Fassara

Monday, May 9, 2016

Kafafen Tumasanci da Yaɗa Bambaɗanci

09 Ga Mayu, 2016



B
abu kafar yaɗa labarai da mafi yawan talakawan Najeriya suka dogara da ita domin samun bayanai kamar rediyo wataƙila saboda araha wajen mallaka da kuma sauƙin sarrafawa. A gefe guda kuma babu kafar da ake jibgawa kowacce irin shara a Najeriya, musamman ma Arewa, kamar ita rediyon. Akwai tarin matasloli da suke damun sauran kafafen yaɗa labarai irin su talabijin, jaridu da kuma yanar gizo; amma kusan babu kafar da ta kai rediyon fuskantar matasaloli iri daban-daban.

A cikin manya da ƙananan gidajen rediyo kusan guda 150 ko sama da haka da muke dasu a ƙasarnan, sama da 50% mallakar gwamnatocin jihohi  ne da na Gwamnatin Tarayya. Misali, aƙalla kowacce jiha tana da gidan rediyo mallakarta guda ɗaya a zangon AM, wasu jihohin da dama suna da ƙarin tasha ɗaya ko sama da haka a zangon FM. Bayan haka, Gwamnatin Tarayya tana da gidajen rediyo ɗai-ɗai a kan zangon FM a kowacce jiha waɗanda ta buɗe a shekarar 2003 domin faɗaɗa shirye-shiryen da babban gidan rediyo na ƙasa yake gabatarwa daga Abuja zuwa dukkan sassan ƙasarnan. Duk wannan lissafi bai haɗa da gidajen rediyoyi da dama a Najeriya waɗanda suke yaɗa shirye-shiryensu a kan yanar gizo kaɗai ba.

Mallakar kafafen yaɗa labarai a ɓangaren gwamnati ko wasu sassanta ba wani sabon abu bane a duniya kuma ba wani abin damuwa bane. Hasalima wasu manya-manyan kafafen yaɗa labarai da ake taƙama dasu a duniya wajen shahara da ƙwarewa irinsu BBC, Muryar Amurka, da DW duk mallakar gwamnati ne. Abinda yake matsala shi ne idan masu riƙe da madafun iko suna yin amfani da waɗannan kafafen yaɗa labarai domin amfanin kansu da ‘yan korensu. Ba wai an ce kada waɗannan kafafen yaɗa labarai su tallata manufofi da aiyukan gwamnati ba, amma ya kamata su yi abin cikin hikima da ƙwarewa kuma su bayar da cikakkiyar dama ga masu yin adawa da manufofin gwamnatin domin su mayar da martani.

Kafafen yaɗa labarai, musamman gidajen rediyo mallakar gwamnatocin jihohi sun zama kafafen yi wa gwamnoni tumasanci da bambaɗanci. Mafi yawan shirye-shiryensu sun karkata wajen yabon gwamnatin da take mulki komai kuwa irin ta’asar da take aikatawa. Wani lokaci, waɗannan gidajen rediyo su kan gabatar da shirye-shirye masu muhimmanci da zasu ilmantar da kuma faɗakar da al’umma, to amma saboda wannan ɗabi’a tasu mai ban haushi, da yawa an haƙura da shirye-shiryen nasu baki ɗaya. Haka za a ci gaba da tafiya; ana ɗiban kuɗin al’umma wajen gudanar da irin waɗannan kafafen yaɗa labarai, a gefe ɗaya kuma shugaban ƙasa, gwamnoni da muƙarraban jam’iyya mai mulki suna amfani da waɗannan kafafe tamkar mallakarsu na ƙashin kansu?

Wani lokaci ina tattaunawa da wani ma’aikacin gidan rediyo mallakar gwamnati a wata jiha a Arewa maso yammacin Najeriya; sai yake bani labarin wani gwamna da aka taɓa yi wanda a lokacinsa ba a isa a sanar da ko da ɗaurin auren wani ɗan jam’iyyar adawa ko mai alaƙa da shi ta wannan kafa ba. A wasu lokutan da kansa gwamnan yake bugo wa manajan gidan rediyon waya yace a katse kowanne irin shiri da ake yi, a saka masa wata waƙarsa ta siyasa wadda yake so. Wannan kaɗan ne daga cikin irin yadda wasu gwamnonin suke yi wa irin waɗannan kafafen yaɗa labarai mulkin mallaka. A wasu lokutan kuma ba laifin gwamnan bane da kansa, muƙarrabansa ne da ‘yan jam’iyyarsa suke yin uwa da makarɓiya a gidajen rediyon, shi kuma gwamnan sai ya kasa hanasu saboda dalilai na siyasa. Wani lokaci kuma manajan gidan rediyon da gwamna ya naɗa ne yake mayar da gidan rediyon fagen bambaɗanci da tumasanci ga gwamna domin ya gyara miyarsa; shi kuma ƙila gwamnan dama haka yake so.

Kafafen yaɗa labarai mallakar gwamnati su ya kamata a ce sun zamo abin misali ta hanyar fin  kowa nagarta domin su ba kuɗi suke nema ba kamar na ‘yan kasuwa kuma an kafasu ne domin su bauta wa jama’a ba gwamna ko shugaban ƙasa ba. An ƙaddara cewa su mallakar jama’a ne kuma wasu kafafe ne na sadarwa, faɗakarwa, wayarwa da kuma tallata manufofin kishin ƙasa da ci gaba. To amma maimakon haka, sun zama kafafen farfaganda da ɗaukar bangare tare da goyon bayan son zuciya. Wannan ita tasa mafi yawancin jama’a suka ƙaurace musu domin sauraron na ‘yan kasuwa masu zaman kansu duk kuwa da cewar ba finsu ƙwararrun ma’aikata ko iya gabatar da shirye-shirye aka yi ba.

Kafafen yaɗa labarai na talabijin, suma haka gwamnatoci suka lalata al’amarinsu tare da sauke su daga bin ƙa’idojin aikin jarida inda ba abinda ake yi sai tallan masu mulki da kuma hana ‘yan adawa damar faɗar albarkacin baki. To amma, daɗinta ita talabijin ba ma kowa ne yake da ita ba kuma ba dukkan masu itan bane ma suke da isasshiyar wutar lantarkin da zasu dinga kallonta akai-akai ba. Su kuwa jaridu mallakar gwamnatoci, mafi yawancinsu sun durƙushe, gwamnatocin sun kasa riƙe su. Ita kuwa yanar gizo ta kowa ce, babu wani mai mulki da zai iya hana faɗar albarkacin baki a cikinta ko kuma yace sai abinda yake so shi mutane zasu karanta. Matsalar kawai ita ce, yanar gizo tana da matuƙar matsala domin ana yawan yaɗa ƙarya da labaran ƙanzon kurege ta wannan  kafa kuma ana yawan amfani da ita wajen ci wa  jama’a da masu mulki mutunci da yi musu ƙage a inda basu ji ba basu gani ba.

Kasancewar halin da kafafen yaɗa labarai mallakar gwamnati suka samu kansu, mutane da yawa sai suka ƙaurace musu, suka koma na ‘yan kasuwa. Idan bamu manta ba, har a shekarar 1999 babu gidan rediyo mallakar ‘yan kasuwa ko ɗaya da yake aiki ka’in da na’in a Arewacin Najeriya, sannan waɗanda suke a kudanci basu fi a ƙirge su ba. Yanzu irin waɗannan gidajen rediyo sun mamaye ko’ina amma har a yanzu haka akwai tsirarun jihohin da basu da gidan rediyo masu zaman kansu ko ɗaya, sai dai na gwamnati. Irin waɗannan jihohi suna fuskantar cikas sosai wajen faɗin albarkacin bakinsu. Matsalar a nan ita ce, su ‘yan kasuwa kuɗi suke nema domin sun zuba maƙudan kuɗaɗe wajen samun lasisi da kuma kafa injina. Bayan haka suna kashe maƙudan kuɗaɗe wajen samar wa da kansu wutar lantarki, biyan haraji da albashin ma’aikatansu. Wannan ce ta sa, mafi yawancinsu kuɗi sune abinda suka fi nema ido rufe. Sakamakon haka, sai ‘yan siyasa da sauran jama’a suka yi amfani da wannan dama wajen mayar da su gurin zubar da kowacce  irin shara suka ɗebo. A wasu lokutan, matuƙar kana da ‘yan kuɗinka a aljihu, sai kaje ka biya a barka kai ta faɗar irin sakarcin da kake so da sunan siyasa; mutane su yi ta faɗin ƙazantar bakinsu amma wai su kira shi da faɗin albarkacin baki. Waɗanda basu da ilimi ko ƙwarewar da ya kamata su yi magana a sauraresu, sai su shiga gidan rediyo mai zaman kansa su yi ta soki burutsu wai su ga masu ‘yanci, banza ta faɗi.

