukkan alhazai 247 ‘yan Najeriya da kuma ma’aikatan jirgin 14. Jirgin ya faɗi ne  jim kaɗan bayan tashi daga  Filin Jirgin Saman Sarki Abdulaziz. Haka ma haɗarurrukan jiragen sama sun afku a hanyar zuwa ko dawowa daga aikin hajji a tsakanin ƙasashen duniya daban-daban a shekarun 1973, 1974, 1978, 1979 da 1980 inda kusan dukkan alhazan da abun ya shafa suka rasa rayukansu.
Rugujewar otal ɗin Al-Gaza a kusa da Harami a 2006 ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 76 da raunata 64. Sannan faɗowar ƙugiya a cikin Harami a ranar 11 ga Satumbar 2015 ya kashe mutane 118 tare da raunata 394.
An rasa alhazai da yawa sakamakon ɓarkewar cututtuka da annoba a shekarun da suka gabata. Kafin fara aiyukan Hajjin 2006, alhazai 243 ne suka rasu daga ƙasashe daban-daban sakamakon cututtuka masu alaƙa da zuciya, gajiya, tsufa da kuma rashin lafiyar da aka zo da ita tun daga gida. A shekarun baya cututtuka irinsu zazzaɓi, kwalara, polio, mura da ƙyanda sun yi sanadiyyar rasuwar wasu tsirarun alhazai.

Jifan Sheɗan (rami-aljamarat)
Jifan sheɗan wanda a ke gudanar da shi a birnin Mina, yana daga cikin rukunan aiyukan Hajji mafi haɗari a shekarun baya  saboda yawan jama’a, musamman a lokacin da mutanen suke tsallaka gadar jamarat wacce take sada su zuwa ga inda za su yi jifan. Mafi yawan cinkoso, turmutsutsu da asarar rayuka ya kan auku ne  a wajen jifan sheɗan.

Alhazai a Jamarat a shekarar 2006

Bayan turmutsutsun shekarar 2004, Gwamnatin Saudiyya ta yi aikace-aikace masu yawa a wajen gadar jamarat. An ƙara yawan hanyoyi da wajen tsallakawar mutane da kuma hanyoyin fita na ko-ta-kwana. Bayan haka kuma an musanya manyan durakun nan guda uku masu wakiltar Sheɗan ɗin da wani shafaffen bango babba na kankare domin gujewa turereniyar da alahazai suke yi a ƙoƙarin samun guri saitin waɗannan duraku a shekarun baya.
Bayan wani turmutsutsun a shekarar 2006, Gwamnatin Saudiya ta ƙara yin wasu rushe-rushe, sauye-sauye, faɗaɗe- faɗaɗe da gyare-gyare a jamarat domin sauƙaƙa wa alhazai yayin jifan sheɗan. Sannan kuma an ɓullo da tsaruka domin hana cinkoso da kuma shiga haɗari. To amma duk da wannan matakai, an sake samun turmutsutsu a wannan waje a shekarar 2015 da muke ciki.

Haɗarurrukan Aikin Hajjin Bana na Shekarar 2015
A baya bayannan, in banda shekarar 1990, babu wata shekara da aka samu rashin rayukan alhazai kamar a wannan shekara da muke ciki. Tun da farko dai, kamar kowacce shekara, an samu mutuwar alhazai ɗaiɗaiku daga ƙasashe daban-daban sakamakon dalilai na rsahin lafiya da kuma ajali. Bayan haka kuma faɗowar ƙugiya a cikin Masallacin Harami a ranar 11 ga Satumbar 2015 ya kashe mutane 118 tare da raunata 394. Tuni dai Gwamnatin Saudiyya ta tabbatar da biyan diyyar Riyal miliyan guda guda ga iyalan mamata da kuma waɗanda suka samu nakasata din-din-din a haɗarin wannan ƙugiya. Sannan kuma waɗanda suka samu raunuka aa basu Riyal 500,000. Bayan haka an yi alƙawarin kujerun aikin Hajjin baɗi biyu ga iyalan kowanne mamaci tare da sanyasu a cikin baƙin Sarkin Makka na musamman.