Lokacin da ministan yaɗa labarai da ci gaban al’adu na gwamnatin Shugaba Buhari, Alhaji Lai Mohammed ya kama aiki kimanin watanni shida da suka wuce, ya yi alƙawarin cewar Gwamnatin Tarayya zata yi wa kafafen yaɗa labaranta garanbawul domin su amfani dukkan ‘yan kasa ba wai waɗanda suke mulki ko ‘yan jam’iyya mai mulki kaɗai ba. Daga wancan lokaci zuwa yanzu, alamu sun nuna an ɗan soma samun canji kaɗan ba da yawa ba musamman a kafafe irinsu NTA, FRCN, NAN da dai sauransu. Ya kamata jihohi su bi sahu wajen kawo gyara ga kafafen yaɗa labarai. Yana da kyau masu mulki su fahimci cewar aikin da suka yi ko suka ƙi yi wa talakawa shi zai yi musu alƙalanci ba wai mallake kafafen yaɗa labarai ba. Kan mutane yanzu a waye yake; idan sun yi abu mai kyau ko mara kyau, za a samu kafar da za a faɗa, koda sun hana a faɗa a kafar gwamnati.

Yana da kyau, ƙungiyar ‘yan jaridu ta ƙasa, NUJ ta dinga yi wa ma’aikatanta masu aiki a irin waɗannan kafafen yaɗa labari na gwamnati bita ta musamman tare da fahimtar dasu cewar aikin jama’a suke yi ba na mai mulki ba kuma ‘yan siyasa basu da ikon tilasta musu  kauce wa dokokin aikin jarida don kawai suna masu mulki. Su nuna musu cewar, idan suka haɗa kansu, za su iya bin duka matakan da suka dace domin tsaftace aikinsu da ƙin yarda a lalata musu shi. NUJ ta fahimtar dasu irin zubewa da ƙimarsu da mutuncin aikinsu yake yi wajen  yi wa masu mulki bambaɗanci da tumasanci a rediyo da sunan yaɗa labarai ko aikin jarida.

Majalisun dokoki na jihohi da na tarayya, ya kamata su kalli wannan matsala  tare da duba yiwuwar yin dokokin da zasu hana gwamna ko shugaban ƙasa ikon naɗa ko tuɓe shugabannin gidajen yaɗa labarai mallakar gwamnati domin samar musu da ‘yancin kansu.

Sunday, April 17, 2016

Shekara ɗaya a Gwamnatin APC: Ko Kwalliya ta Fara Biyan Kuɗin Sabulu?

10 Ga Afrilu, 2016


Daga: Amir Abdulazeez

R
anar 28 ga watan Maris aka gudanar da zaɓen shugaban ƙasar da ya kafa tarihi a Najeriya. Zaɓen da ya yi sanadiyyar kawar da jam’iyya mai mulki ya kawo jam’iyyar adawa kan mulki a karo na farko a  tarihin dimokraɗiyyar Najeriya. Haƙiƙa irin wannan ba ta cika faruwa ba a Nahiyar Afrika tun daga lokacin da turawan mulkin mallaka suka bai wa ƙasashen nahiyar ‘yancin kai har zuwa yau. Hasalima, kullum al’amuran zaɓuka ƙara lalacewa suke yi saboda ƙudurin da mafi yawan shugabannin Afrika suke da shi na dauwama a kan mulki.

Jam’iyyar APC ta ɗare kan mulki bayan tsawon shekaru 12 da jam’iyyun adawa suka shafe suna fafutukar ganin sun kawar da PDP daga mulki ba tare da sun samu wata ƙwaƙƙwarar nasara ba. Bayan kujerar shugaban ƙasa, ta kuma samu nasarar kafa rinjaye a Majalisar Wakilai ta Tarayya da kuma Dattijai ta Sanatoci. Bugu da ƙari, ta samu damar kafa gwmanati a jihohi 23 cikin 36 da ake dasu a ƙasar nan. Saboda haka tun daga sama har ƙasa, sama da 65% na madafun ikon gwamnatocin ƙasarnan a hannun jam’iyyar yake kai tsaye.

Daga kafa gwamnatin APC zuwa yanzu, aƙalla an samu shekara ɗaya; wannan na nufin cewar jam’iyyar ta cinye kashi ɗaya bisa huɗu na wa’adin da ‘yan Najeriya suka zaɓe ta tayi. Sakamakon haka, akwai buƙatar a kalli irin jagorancin da gwamnatin ta APC ta gabatar a tsawon wannan lokaci domin ganin ko kwalliya ta fara biyan kuɗin sabulu. Kafin a yi hakan, akwai buƙatar a yi waiwaye adon tafiya don ganin irin rawar da PDP ta taka a tsawon shekaru 16.

Tsakanin Gyara da Kuma Ɓarnar PDP
A jimlace zamu iya cewar, PDP ta gaza, nesa ba kusa ba wajen ciyar da Najeriya gaba a tsawon shekaru 16 da ta yi tana mulki domin kuwa mafi yawan matsalolin da muke ciki a 1999 a lokacin da jam’iyyar ta fara mulki, sune dai suke damunmu har a shekarar 2015 da ta bar mulki. To amma kuma, duk da tarin ɓarna da lalata ƙasa da mafi yawancin ‘yan Najeriya suke kallon jam’iyyar PDP ta yi, akwai wasu abubuwa na kirki da ta taɓuka. Babu shakka dole mu yarda cewar PDP ta taka rawar gani sosai wajen lalata al’amuran zaɓe da nagartacciyar dimokraɗiyya a ƙasarnan tare da ɗaukaka matsayin cin hanci da rashawa da yi wa doka karan tsaye a Najeriya. To amma ta wani ɓangare, PDP ɗin, musamman  a ƙarƙashin jagorancin Obasanjo da ‘Yaradua, ta taimaka wajen farfaɗo da tattalin arziƙin ƙasa. Misali, lokacin da Obasanjo ya karɓi mulki a hannun sojoji, asusun ajiyar Najeriya na ƙasar waje, abin da yake cikinsa bai wuce  dala biliyan huɗu ba kacal, amma lokacin da ya bar mulki zuwa lokacin  da ‘Yaradua ya rasu, akwai sama da dala miliyan 60 a cikin wancan asusu.
Kodayake ana kallon Jonathan a matasayin wanda yafi kowa ɗaurewa cin hanci da rashawa gindi, amma alokacinsa ne zaɓuka suka fara gyaruwa, abinda har ya kai ga samar da ingantaccen zaɓen da ya kawar da shi daga mulki.
Duk da irin wadaƙa da kuɗin gwamnati da ake kallon PDP ta yi, akwai abubuwa da ta tafi ta bari wanda APC zata iya ɗorawa a kai.

Halin da APC ta Samu da Najeriya
Jam’iyyar APC ta karɓi Najeriya a lokacin da ƙasar take cikin wani mawuyacin hali. Farko dai akwai rarrabuwar kai da ƙin jinin juna bisa dalilai na addini da ƙabilanci da ya kai matakin ta’azzarar da bai taɓa kaiwa ba tun bayan gama yaƙin basasa na Biafra a shekarar 1970. Bayan haka, akwai faɗuwar farashin man fetur wanwar wanda wani lokaci tsakanin shekarar 2009 zuwa 2013, farashin gangarsa guda ɗaya ta kai dalar Amurka 100 zuwa 140. A kwanakin baya, ganga ɗaya sai da ta kai dala 30, a yanzu ana sayar da ita tsakanin dala 39 zuwa 41. Wannan na nufin cewar kuɗin shigar Najeriya ya ragu da kaso kusan biyu bisa uku. Jam’iyyar APC ta samu Najeriya a cikin badaƙƙaloli daban-daban na almundahana da kuɗin ƙasa, ta samu an yi wa asusun ƙasa wakaci ka tashi tun daga kan matakin tarayya har zuwa jihohi.
Jam’iyyar APC ta gaji babbar matasala wacce ita ce ta harkar tsaro. Daga cikin wannan matsala akwai Boko Haram, fashi da makami, satar shanu, garkuwa da mutane, tada zaune tsaye a yankin Niger-Delta, satar ɗanyen mai, bangar siyasa, faɗan Fulani makiyaya da manoma, rikice-rikicen addini da na ƙabilanci a sassa daban-daban da dai sauransu.
Jam’iyyar ta gaji sauran matsaloli waɗanda suka haɗa da rashin ɗorarren samuwar man fetur, dogaron tattalin arziƙin ƙasa a kan man fetur, durƙushewar noma, rashin wadatacciyar wutar lantarki, rashin ingancin noma da masana’antu da dai sauransu.