Faɗowar ƙugiya a cikin Masallacin Harami a ranar 11 ga Satumbar 2015 

Ranar 24 ga Satumbar 2015, hukumomin Saudi Arabia sun bayyana mutuwar sama da alhazai 769 da raunatar sama da 860 a wajen jifan sheɗan. A baya bayannan masu sanya idanu daga ƙasashe daban-daban sun fitar da sanarwar cewar adadin waɗanda suka rasu daga wannan turmutsutsu kuma aka ga gawarwakinsu ya kai 1,090 yayin da kuma har yanzu ake neman alhazai da dama waɗanda ba a gani ba. Wannan haɗari ya faru ne yayin da rukunin wasu alhazai masu dawowa izuwa masaukinsu bayan sun yi jifa, suka biyo hanyar tafiya a maimakon su bi ta hanyar da aka ware domin masu komowa inda suka haɗu kuma suka yamutsa da alhazai masu tafiya izuwa jamrat.

Asarar Rayukan Alhazan Najeriya a Hajjin 2015
Duk da dai cewar har yanzu ba a gama tattara yawan alhazan Najeriya da suka rasu ko suka ji ciwo a wannan aikin Hajji na bana ba, amma a ranar Juma’ar da ta gabata shugaban hukumar alhazai ta ƙasa, Alhaji Abdullahi Mukhtar ya bayyana adadin alhazan Najeriya da suka mutu a wajen turmutsutsun jamrat kaɗai a matsayin guda 74 yayin da sama da 71 suka samu raunuka yayin da yawan alhazan da ba a gani ba ya kai 244. Alhazan da suka rasu sun fito daga jihohin Bauchi, Borno, Cross-Rivers, Jigawa, Kano, Katsina, Kebbi da Nassarawa. Waɗanda suka ɓace kuma sun fito daga jihohin Adamawa, Bauchi, Borno, Ekiti, Abuja, Gombe, Kaduna, Kano, Katsina, Kebbi, Kwara, Nassarawa, Ondo, Niger, Plateau, Rivers, Sokoto, Taraba, Yobe da Zamfara. Wannan ya biyo bayan alhazai 6 da suka rasu yayin da 4 suka ɓata a faɗowar ƙugiyar cikin Masallacin Harami yayin kuma da wasu ƙarin 20 suka mutu tun da farko bisa dalilai na rashin lafiya ko kuma ajali.
Yanzu haka dai Shugaban ƙasa Muhammadu Buhari ya bayar da umarni ga Hukumar Aikin Hajji ta ƙasa da ta gaggauta bin ba’asin duk wani alhajin Najeriya da ya rasu, ya ji rauni ko kuma ya ɓata domin sanar da ‘yan uwansa halin da yake ciki.
 
Yawan Alhazan Duniya a duk shekara
Tun daga lokacin da jiragen sama suka zama ruwan dare a duniya, kullum yawan maniyyata aikin Hajji yake ƙaruwa daga ƙasashe daban-daban. Wannan ya biyo bayan samuwar sauƙin sufuri saɓanin a shekaru masu yawa a baya da ake zuwa a a motoci, jiragen ruwa, a kan dabbobi, wasu ma har a ƙasa.
A cikin shekaru goma da suka gabata, ƙasar Saudiyya tace ta karɓi baƙuncin yawan alhazai miliyan 25 sannan kuma kamfanin dillacin labarai na Reuters ya rawaito cewar a cikin waɗannan shekaru goma, shekarar 2012 ita ta fi kowacce shekara yawan alhazai da adadin mahajatta miliyan 3.16 yayin da shekarar 2013 ta fi kowacce ƙarancin mahajatta da alhazai miliyan 1.98. A mafi yawan shekaru, alhazan ƙasar Indonesia su kan fin na ko’ina yawa inda suke kasancewa kimanin 20% na yawan alhazan da ba ‘yan ƙasar Saudiyya ba a kowanne aikin Hajji.

Aikin Hajji a 1960
                                                                                                         
Tasirin Rashin Jituwar ƙasashen Saudi Arabia da Iran ga Aikin Hajji
Babu shakka, dukkan mai nazari a kan al’amuran yau da kullum, zai ga cewar akwai rashin jituwa a tsakanin ƙasar Saudi Arabia da kuma ƙasar Iran. Wannan rashin jituwa kuwa tana nema ta ci gaba da kawo matsaloli a a cikin aiyukan Hajji. Yayin da ƙasar Saudiyya take zargin alhazan Iran da ɓullo da matsaloli da gangan domin kawo cikas ga aikin Hajji, ita kuwa Iran ta na zargin Saudia Arabia da gazawa wajen samar da cikakken tsaro a aikin Hajji.
A ranar 31 ga Julin 1987, mutane 400 ne suka mutu yayin da dubannai suka jikkata a lokacin da jami’an tsaron Saudiyya suka yi arangama da wasu mahajjatan Iran masu zanga-zanga. Ko shakka babu wannan abu ne mara daɗi wanda za a iya gujewa afkuwarsa. Ya kamata ƙasashen biyu su yi ƙoƙari su samu daidaito  a tsakaninsu ta yadda saɓani da rashin jituwarsu a siyasance ba zai dinga shafar aikin Hajji ba.
Ko a wannan iftila’in da ya faru na Hajjin bana, an samu taƙaddama tsakanin Saudia da Iran a kan silar afkuwar matsalar da kuma adadin alhazan da suka mutu. Ita dai Iran ta zargi Saudia da ƙin bayyana ainihin adadin yawan waɗanda suka rasu inda take ganin yawansu ya haura a 4,000, kodayake ba ta bayar da wata hujja gamsasshiya ba a kan wannan adadi. Ita dai Iran, ita ce ƙasar da ta fi kowacce ƙasa rasa rayukan alhazai a Hajjin wannan shekara inda sama da mahajjatanta 400 ne suka rasu.

Ta Yaya Za a Kori Gaba?
Ko shakka babu, mahukuntan ƙasar Saudiyya suna iya bakin ƙoƙarin su domin hana afkuwar haɗurra a yayin aikin Hajji, to amma duk da wannan ƙoƙari har yanzu idan tsautsayi ya gifta a kan samu asarar ɗumbin rayuka da jikkatar jama’a. Ya kamata su ƙara ƙoƙari a kan ƙoƙari, kada su gajiya. Babu wani abu da za a iya yi wanda ya wuce rigakafi. Ya kamata Mahukuntan Saudiyya kuma su gudanar da cikakken bincike dangane da zargin wariyar launin fata da nuna fifiko ga fararen fata da ake zargin jami'anta suna yi wa alhazai.
Idan muka kalli mafi yawan haɗarurraka kuma sai muga cewar masu alaƙa da cinkoso ne. Mataki na farko da ya kamata a a ɗauka shi na a duba yiwuwar taƙaita yawan mahajjatan da suke fitowa daga kowacce ƙasa a duk shekara. A duba, a tantance a gani, duk wanda ya taɓa zuwa aikin Hajji sau biyu ko sau uku, to a dakatar da shi daga zuwa aikin sai bayan wasu shekaru domin sauƙaƙa cinkoso. Maimakon mahajatta miliyan 2 zuwa 3 da ƙasar Saudiyya ta ke karɓa kowacce shekara, a rage su zuwa miliyan 1 ko 1.5. wannan zai kawo sauƙin cinkoso ƙwarai da gaske.
Sannan kuma su mahajattan su kansu, su ƙara zage damtse wajen gujewa matakai da zasu kawo cikas. Kowacce ƙasa ta dinga yin bita tare da ilmantar da alhazai ba wai kawai yadda za su yi ibadar Hajji ba kaɗai, har da yadda za su gujewa haɗurra da kuma matakan da zasu ɗauka na gaggawa idan haɗarin ya auku.
Bayan haka, ƙasashen Musulmi su ɗauka cewar samun nasarar aikin Hajji ya rataya a wuyayensu ne baki ɗaya ba wai a wuyan ƙasar Saudiyya kawai ba. Ita ma Saudi Arabiar, a fahimtar da ita hakan. A taru a samar da wani kwamiti mai wakilcin dukkan ƙasashe domin gudu tare a tsira tare. Kada a ce za a taƙaita ikon Saudiyya da hukumominta, wajen tsarin aikin Hajji, amma ya zama sauran ƙasashe su zamo masu ruwa da tsaki wajen tsare-tsaren cikin fahimta da manufa mai kyau.
Allah Ubangiji Ya karɓi shahadar waɗanda suka rasu, marasa lafiya kuma, Allah Ya basu lafiya.

©Wannan rubutu mallakar Mujallar Mikiya ne, 2015. A nemi izini kafin sarrafa shi.

A KULA: An ciro mafi yawan bayanan dake cikin wannan sharhi daga shafin Wikipedia, daga kamfanin dillacin labaran ƙasar Faransa na AFP, wallafe-wallafen hukumomin kula da aikin Hajji na ƙasar Saudi Arabia, kafafen yaɗa labarai na ciki da wajen Najeriya da kuma ta wasu hanyoyi masu yawa wanda yawansu ba zai bayar da dama a bayyanasu ba.

Shafin Mallam Amir a Twitter shine: @AmirAbdulazeez