A ina APC ta Samu Nasara Cikin Shekara Guda?
Duk da yake ba zai yiwu a ce an ga ƙwaƙƙwaran sauyi a cikin shekara guda ba, amma an ce wai Juma’ar da zata yi kyau, daga Laraba ake gane ta. Abu na farko muhimmi da gwamnatin APC ta fara yi shi ne wajen taimaka wa jihohi 27 da maƙudan kuɗaɗe a matsayin rance domin su samu su biya tarin albashin da ma’aikatansu suke binsu na wata da watanni. Wannan ta taimaka wajen ceto mafi yawan jihohin da ƙananan hukumominsu daga faɗawa mawuyacin hali.
Gwamnatin Tarayya ta APC ta taka rawar gani ta fuskar yaƙi da Boko Haram, duk da dai cewar har yanzu akwai matasalar a Arewa maso gabashin ƙasarnan amma nasarar da aka samu a bayyane take. Sai dai kuma a sauran matsalolin tsaro irinsu satar shanu, rikicin Fulani da manoma, garkuwa da mutane, har yanzu gwamnatin tana da sauran aiki a gabanta.
Jam’iyyar APC ta duƙufa gadan-gadan wajen yaƙi da cin hanci da rashawa musamman wajen tuhumar jami’an gwamnatin da suka gabata. Misali shine yadda gwamnatin ta bankaɗo badaƙƙalar sayen makamai a ofishin Sambo Dasuki da kuma yadda EFCC ta samu wani sabon ƙarfi wajen tuhuma da gurfanar da waɗanda ake tuhuma da satar dukiyar gwamnati a gaban kotu. Sai dai kuma wani hanzari ba gudu ba shine, gwamnatin har yanzu ba ta samu nasarar tabbatar da ko da mutum ɗaya a matasyin mai laifi ba a gaban kotu a tsawon sheka guda. Idan aka tafi a haka, mutum nawa zata samu damar kammala shari’unsu a cikin shekaru huɗu? Bayan haka, ana zargin gwamnatin da ƙyale wasu shafaffu da mai ‘yan jam’iyyar APC tare da maida hankali a kan ‘yan adawa kawai. Sannan kuma ana ganin gwamnatin a wasu lokuta ba ta yin biyayya ga umarnin kotu a wannan yaƙi da take yi.
Duk zaɓukan cike gurbi da aka gudanar a ƙarƙashin Hukumar Zaɓe ta mulkin APC, an kwatanta adalci. Ko jama’iyyar adawa ta PDP zata shaidi hakan. Wannan nasara ce babba.
Wata nasara kuma ita ce, yadda gwanatin take ƙoƙarin tsaftace al’amaura a dukkan matakai na gudanarwa. Banda haka, ƙimar Najeriya ta farfaɗo ƙwarai da gaske a idon duniya a ƙarƙashin jam’iyyar APC, duk da cewa wasu suna sukar Shugaba Buhari a kan yawan tafiye-tafiye da yake yi zuwa ƙasashen ƙetare.

A Ina Matsalolin APC Suke a Shekara Guda?
Gwamnatin jam’iyyar APC ta ɗauki sama da watanni shidan farkon mulkinta tana jan ƙafa da sanɗa; ta shafe tsawon wannan lokaci ba tare da ministoci da sauran jami’an gwamnati ba. Wannan ta taimaka ƙwarai wajen kawo wa gwamnatin cikas a kan tafiyar da aiyukanta. Har kawo yanzu akwai naɗe-naɗen masu muhimmanci da gwamnatin take ta jan ƙafa wajen yinsu.
Bayan haka, gwamnatin tarayya ta APC har yanzu bata yi wani yunƙuri ba a hukumance na ganin ta haɗa kan ‘yan Najeriya duba da yadda kawuna suka rarrabu a kan siyasa, addini, ƙabilanci da ɓangaranci dab da zaɓen shekarar 2015. Wannan rarrabuwar kai har yanzu tananan tana ƙara cigaba, kuma ɗaya daga cikin sakamakonta kuwa shine sabon yunƙurin kafa ƙasar Biafra da aka taso da shi ‘yan satattaki kaɗan bayan kafa sabuwar gwamnatin. Bugu da ƙari, ‘yan Kudu suna yi wa gwamnatin kallon kamar tana fifita ‘yan Arewa.
Babbar matasalar gwamnatin jam’iyyar APC ita ce yadda ta kasa shawo kan matsalar man fetur a Najeriya wacce ake ta fama da ita. Banda haka, ta kasa tsayawa a kan wata tartibiyar manufa dangane da sashen man fetur. Yau ta faɗi wani abu, gobe kuma sai ta canza, jibi kuma sai ta aikata wani abin daban.
Dangane da tattalin arziƙi, gwamnatin ta kasa shawo kan tashin farashin Dalar Amurka da sauran kuɗaɗen ƙara waje da muke tsananin buƙata domin sayo kayayyaki daga waje. A gefe ɗaya kuma, tsadar kayayyaki sai ƙara ta’azzara take yi.    
Kasafin kuɗin 2016 wanda shine na farko da jam’iyyar APC ta yi a mulkinta yazo da kura-kurai da aringizo da yawa-wani abu da ba a yi tsammaninsa a gurin gwamnati mai taƙama da gaskiya da riƙon amana ba.


Me ya kamata APC ta Yi?
Har yanzu jam’iyyar APC tana da sauran shekaru uku a cikin huɗun da aka zaɓeta ta yi; akwai buƙatar ta yi waiwayen watannin da ta shafe  a kan mulki kuma ta yi wa kanta alƙalanci da kanta. Inda ta yi kurakurai, to ta yi ƙoƙari da gaggawar gyarawa, inda ta samu nasara sai ta yi ƙoƙarin ɗorawa a kai.
Maganganu da ƙulle-ƙullen siyasar 2019 da suka dabaibaye jam’iyyar tun kafin a je ko’ina, kamata ya yi a ajiye su waje ɗaya, ‘yan jam’iyyar su haɗa kai don ganin sun sauke nauyin da jama’ar Najeriya suka ɗora musu tukunna.
Yana da kyau jam’iyyar ta bar ƙofarta a buɗe wajen karɓar shawarwari komai ɗacinsu kuma koda daga wurin maƙiyansu ne. Bayan haka kuma ya kamata su sani cewar lokaci ba abokinsu bane a yanzu, dole sai sun zage damtse.


©Mujallar Mikiya 2016

Tuesday, April 5, 2016

Ko Tinubu Zai Tsaya Takarar Shugaban ƙasa?

04 Ga Afrilu, 2016


Daga: Amir Abdulazeez

A
gurin mafi yawan manazarta harkokin siyasar Najeriya, ba wai abin da Tinubu yake buƙata shine abin tambaya ba; wataƙila tambayar ita ce, ko Tinubu zai samu abin da yake buƙata? Kasancewar gwamnatin Shugaba Buhari ta kammala kusan dukkan wasu muhimman naɗe-naɗen muƙamai ba tare da an ji sunansa a ko ɗaya daga ciki ba, alama ce da take nuna cewar akwai wani abu daban kuma babba da Asiwajun yake hari.

Yunƙurin Bola Tinubu a kusan tsawon shekaru goma da suka gabata na ganin ya zama Mataimakin Shugaban ƙasar Najeriya, wani abu ne da kusan duk wani mai sanya idanu kan harkokin siyasa yake sane da shi. Wannan yunƙuri nasa, duk da ya jawo masa abubuwa daban-daban na cigaba da kuma cikas, amma ya yi sandiyyar zamansa wani ƙusa kuma jigo a matakin ƙasa. Labari ya yi ta kewayawa cewar, ƙoƙarin da Tinubu ya yi na zama ɗan takarar mataimaki ga tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar a ƙarƙashin tsohuwar jam’iyyar Action Congress (AC)  a zaɓen Shugaban ƙasa na shekarar 2007 shi ya kawo rashin jituwa tsakaninsu wanda har ta kai ga Atikun ya bar jam’iyyar AC ɗin ya koma PDP a shekarar 2008-matakin da har yanzu yake bibiyarsa har kawo yau kuma wasu suke ganin ya taka wata ‘yar rawa wajen rashin nasarar Atikun wajen samun tutar takarar APC a shekarar 2015. An rawaito cewar shi Atiku yana ganin ba a yi adalci ba idan aka bai wa Bayerabe ko ɗan kudu maso yamma takarar mataimakin shugaban ƙasa a dai-dai lokacin da Shugaba Obasanjo wanda yake Bayerabe ne shima yake kammala shekaru 8 a kan mulki. Don haka Atiku sai ya bada mamaki wajen ɗaukar Sanata Ben Obi wanda ba a sani ba sosai daga kudu maso gabashin Najeriya a maimakon Tinubu wanda shi ya yi uwa yai makarɓiya wajen ganin shi Turakin Adamawa ɗin ya samu tikitin AC cikin sauƙi, bayan PDP ta yi masa wulaƙanci.

Rahotanni sun nuna cewar rashin amincewar Buhari na ya ajiye Fasto Tunde Bakare ya ɗauki Tinubu, ita ta kawo rugujewar ƙoƙarin haɗewa ko dunƙulewa tsakanin tsofaffin jam’iyyun CPC, ANPP da ACN a shekarar 2011 domin tunkarar Jonathan da PDP. Daga baya Buhari ya yi masa biyan bashi a 2015 inda ya yi wa Tinubu tayin bashi abinda bai samu damar bashi ba a 2011. To amma Jagaban Borgun yana sane da matsala da tarnaƙin da tsayar da Musulmai zalla za ta iya kawo wa damar da jam’iyyar APC take da shi na cin zaɓen shugaban ƙasa. Tinubu ya bai wa mutane mamaki wajen danne kwaɗayinsa tare da miƙa sunan tsohon kwamishinansa Farfesa Yemi Osinbajo a matsayin ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa. Mutane da yawa suna kallon Osinbajo a matsayin wanda kawai yake riƙe da waccan kujera a madadin jagoran APC ɗin na ƙasa.

Me yasa Tinubu ya dinga fafutukar zama mataimakin shugaban kasa, ba ji ba gani? A tarihin dimokraɗiyyar Najeriya, da wahala a samu wani wanda ya ƙaunaci zama mataimakin shugaban ƙasa kamar sa. Amsar ba wata mai wahala bace; magana ce ta dabarar siyasa, me yiwuwa yana son zama shugaban ƙasa kuma yana so ya bi ta hanya mafi sauƙi, wacce ita ce ya fara zama mataimakin shugabn ƙasa. Tinubu ya samu damar da zai tsayar da kansa ɗan takarar shugaban ƙasar jam’iyyar ACN a shekarar 2011, amma bai yi hakan ba, me yiwuwa saboda ya san ɓata lokaci ne kawai kuma ƙila ba kamar sauran ‘yan siyasa ba, shi ba burinsa kawai  ace ya taɓa takarar shugaban ƙasa ba. Bayan haka kuma bai yi wani yunƙuri na zama mataimakin Nuhu Ribaɗu ba, wanda jam’iyyar ACN ɗin ta bai wa takarar shugaban ƙasa a wancan lokaci. Kodayake hakan bai ba wa mutane mamaki ba.
Dukkan jama’a, ciki har da Tinubu shi kansa sun san cewar zai yi matuƙar wahala ga wani mutum ɗan kudu maso yamma ya zama shugaban ƙasa kai tsaye a nan kusa, duba da cewar Obasanjo ya riga ya yi mulki na tsawon shekaru 8 a cikin 16 ɗin da aka yi da dawowar dimokraɗiyya a madadin wannan yankin. Da alama dai Asiwaju ya sadaukar da burinsa na zama mataimakain shugaban ƙasa a shekarar 2015 domin tabbatar da nasarar jam’iyyar APC, sai dai kuma ba za a fitar da ran cewar kuma a ƙarshe zai tsaya takarar shugaban ƙasar kai tsaye ba a shekarar 2019. Idan Buhari ya yanke shawarar ba zai nemi zango na biyu ba, to tamkar ya share wa Tinubu hanyar zama ɗan takarar jam’iyyar APC ne a 2019.

Idan Tinubu ya samu nasarar zama shugaban ƙasa, hakan zai zamo wani sakamako ko lada na tsawon lokaci da aka ɗauka ana tsare-tsare, haƙuri, surƙullen siyasa, zuba jari da kuma sadaukarwa. Tushen kafuwar sansanin siyasa da ƙarfin faɗa-a-jin tsohon gwamnan Jihar Lagos ɗin wanda yake ƙara faɗaɗa a kullum, ya samo asali ne daga kasancewarsa gwamna ɗaya tilo wanda ba na PDP ba a yankin Kudu maso yamma da kuma ɗaya cikin biyu a yankin Kudancin Najeriya baki ɗaya bayan zaɓukan shekarar 2003 da kuma jajircewarsa da fafutuka wajen ganin an fatattaki PDP daga yankinsa na Yarabawa tare da tabbatar da siyasar adawa a ƙasa baki ɗaya.

Wasu na kallon rashin karɓar wani muƙami a gwamnatin Buhari kawo yanzu daga ɓangaren Tinubu, kamar wani abu ne da zai iya haifar masa da matasala; wasu kuwa suna ganin hakan ma ƙarfi zai ƙara masa. Masu kallon hakan a matsala suna ganin cewar waɗansu mutane da suke cikin gwamnatin Buhari zasu yi amfani da muƙamansu wajen yin aikace-aikacen da zasu birge Buharin ta yadda zai yi tunaninsu a matsayin waɗanda zasu gaje shi domin ɗorawa a kan manufofin gwamnatinsa, hakan kuwa zai kawar da Tinubu daga lissafi. A ɗaya ɓangaren, wasu na ganin cewar rashin karɓar wani muƙami zai sa Tinubu ya mayar da hankali kan siyasarsa kuma zai raba kansa da duk wata badaƙƙala mai alaƙa da aikin gwamnati. Sannan kuma jam’iyyar APC  zata cigaba da jin cewar har yanzu yana binta bashin da baza ta iya biyansa ba. Bayan haka matasayinsa na kafi-sarki zai ci gaba da ɗorewa.

Ko shakka babu, ƙudurin Tinubu na zama shugaban ƙasa, akwai yiwuwar ya gamu da ƙalubale daban-daban. Akwai muhimman mutane da mai yiwuwa su nemi yin takara da shi tun ma daga yankinsa na kudu maso yamma. Muhimman Yarabawa irinsu Babatunde Fashola, Kayode Fayemi ko ma Yemi Osinbajo, duk zasu iya nuna sha’awarsu ga kujerar shugaban ƙasa. Muhimman ‘yan jam’iyyar APC daga yankin kudu maso gabas na Inyamurai kamarsu Chris Ngige, Ogbonnaya Onu da Rochas Okorocha suma zasu iya cewar to idan har mulki zai dawo kudu ne, to kamata yayi a ce kudu maso gabas zai dawo ba kudu maso yamma ba. Duk da irin shahararren gangancin siyasa da ragon azancin da kudu maso gabas suka yi a zaben shekarar 2015, zasu iya kallon Tinubu a matsayin wanda ya hana a basu kujerar mataimakin Shugaban ƙasa kuma zasu tashi tsaye a kansa wajen ganin bai ƙara hanasu wata damar ta samun kujerar mataimakin shugaban ƙasar ba, da ma ƙila ta shugaban ƙasar baki ɗungurugum a shekarar 2019. Wata mishkila da Tinubu zai iya fuskanta ita ce yankin Arewa wanda zai iya cewa idan har Buhari ba zai yi zango na biyu ba, to dole a ƙyale wani daga yankin aƙalla ya ƙarashe mulkin na tsawon shekaru huɗu. Mutane irinsu Atiku Abubakar, Bukola Saraki, Rabi’u Kwankwaso, Nasir El-Rufa’i da kuma wasu gwamnonin APC ɗin da suka gama zangonsu na biyu duk zasu yi yunƙurin gwada damarsu idan hakan ta faru.

Kasancewar mafi yawan jam’iyyar APC a aljihun Tinubu take, zai zamo riba a gareshi sosai, to amma kuma zai iya zamo masa matsala. Ya tara maƙiya da yawa a ƙoƙarinsa na baza ƙarfin ikonsa zuwa ko’ina a cikin jam’iyyar. Babu wani mutum da ya cicciɓa kuma ya sassaka yawan mutane a cikin shugabancin jam’iyya da gwamnati kamarsa, kuma bisa ga dukkan alamu, zai iya samun goyon bayan Buhari. Sai dai kuma, kankanewarsa da babbakewarsa a kowanne bangare da kuma ƙoƙarin zama mai ruwa da tsaki a kan duk wani abu zai iya kawo masa tarnaƙi. Yanzu haka rahotanni sun fara kewayawa cewar, wasu jiga-jigan APC sun fara tunanin barin jam’iyyar saboda irin ƙarfin da Tinubu yake da shi. Kwanakin baya, an kawo masa cikas a yunƙurinsa na ƙaƙaba wa Majalisun Tarayya shugabanci; idan bai bi a hankali ba, ɓangarori da yawa a cikin APC zasu dunƙule waje ɗaya domin su yi masa taron dangi a 2019.

©Mujallar Mikiya, 2016.

Twitter: @AmirAbdulazeez

Wednesday, March 23, 2016

Kwankwaso, Ganduje da Siyasar Aika-Aika

18 Ga Maris, 2016


Daga: Amir Abdulazeez

B
abu wanda wannan rikicin siyasar tsakanin Kwankwaso da Ganduje za ta bai wa mamaki sai wanda ba ya bibiyar al’amuran siyasar Jihar Kano da Najeriya ko kuma a’a yana bibiya amma ba ya fahimtar yadda abubuwa suke tafiya. Don haka ba rigimar ce yanzu abin mamaki ba, fara ta da aka yi da sanyin safiya kafin tafiya ta yi nisa shine abin mamaki. Kodayake akwai waɗanda suka so ma ayi wannan rigima tuntuni ma kafin wannan lokaci, to amma masu hasasshe sun tabbatar wa da irin waɗancan mutane masu azarɓaɓi tun a lokacin da gwamna Ganduje ya cika kwanaki 100 a kan mulki cewar rigima fa za a yi ta, sai dai jiran lokaci. Ba wai abubuwan da suka faru a zuwan Kwankwaso ‘ta’aziyya’ ne ya tada rigimar ba, sune dai suka munanata.

Bari mu manta da batun wanene da gaskiya ko kuma wanene ba shi da gaskiya a cikin wannan al’amari, mu manta da waye ya yi butulci ko waye bai yi ba. Kai mu ma manta  da batun wanene zai yi nasara, wanene kuma zai sha kashi. Mu tambayi kanmu da su waɗannan shugabanni biyu masu rigima, shin wannan rikici shi ya kamaci kowannensu a dai-dai wannan lokaci kuma menene sakamakonsa?

Bari mu fara da Gwamna Ganduje. Maigirma gwamna yana da manya-manyan maƙiya guda uku a yanzu kuma duka a cikinsu babu Kwankwaso. Sahun gaba a cikin maƙiyan Ganduje sune masu kiran kansu magoya bayansa waɗanda suka fara yi masa kamfen ɗin tazarce a 2019 tun ma kafin ya cika kwanaki 100 a kan mulki. Wasu daga cikin irin waɗannan ‘magoya baya’ basu ma san da Ganduje ba sai bayan ya samu takara, wasu ma sai bayan ya ci gwamna, amma bambaɗanci da bani-na-iya tasa su suka fi kowa fada yanzu a gurinsa. Duk wani magoyin bayan gwamna na gaskiya ba wai na son zuciya ko rinto ba, kamata yayi ya mayar da hankali wajen taimaka masa da faɗar gaskiya komai ɗacinta, shawarwari da addu’a domin ya sauke nauyin da yake kansa kuma ya samu ya gama zangonsa na farko lafiya cikin nasara ba tare da an samu aika-aika ba.

Maƙiyin Ganduje na biyu shine faɗuwar farashin ɗanyen man fetur wanda ya haddasa masifar ƙarancin rashin kuɗin shigar da shi da takwarorinsa gwamnoni suke ciki. Bayan haka, yunƙurinsa na rage kaifin wannan matsala ta hanyar zafafawa a kan karɓar haraji, ya kawo wa gwamnatinsa baƙin jini da rashin fahimta a gurin mutanen Kano. Ko an ƙi ko an so, wannan za ta dakushe ƙoƙarin gwamnatinsa na ganin ta yi abin kirki. Wannan matsala ita kaɗai ta isa ta hanashi ya wanye da mutanen Kano lafiya wanda tun a yanzu da yawa daga cikinsu sun fara yi masa laƙabi da mai zango ɗaya kuma suke kallonsa a matsayin mai rauni wanda ba zai iya mulkin ba ma.

Matsalar Ganduje ta uku ita ce ƙunshin  da tsarin gwamnatinsa. Kwata-kwata yanayin ƙunshin gwamnatinsa bai nuna cewar so ake yi a cimma wani abu na a-zo-a-gani ba. Mafi yawan naɗe-naɗensa sun fi maida hankali ga biyan bashi ga waɗanda suka wahaltawa kamfen ɗinsa da kuma waɗanda zasu taimakeshi ya yaƙi Kwankwaso ko kuma ‘yan bambaɗanci. Banda haka, fama da rashin kuɗin shiga bai hana gwamnatin yin naɗe-naɗe barkatai marasa kan gado ba. Bugu da ƙari, bayan watanni 10, har yau gwamnatin bata nuna alamun tana da wata alƙiblar da tasa a gaba ba; waɗanne abubuwa ne zata fi mayar da hankali  a kansu; noma, kiwon lafiya ko me? Idan Ganduje ya tsaya faɗa da Kwankwaso ba tare da ya yi maganin waɗannan maƙiya nasa ba, to lallai a ƙarshe za a samu aika-aika.

Bari mu dawo kan Kwankwaso. A yanzu Sanatan Kano ta tsakiya, babu abin da ya kamata mu yi masa sai jaje kuma mu ji tausayinsa saboda dalilai da yawa, amma ga kaɗan daga cikinsu. Na farko dai, Kwankwaso yana girma amma lamurransa suna ƙara lalacewa. A matsayinsa na wanda yake tunkarar shekaru 60 da haihuwa a duniya, ya kamata a ce ya haƙura da mugunyar aƙidarsa ta ba-zai-bi-ba, sai dai a-bi-shi. Kullum gani yake shine mai sawa da hanawa kuma a haka zai dauwama. Tunaninsa, shi ya kafa kowa, ya kuma manta cewar shima kafa shi aka yi. Taƙamarsa shi babbane kuma jagora, amma abubuwan da yake yi wani sa’in, masu baki da kunu da ‘yan aika-aika ma baza su yi ba.

Abu na biyu da ya kamata  a yi wa Kwankwaso jaje a kansa shine tsananin matsawa kansa da yayi sai ya zama Shugaban ƙasar Najeriya. Ba wai muradin zama shugaban ƙasar ne laifi ba, yadda yake ƙaddamar da muradin nasa ne matsala. Duk wanda baya goyon bayan takararsa, to ganinsa yake kamar maƙiyinsa ne, me yiwuwa shi a ganinsa ƙila dole ne kowa ya goyi bayansa sai kace kowa bawansa ne. Ya manta dimokraɗiyya ake yi ba wai aika-aika ba.

Abin jaje na uku ga Kwankwaso shine duk da farfaganda, surutai dan nuna yafi kowa iyawa da yayi ta yi  a lokacin mulkinsa, sai gashi gwamnatinsa ta ƙare da zarge-zarge da kuma yawan bashi da ba a taɓa jin irinsa ba a tarihin Kano. Har yanzu Sanata Kwankwaso ko magoya bayansa sun kasa yi wa jama’ar Kano cikakke kuma gamsasshen bayani a kan zarge-zargen da ake yi masa na wawashe kuɗaɗen ƙanannan hukumomin Kano da rana tsaka tare da yin kamfen ɗin takararsa ta shugaban ƙasa dasu. Daga an tayar da wannan magana sai magoya bayansa su fara yi wa jama’a labarin irin aiyukan da ya shimfiɗa, sai kace yin aiki wani lasisi ne da mutum kuma zai ɗebi kuɗin jama’a. Idan da nine Kwankwaso, zan mayar da hankali ne wajen wanke kaina daga waɗannan zarge-zarge domin karsu zamarmin tangarɗa a 2019, a maimakon yunƙurin nuna wa Ganduje cewar bai isa ba, nine isasshe.  Kai ko ba don 2019 ba, zan yi hakane don gudun kada waɗannan zarge-zarge su lalata min tarin aiyukan alkhairin dana yi a mulkina kuma ta yadda ba zan bari sunana ya shiga cikin tarihin waɗanda ake zargi da yin aika-aika da kuɗin Kano ba. Sannan kuma ba zan ci gaba da kallon Kano kaɗai kamar ita ce zata bani shugaban ƙasa ba, Najeriyar zan dinga kalla gabaɗaya.

A ƙarshe, akwai shawarwari, duk da dai cewar faɗa ko rikicin siyasa irin wannan ba a cika samun wani sulhu mai ma’ana a cikinsa ba, amma dai kowa akwai hanyar da zai bi don kada ya zamo abin dariya a gurin mutane. A mayar da makamai na zahiri, a ci gaba da yin faɗan ta-ciki-na ciki a baɗini.

Ya kamata Gwamna Ganduje yayi amfani da tarin ƙwarewarsa da hangen nesansa da kuma haƙurinnan da aka sanshi da shi wajen taka-tsantsan a wannan rigima. Ko ba komai, shi ne wanda nauyin jama’ar Kano yake kansa ba wai Kwankwaso ba, ya dubi illar da rigimar za ta iya yi wa wannan nauyi da yake kansa. Sannan kuma gwamna mai ci yanzu, ya tuna cewar fa ya bamu labari a baya cewar duk nasarorin da tsohon maigidansa ya samu, tare suka samu; mai zai hana ya rungumi aika-aikar da suka yi tare?

Kwankwaso! Kwankwaso! Kwankwaso! Sau nawa na kira ka? Lokacinka ya wuce, ka gode wa Allah; kaf  a tarihin siyasar Kano babu wanda ya kai ka sa’a da samun ni’imomi. Ganduje ko Buhari duk baza su hana ka zama shugaban ƙasa ba, idan Allah Ya so, faɗa ko rashin faɗanka dasu ba zai sa ko ya hana komai ba. To wai me neman Shugaban ƙasa ma, ina shi ina wani faɗa? Ganduje kuma, ba kai zaka cireshi ba, ka barshi da mutanen Kano domin su suka ɗaukeshi aiki. Idan ka ci gaba da faɗa da shi, akwai fa tarin aika-aikar da zai iya bankaɗowa wacce mai yiwuwa ba zaka so jinta ba, kai shima baza ta yi masa kyau ba. Idan kuma kana ganin ka yarda da kanka kuma zaka iya kare kanka, to ga fili ga mai doki.

‘Yan uwana talakawa, wannan rigima ce ta ‘yan siyasa, kada mu yarda su raba mana kawuna ko kuma magoya bayansu su raina mana hankali, duk maganace ta buƙatar kai da son zuciya, ba don mu ake yi ba. Irin haka ta faru ba sau ɗaya ba sau biyu ba, ya kamata mu ɗauki darasi, idan kuma mun ƙi, to zamu ga aika-aika.


Twitter: @AmirAbdulazeez   

Friday, February 12, 2016

Ta Yaya Zamu Farfaɗo da Darajar Naira?

12 Ga Fabrairu, 2016.




T
un bayan gama Yaƙin Duniya na Biyu a shekarar 1945 tare da bayyanar ƙasashen Amurka da Rasha a matsayin mafi ƙarfin-faɗa-a-ji a duniya, Dalar Amurka ta fara kuma take ci gaba da gauraye duniya. Lokacin kuwa da yaƙin cacar baki wanda aka fi sani da Cold War tsakanin ƙasashen Rasha da Amurkar ya zo ƙarshe a shekarar 1991 tare da bayyanar ƙasar Amurka a matsayin ƙasa ɗaya tilo mafi ƙarfi a duniya, tuni Dalar Amurka ta game ko’ina a faɗin duniya; ta zama takardar kuɗi ta ƙasa da ƙasa, sannan kuma ma’aunin darajar sauran kuɗaɗen ƙasashen duniya. Kodayake takardar kuɗi ta Euro wanda ake amfani da ita a Nahiyar Turai da Pound Serling to Ingila sun fi ta daraja ta fuskar tsada, amma basu ko kama ƙafar ta ba wajen hada-hada da karɓuwa ba.

Ɗaya daga cikin matakan da gwamnatin Shugaba Yakubu Gowon ta ɗauka tun bayan kammala yaƙin basasa shine na ƙirƙiro da takardar kuɗi ta Naira a shekarar 1973. Kafin wannan lokacin, Najeriya tana amfani ne da takardar Pound Sterling ta Africa ta Yamma wacce take da kwatankwacin daraja ɗaya da Pound Sterling ta Birtaniya a wancan lokaci, kusan ma babu wani bambanci tsakaninsu. Ita kanta Nairar da aka ƙirƙiro daga baya, kusan darajar su ɗaya da Pound Sterling ta birtaniya, har akwai lokutan ma da ta ɗara ta a daraja a lokutan da aka fuskanci tsadar ɗanyen man fetur wanda Najeriya take kan ganiyar haƙowa a wancan lokaci. A tsakanin shekarun 1978 zuwa 1982, akwai lokacin da sai mutum ya bayar da Dalar Amurka biyu sannan za a bashi Naira ɗaya; ma’ana, Naira ta ninka Dala a daraja a wancan lokaci.

Duk da zargin karya tattalin arziƙi da sojoji suka yi wa gwamnatin Shugaba Shehu Shagari, amma har ya bar mulki ana canza kowacce Dalar Amurka ɗaya a kan tsakanin Naira ɗaya zuwa ƙasa da haka. Lokacin da Janar Babangida ya yi wa Janar Buhari juyin mulki, ana canzar kowacce Dalar Amurka ɗaya a kan Naira ɗaya zuwa biyu. A lokacin Babangida ne, Najeriya ta rungumi tsarin gudanar da tattalin arziƙi na Hukumar Bayar da Lamunin Kuɗi ta Duniya (IMF) tare kuma da karɓar maƙudan kuɗaɗe a matsayin rance daga wannan hukuma. Wannan tsari da Babangida ya kawo wanda aka fi sani da SAP, tsarin da tun da farko ya kasa samun shiga a gurin gwamnatin Janar Buhari, shi masana da dama suke ganin ya jefa Najeriya a cikin mawuyacin halin tattalin arziƙin da har yanzu bata farfaɗo ba. Bayan ‘yan wasu lokuta da kankamar tsarin SAP, a shekarar 1991, Dalar Amurka ɗaya sai ta koma Naira goma. Lokacin da Babangida ya tafi a 1993, tuni Dalar Amurka guda ɗaya ta koma tsakanin N22 zuwa N57, ya danganta da alƙaluman gwamnati ko na ‘yan canji. Dalar Amurka ta dinga hawa ba ƙaƙƙautawa a hannun gwamnati da ‘yan canji tun daga lokacin Shugaba Abdussalmi har zuwa lokacin Mulkin Shugaba Jonathan inda ta zama N86, N100, N140 har sama da haka. A yau Dalar Amurka ɗaya a hukumance, ana canzar ta ne a kan N197,  a hannun ‘yan kasuwa kuwa tana kaiwa N310 zuwa N315. Babu wata lalacewa ko taɓarɓarewa da za a iya kwatantata da wannan.

Kafin a san magani, ya kamata a fahimci cuta tukunna. Duk da cewar mafi yawan ‘yan Najeriya suna ɗora alhakin faɗuwar darajar Naira da taɓarɓarewar tattalin arziƙi a kan tsarin SAP na turawan yamma da Shugaba Babangida da Ministan harkokin kuɗinsa na wancan lokacin, Cif Olu Falae, to amma ya kamata mu kalli wasu dalilan da dama bayan wannan. Tun daga shekarar 1973 zuwa 2016, kowanne ɗan ƙasa ya bada gudunmawarsa wajen lalacewar darajar Naira. Akwai laifin gwamnati, shugabanni, ‘yan siyasa, ‘yan kasuwa, ma’aikata da kuma talakawa.

Tun farko dai ƙasashen Afrika ciki har da Najeriya da kuma sauran dukkan ƙasashe masu tasowa sun tafka babban kuskure wajen tunanin cewar ƙasashen Turawa masu ƙarfin tattalin arziƙi zasu ji tausayinsu ko kuma zasu kawo wani tsari wanda zai taimakesu tsakani da Allah ba tare da wani kitso da kwarkwata ba. Kullum hasashen irin waɗancan ƙasashe shine ya za a yi mu dauwama a ƙasa, su suna sama, to ta yaya zasu bamu wani taimako nagari? Ci gaba da taɓarɓarewarmu, ita ce ci gaba da bunƙasarsu; idan muka zama iyayen gidan kanmu, wa zasu mulka balle har su yi masa fankama? Kullum burinsu su dinga tsakuro tallafi suna bamu kamar almajirai ko kuma su bamu rancen maƙudan kuɗuɗe domin mayar damu bayin ƙarfi da yaji. Ƙasashe irinsu China, India da Brazil da suka farga tun da wuri suka yi watsi da dogaro a kan Turawa, yau sun tsaya kai da fata sun ciyar da kansu gaba, kuma sun fita daga ƙangin bauta. A yau ƙananan ƙasashe da dama sun haramtawa kansu amfani da kayayyakin Turawan Yamma domin bunƙasa nasu na gida Dole ne Najeriya ta kama hanyar bin sahun waɗannan ƙasashe koda kuwa a faro zamu sha baƙar wahala kafin mu murmure.

Tsawon shekaru da yawa, Gwamnatin Najeriya a ƙarƙashin shugabanni daban-daban sun ƙyale ƙasar ta dogara da ɗanyen man fetur ba tare da ta maida hankali  a kan noma, kiwo da bunƙasa masana’antu ba. Wannan ta jawo, babu wata muhimmiyar hanya da kuɗaɗen ƙasar waje suke shigo mana sai ta hanyar ɗanyen man fetur, kuma gashi tataccen fetur ɗin sai mun fita wata uwa duniya mun sayo shi tunda mun bar namu matatun a lalace, hakan ya kawo faɗuwar darajar Naira, musamman a yanzu da farashin ɗanyen man ya faɗi wanwar  a kasuwar duniya. Bayan haka kuma, gwamnatoci da yawa da suka shuɗe basu tashi tsaye sun ɗauki takardar Nairar ita kanta da muhimmanci ba balle su kare ta. Ana zargin da yawa daga cikin shugabannin Najeriya da ‘yan siyasarta da wawushe kuɗin ƙasa, kuma abin takaici, maimakon su ajiye su a Najeriya ko kuma su zuba hannun jarin a Najeriya, a’a sai su ɗebi kuɗin su ajiye su a ƙasashen waje. Daga 1999 zuwa 2015, Allah ne kaɗai ya san iya dukiyar da ɓarayi daga cikin shugabannin Najeriya, ma’aikata da ‘yan siyasa suka sata suka kai ƙasar waje, wannan ya taimaka wajen karya tattalin arziƙin ƙasa da kuma karya darajar Naira.

Sana’ar canji, wacce kwata-kwata da ba a san da ita ba a Najeriya sai daga baya ta taka rawa wajen lalata darajar Naira duk da cewar kuma ta taimaka wajen sauƙaƙa samun kuɗaɗen ƙasashen waje tare kuma da samar da sana’a ga mutane da dama. Babbar matsalar ita ce, su ‘yan canji riba ce zalla kuma tsababa kawai a gabansu ba wai makomar darajar Naira ko kishin ƙasa ba. Wannan ce ta kawo lalacewar sana’ar canji kuma a maimakon ta zamo mataimakiya wajen kare martabar Naira, zai ta zamo wata hanyar da ake amfani da ita wajen kassara Nairar tare da ɗaukaka darajar kuɗaɗen ƙasashen waje domin kawai a ci riba. Bayan haka kuma, wasu mutane suna yin amfani da harkar canji ko kuma ‘yan canjin wajen karɓo kuɗaɗen ƙasashen waje a hannun gwamnati kuma su ɓoyesu ko kuma su yi amfani dasu ta hanyoyin da zasu cutar da tattalin arziƙin ƙasa. Dole sai an tsaftace tare da yin garanbawul ga wannan sana’a idan har ana so a samu farfaɗowar darajar Naira.

Mafi yawan ‘yan kasuwarmu, kullum tunaninsu shine su fita ƙasar waje su sayo kaya, a maimakon su maida hankali wajen samar da fasahar ƙera kayan a nan gida Najeriya da kansu. Kusan kowa yafi son daga-buhu-sai-tukunya, kawai ya sayo kaya ya sayar ya ci riba a karan kansa, koda ƙasar za ta mutu. Bugu da ƙari kuma, mafi yawan ‘yan kasuwar basa biyan haraji balle gwamnati ta ɗan ƙaru da wani abu. Wannan tasa mun wayi gari kusan komai da muke amfani da shi, shigo dashi ake daga ƙasar waje, hatta tsinken sakace. Mu kusan babu mai shigowa ya sayi namu kayan, amma kullum muna kan hanya wajen sayo kayan wasu; wannan ta taimaka wajen faɗuwar darajar Naira. Mafi yawan ‘yan Najeriya babu kishin ƙasa a gabansu, kowa burinsa kawai ya gamsar da kansa ko ya biya buƙatarsa, babu ruwansa da makomar ƙasa. Wannan ita tasa mafi yawancin mutane, burinsu su sayi kayayyakin ƙasashen waje,  a dalilin haka ne ma kayayyakin da aka sana’anta a Najeriya suke yin kwantai kuma waɗanda suke yinsu suke watsarwa suna koma sayo na ƙasar waje. Kullum tunaninmu wai kayan ƙasar waje yafi kyau, to ta yaya namun zai yi kyau, idan bama saya? Munata rage wa kanmu ƙarfi muna ƙarawa masu ƙarfi ƙarfi; wannan ta kawo faɗuwar darajar Naira.

Idan da barci muke , to ya kamata yanzu mu farka. Takardar kuɗin ƙasa wata aba ce mai martaba da ƙima wacce take nuna irin darajar tattalin arziƙi da kuma darajar ƙasar ita kanta. Yanzu Naira ta hau kan wata turbar taɓarɓarewar da ba a taɓa gani ba kuma idan muka zuba ido cewar gwamnati ce kaɗai za ta gyara ta, to kuwa zamu sha mamaki. Idan muka yi wasa sai mun wayi gari Naira ta koma bata da amfanin komai sai zubarwa. Duk da cewar wannan matasala ta kwararo a cikin shekaru sama da 40 baya, amma idan muka haɗu a kan manufar kawo gyara, to Naira zata farfaɗo ko da kuwa ba yanzu yanzu ba.

Tun da farko dai dole gwamnati ta maida hankali a kan harkar noma tare da samar da isasshiyar wutar lantarkin da  zata bai wa masana’antu dama domin su farfaɗo su dinga aiki ka’in da na’in. Banda haka, dole ne a tsaurara matakan ladabtarwa a kan masu satar dukiyar ƙasa suna zuba hannun jari  a ƙasashen waje. Dole ne gwamnati ta zage damtse wajen dawo da dukkan kuɗaɗen Najeriya da aka sace daga ƙasashen waje. Kodayake Turawan yamma da sauran wasu ƙasashe baza su so a janye wannan ɗimbin dukiya wadda take ƙarawa tattalin arziƙinsu ƙarfi ba, amma wannnan ya zama dole in har muna so mu cigaba. Bayan haka, idan gwamnati tana so ‘yan Najeriya su sayi kayayyakin da aka ƙera acikin ƙasar, to sai ta zamo abin koyi. Dukkan abin da zata saya, ita ma ta dinga sayen na cikin gida kuma ta rage bai wa kamfanunuwan ƙasashen waje kwangila sai ya zama dole. Bayan haka ta duba yiwuwar kafa dokar hana shigo da rukunin wasu kayayyakin da za a iya ƙerawa a nan gida ko kuma ta sanya haraji mai tsanani  a kansu.

Dolene ‘yan siyasarmu, musamman na 1999 zuwa 2015 su karɓi alhakin ɗaiɗaita mana tattalin arziƙi da jefamu a cikin mawuyacin halin da muke ciki da suka yi. Wajibine a kawo ƙarshen siyasar kuɗi domin guje wa ɓarnatar da dukiyar ƙasa. Yanzu ‘yan siyasarmu saboda tsananin rashin kishin ƙasa, idan zaɓe ya matso, duk wata Dalar Amurka da manyan kuɗaɗen ƙasashen waje dake cikin Najeriya sai sun sayesu domin su saya ko su ƙwaci zaɓe, saboda suna so su dauwama a kan mulki, alabashi ita kuma ƙasa taje can ta shiga halin da zata shiga babu ruwansu. Naira ta yi musu rashin daraja da yawa, don haka Daloli suke rarrabawa domin su ba sai an yi kayansu ba niƙi-niƙi. Dalolin da ya kamata a sayar wa da ‘yan kasuwa domin su saro kaya, ‘yan siyasa da masu mulki duk sun sayesu; wacce take hannun gwamnatinma kuma sun yi amfani da alfarmarsu sun saye, a wasu lokutanma sun sace su kai tsaye. Ta yaya Naira ba zata lalace ba?

Wajibi ne ‘yan kasuwar mu su haɗu a kan yadda zasu dinga ƙera kaya da kansu a maimakon sayosu daga ƙasashen waje. Babu shakka, wannan wani abu ne mai wahala, amma idan suka sa kansu zasu iya, kuma a kwana a tashi, zasu saba har su zama ƙwararru. Yanzu ga Aliko Dangote nan, ai bai zama mai kuɗin Africa baki ɗaya ta hanyar shigo da simiti ba, ya zama ne ta hanyar sana’antashi ya fitar zuwa wasu ƙasashe ko kuma a biyoshi har inda yake a saya. Mu kuma talakawa da mafi yawan masifa take ƙarewa a kanmu, mu yafi kamata ma mu tashi tsaye. Kowa ya yi duba na tsanaki a kan kansa ya ga shin yana sayen kayan da aka ƙera a Najeriya?  Idan akwai abin da ake ƙerawa a Najeriya, to ka ƙyale na ƙasar waje. Idan kana ganin na ƙasar wajen yafi na gida kyau, to sayensa da kake yi ne yasa yafi na gidan kyau, idan ka koma sayen naka, shima zai yi ingancin da watarana zai fi na ƙasar wajen.

Wednesday, January 6, 2016

Shekaru 50 Bayan Sardauna: Ko Mazan Yau Zasu Yi Kamar na Jiya?

4 Ga Janairu, 2016



S
hekaru hamsin bayan juyin mulki na farko a Najeriya wanda ya yi sanadiyyar kashe Sir Ahmadu Bello, Sardaunan Sokoto da Sir Abubakar Tafawa-Balewa, har yanzu waɗannan mutane sune abin misali a Arewa, Najeriya da ma wasu sassan Afrika baki ɗaya. Shekaru hamsin da kwanta damarsu, har yanzu kusan an kasa cike giɓin da suka tafi suka bari, musamman ma ta ɓangaren Sardauna. Dama-dama ma Tafawa-Balewa, an samu wasu gwarazan shugabannin a matakin ƙasa, irinsu Marigayi Murtala Ramat Muhammad da suka kwatanta yin jagoranci bisa jajircewa da adalci kamar irin nasa, amma har yanzu Arewacin Najeriya ta kasa samun wani shugaba kamar Sardauna.

Shin nagartar Sardauna ce ta yi yawan da ba za a iya mai da kamarsa ba ko kuwa lalacewar shugabannin da suka biyo bayansa ne ta kai aka kasa samun magajinsa, ko kuma dalilai biyun ne a haɗe? Ko kuwa a’a, zamani da tsarin da muke ciki a yanzu ne suka canza kwata-kwata daga irin na lokacin su Sardaunan ta yadda zai yi wahala a samu wani ya iya yin irin tasirin da Sardauna ya yi ga mutanen Arewacin Najeriya? Idan muka duba, zamu ga cewar ba wai a Arewacin Najeriya ba, har a sauran sassan ƙasar ma, da yawa suna kukan cewar an kasa maye gurbin shugabannin da suka wuce. Shin an mayar da gurbin Cif Obafemi Awolowo a yankin Kudu maso Yamma da kuma Nnamdi Azikwe a yankin Kudu maso Gabas?

Akwai lokutan da a kan samu wasu shugabanni su kafa tarihin da kusan babu wanda ake ganin zai iya zuwa ya sha gabansu a tarihin al’ummarsu, misalin irin waɗannan mutane sun haɗa da Nelson Mandela na Africa ta Kudu, Kamal Ataturk na Turkey, Mao Zedong na China, Mahatma Gandhi na India, Kwame Nkurumah na Ghana, Julius Nyerere na Tanzania, Thomas Sankara na Burkina Faso, Jamal Abdulnasir Na Masar, Patrice Lumumba na Congo da dai sauransu. A baya-bayannan akwai Lee Kuan Yew na Singapore, Hugo Chaves na Venezuela, Mikael Gorbachaev na Russia da makamantansu. Duk da cewar wasu shugabannin su kan kafa tarihi na din-din-din sakamakon kasancewar sune sahun farko tun a lokacin da ƙasashensu suke tasowa, kuma tsarin da suka bi wajen kafa wannan tarihi yanzu babu shi; misali, yawancinsu sun yi gwagwarmayar kafa ƙasashensu, yaƙin neman ‘yancin kai daga zalunci ko mulkin mallaka, jagorantar wani juyin juya hali ko kuma yaƙin ƙwato ƙasar daga wani mawuyacin hali wanda yanzu kusan duk babu irin waɗannan abubuwa. To amma,  a kan samu wasu nagartattu mutane su biyo bayansu kuma su kamanta irin nasu ƙoƙarin, wani lokacin ma har su kere su. Misali, a ƙasar Ghana, bayan Kwame Nkurumah, an samu Jerry Rawlings wanda ake wa kallon ya bar tarihi mai kyau.  A ƙasar amurka, shekaru masu yawa bayan kashe shugaba abin alfahari Abraham Lincoln wanda ya shiga tarihi, an samu John F. Kennedy wanda shi ma ana ganin an kashe shi ne a tsaka da lokacin da yake kafa tarihi ta hanyar canza Amurka.

A nan Arewacin Najeriya, su waye ake ganin sun kwatanta kamar Sardauna, Tafawa Balewa da Malam Aminu Kano? Akwai dalilai da yawa da suka taru suka bai wa Sardauna wannan kyakkyawan mazauni da yake da shi a tarihin Arewa da Najeriya baki ɗaya. Na farko dai yana daga cikin sanannun masu ilimin zamani na sahun farko a Arewa kuma yana daga cikin waɗanda suka yi gwagwarmayar samo ‘yancin kan ƙasa da kafa siyasu na wancan lokaci. Bayan haka, ya zamo Pirimiyan yankin Arewacin Najeriya gabaɗaya, yankin da yafi kowanne yanki girma da yawan ƙabilu. A wancan lokaci, idan aka haɗa yankunan Yamma, Gabas da kuma Yamma maso Tsakiya da suke a Kudancin Najeriya, duk basu kai girman ƙasa, yawan jama’a da yawan ƙabilun Arewa ba. Bayan haka, Sardauna ya samu nasara ƙwarai da gaske wajen haɗa kan kusan dukkan jama’ar Arewa wajen zama tsintsiya-maɗaurinki-ɗaya, duk kuwa da bambance-bambancen ƙabilu da addini. Banda haka, Sardauna ya gina mutane da yawa daga ko’ina a Arewa, ya ɗaga su a duniya kuma ya jawosu jikinsa sannan kuma alherinsa ya watsu kusan ko’ina ba tare da ya dunƙule shi a waje ɗaya irin yadda shugabannin yanzu suke yi ba. Banda haka, Sardauna wanda dama basarake ne, yana da ƙarfin faɗa-a-ji da tasiri mai yawa a gwamnatin tsakiya ta wancan lokaci wacce take ƙarƙashin Sir Abubakar Tafawa-Balewa, kasancewar jam’iyyarsu ta Mutan Arewa wato NPC, ita ce take da rinjaye a wancan lokaci.

Wani abu da ya ƙara jaddada matsayin Sardauna a cikin tarihi shi ne mutuwarsa a yayin da yake tsaka da bauta wa jama’arsa. Wannan ita tasa shi ya zamo gwarzo na din-din-din. Idan muka bibiyi tarihin duniya, zamu ga mafi yawancin ‘yan gwagwarmaya da jajirtatattun  shugabannin da suka tsaya a kan gaskiya duk kashe su ake. A wancan lokacin, sojoji masu juyin mulkin shekarar 1966 sun kashe Sardauna da Tafawa-Balewa amma ba tare da sun kashe wasu daga cikin takwarorin siyasarsu na kudu ba, musamman ma yankin Inyamurai; duk kuwa da cewa suma suna cikin hamshaƙan masu riƙe da madafun iko a siyasance na wannan jamhuriya ta farko. Wannan, ita tasa har gobe ake yi wa wannan juyin mulki kallon wanda aka yi shi da manufa ta ƙabilanci da ɓangaranci, kodayake waɗanda suka shirya juyin mulkin sun sha musanta hakan tare da nacewa a kan cewa sun yi ne don kishin ƙasa. Abubuwan da suka biyo bayan juyin mulki na farko da kuma na biyu wanda ya yi sanadiyyar mutuwar Shugaba Aguiyi Ironsi watanni shida a tsakani su suka haddasa yaƙin basasar 1967 da ya yi sanadiyyar asarar ɗumbin rayuka da dukiya tare da taɓarɓarewa da lalacewar alaƙa da dangantaka a tsakanin ‘yan Najeriya. Tun daga wannan lokaci zuwa yanzu, har yanzu Najeriya ta kasa hawa kan turbar haɗin kai da ci gaba mai ɗorewa. Ko shakka babu, da ba a yi juyin mulkin farko ba, da yanzu ba haka Najeriya take ba.

Mai yiwuwa masu juyin mulkin Janairun 1966 sun ɗauka cewar kisan da suka yi wa Sardauna da Tafawa Balewa tamkar sun tozarta su Sardaunan ne, amma basu san cewar sun share musu fagen shiga tarihi bane. Domin lokutan da suka biyo bayan kashe sun, duk lokuta ne kusan na rikici da lalcewar al’amura waɗanda garama a ce basu riskesu ba. Cif Awolowo ya rayu kusan shekaru 20 bayan kashe Sardauna kuma sau biyu yana takarar shugaban ƙasa tare da Shagari amma ba ya samun nasara. Dakta Nnamdi Azikwe ya rayu shekaru 30 bayan kashe su Sardauna kuma shima ya jarraba zama shugaban ƙasa amma abin ya ci tura kuma tun yana da rai ma sai da Ojukwu da tsohon mataimakin shugaban ƙasa Alex Ekweme suka dusashe farin jininsa da tasirinsa a tsakanin al'ummarsa ta Igbo a lokuta daban-daban. Su Sardauna, Allah bai rayasu sun kai wani zamani da za a dinga labarin wani basu ba. Wannan ce tasa har gobe ake labarinsu.

Daga Arewacin Najeriya, bayan Sardauna da Tafawa-Balewa, an samu wasu nagartattun mutane waɗanda suka shahara duk da cewar basu kai kamar su Sardaunan ba. Akwai Malam Aminu Kano, Hassan Usman Katsina, Murtala Ramat Muhammad da Janar Muhammadu Buhari. Labarin salon siyasa, hikima, ƙaunar talakawa da iya mu’amala irin ta Malam Aminu Kano, babu inda bai game ba a faɗin Najeriya. Yunƙurin kawo gyara da gaggawa, tsayuwar daka da jajircewa, rashin amincewa da wargi ko rashin gaskiya irin na Murtala Muhammad, babu wanda bai ji labarinsu ba. Masana tarihi su kan kwatanta watanni shidan da ya yi yana mulki a mastayin masu matuƙar amfani da tasiri ga Najeriya. Mutuwarsa ta girgiza kowa ba ma a Nejeriya kawai ba, har a faɗin Afrika baki ɗaya. Yaƙi da zamba, cin hanci, rashawa da cin amanar ƙasa; ƙoƙarin kawo tsarin ɗa’a da martaba gwamnati da kuma farfaɗo da tattalin arziƙi irin na Janar Buhari a 1984 sun sa kowa shiga taitayinsa. Shigarsa siyasa a 2002 da kuma rawar da ya taka a cikin ta, ta sanya shi zamowa ɗaya daga cikin ‘yan siyasar da ya fi kowa yawan magoya baya talakawa zalla a tarihin Africa. An yi ittifaƙin cewar banda  Nelson Mandela, da wahala a samu mutum ɗaya tilo da ya kai Buhari farin jini a tarihin siyasar Africa.

A wannan zamanin da muke ciki, mafi yawan shugabanni a Arewacin Najeriya a dukkan matakai, basu damu da kafa wani tarihi ba. Abin da suka fi damuwa dasu sune tsananin kwaɗayin mulki, fafutukar samun muƙami ko ta halin ƙaƙa, tara ɗumbin dukiya ta hanyar sata da zamba, murƙushe ‘yan adawa, bautar da talakawa, kewaye kansu da ‘yan bani-na-iya da bambaɗanci, haɗa ƙarya da gaskiya ba kunya ba tsoron Allah, da kuma ƙaƙaba ‘ya’yansu da ‘yan korensu a kan muƙamai na siyasa. Wannan shine halin da muka samu kanmu.  A wannan halin, ta yaya za a taɓa samun magadan Sardauna, Tafawa-Balewa, Aminu Kano, Murtala Muhammad da Janar Buhari? A wannan halin, ta yaya Najeriya da Arewa zasu gyaru? A wannan halin, ta yaya talakawa zasu shaƙi iskar ‘yanci da fahimtar makomarsu da ta ƙasarsu? A wannan halin, ta yaya shugabanni zasu samu irin girmamawa da karramawar da su Sardauna suka samu? A wannan halin, wane mai kyakkyawan hali ne zai yi kwaɗayin shiga a dama da shi a harkar gwamnati?

Allah sarki, bayan tafiyar Sardauna, Arewa ta zama koma baya; Najeriya ta zama abin tausayi; mulki ya koma wasan yara; talakawa da mabiya sun koma kwaɗayayyu masu tarewa a gindin masu muƙamai a maimakon masu kishin ƙasa da neman ci gaba. Wasu daga cikin irin shugabannin yanzu, nagartarsu ba ta kai a basu koda masinja ba a lokacin su Sardauna, yau sune gwamnoni, ministoci, ‘yan majalisu, ciyamomi, kansiloli, kai har ma da shugabannin ƙasa. Waɗanda burinsu su saka riga su kece raini, babu talakawa kwata-kwata a gabansu, yau sune masu faɗa-a-ji a ƙasarmu Najeriya. Yau an wayi gari, an fi buƙatar a yi amfani da sunan Sardauna fiye da a yi koyi da shi. Yau an wayi gari, shugabanni basa tuna Sardauna sai sabgar siyasa ta tashi.  

Kungiyar haɗa kan Arewa wato Arewa Consultative Forum (ACF) tayi yunƙuri daban-daban wajen farfaɗo da daraja da martabar Arewa tare da haɗa kan mutanenta tun lokacin da aka kafa ta, amma abin ya ci tura. Ai ƙungiya ba gwamnati ba ce. Mafi yawan gwamnonin Arewa masu riƙe da madafun iko, siyasa ce kawai a gabansu, ba wai haɗin kan Arewa ba. Ba damuwar mafi yawancinsu bane a samu zaman lafiya, a bunƙasa ilimi kuma a haɓɓaka tattalin arziƙin Arewa ba. Wasu daga cikinsu ma da su aka yi amfani aka rusa Arewar da sunan siyasa.

Allah Ya ji ƙan Sir Ahmadu Bello, Sardaunan Sokoto tare da sauran mazan jiya; ba rabo da gwani ba, mayar da kamarsa.

Shafin Mallam Amir a Twitter shine: @AmirAbdulazeez  

©Mujallar Mikiya, 2016. A nemi izini kafin a sarrafa.