Fassara

Sunday, April 17, 2016

Shekara ɗaya a Gwamnatin APC: Ko Kwalliya ta Fara Biyan Kuɗin Sabulu?

10 Ga Afrilu, 2016


Daga: Amir Abdulazeez

R
anar 28 ga watan Maris aka gudanar da zaɓen shugaban ƙasar da ya kafa tarihi a Najeriya. Zaɓen da ya yi sanadiyyar kawar da jam’iyya mai mulki ya kawo jam’iyyar adawa kan mulki a karo na farko a  tarihin dimokraɗiyyar Najeriya. Haƙiƙa irin wannan ba ta cika faruwa ba a Nahiyar Afrika tun daga lokacin da turawan mulkin mallaka suka bai wa ƙasashen nahiyar ‘yancin kai har zuwa yau. Hasalima, kullum al’amuran zaɓuka ƙara lalacewa suke yi saboda ƙudurin da mafi yawan shugabannin Afrika suke da shi na dauwama a kan mulki.

Jam’iyyar APC ta ɗare kan mulki bayan tsawon shekaru 12 da jam’iyyun adawa suka shafe suna fafutukar ganin sun kawar da PDP daga mulki ba tare da sun samu wata ƙwaƙƙwarar nasara ba. Bayan kujerar shugaban ƙasa, ta kuma samu nasarar kafa rinjaye a Majalisar Wakilai ta Tarayya da kuma Dattijai ta Sanatoci. Bugu da ƙari, ta samu damar kafa gwmanati a jihohi 23 cikin 36 da ake dasu a ƙasar nan. Saboda haka tun daga sama har ƙasa, sama da 65% na madafun ikon gwamnatocin ƙasarnan a hannun jam’iyyar yake kai tsaye.

Daga kafa gwamnatin APC zuwa yanzu, aƙalla an samu shekara ɗaya; wannan na nufin cewar jam’iyyar ta cinye kashi ɗaya bisa huɗu na wa’adin da ‘yan Najeriya suka zaɓe ta tayi. Sakamakon haka, akwai buƙatar a kalli irin jagorancin da gwamnatin ta APC ta gabatar a tsawon wannan lokaci domin ganin ko kwalliya ta fara biyan kuɗin sabulu. Kafin a yi hakan, akwai buƙatar a yi waiwaye adon tafiya don ganin irin rawar da PDP ta taka a tsawon shekaru 16.

Tsakanin Gyara da Kuma Ɓarnar PDP
A jimlace zamu iya cewar, PDP ta gaza, nesa ba kusa ba wajen ciyar da Najeriya gaba a tsawon shekaru 16 da ta yi tana mulki domin kuwa mafi yawan matsalolin da muke ciki a 1999 a lokacin da jam’iyyar ta fara mulki, sune dai suke damunmu har a shekarar 2015 da ta bar mulki. To amma kuma, duk da tarin ɓarna da lalata ƙasa da mafi yawancin ‘yan Najeriya suke kallon jam’iyyar PDP ta yi, akwai wasu abubuwa na kirki da ta taɓuka. Babu shakka dole mu yarda cewar PDP ta taka rawar gani sosai wajen lalata al’amuran zaɓe da nagartacciyar dimokraɗiyya a ƙasarnan tare da ɗaukaka matsayin cin hanci da rashawa da yi wa doka karan tsaye a Najeriya. To amma ta wani ɓangare, PDP ɗin, musamman  a ƙarƙashin jagorancin Obasanjo da ‘Yaradua, ta taimaka wajen farfaɗo da tattalin arziƙin ƙasa. Misali, lokacin da Obasanjo ya karɓi mulki a hannun sojoji, asusun ajiyar Najeriya na ƙasar waje, abin da yake cikinsa bai wuce  dala biliyan huɗu ba kacal, amma lokacin da ya bar mulki zuwa lokacin  da ‘Yaradua ya rasu, akwai sama da dala miliyan 60 a cikin wancan asusu.
Kodayake ana kallon Jonathan a matasayin wanda yafi kowa ɗaurewa cin hanci da rashawa gindi, amma alokacinsa ne zaɓuka suka fara gyaruwa, abinda har ya kai ga samar da ingantaccen zaɓen da ya kawar da shi daga mulki.
Duk da irin wadaƙa da kuɗin gwamnati da ake kallon PDP ta yi, akwai abubuwa da ta tafi ta bari wanda APC zata iya ɗorawa a kai.

Halin da APC ta Samu da Najeriya
Jam’iyyar APC ta karɓi Najeriya a lokacin da ƙasar take cikin wani mawuyacin hali. Farko dai akwai rarrabuwar kai da ƙin jinin juna bisa dalilai na addini da ƙabilanci da ya kai matakin ta’azzarar da bai taɓa kaiwa ba tun bayan gama yaƙin basasa na Biafra a shekarar 1970. Bayan haka, akwai faɗuwar farashin man fetur wanwar wanda wani lokaci tsakanin shekarar 2009 zuwa 2013, farashin gangarsa guda ɗaya ta kai dalar Amurka 100 zuwa 140. A kwanakin baya, ganga ɗaya sai da ta kai dala 30, a yanzu ana sayar da ita tsakanin dala 39 zuwa 41. Wannan na nufin cewar kuɗin shigar Najeriya ya ragu da kaso kusan biyu bisa uku. Jam’iyyar APC ta samu Najeriya a cikin badaƙƙaloli daban-daban na almundahana da kuɗin ƙasa, ta samu an yi wa asusun ƙasa wakaci ka tashi tun daga kan matakin tarayya har zuwa jihohi.
Jam’iyyar APC ta gaji babbar matasala wacce ita ce ta harkar tsaro. Daga cikin wannan matsala akwai Boko Haram, fashi da makami, satar shanu, garkuwa da mutane, tada zaune tsaye a yankin Niger-Delta, satar ɗanyen mai, bangar siyasa, faɗan Fulani makiyaya da manoma, rikice-rikicen addini da na ƙabilanci a sassa daban-daban da dai sauransu.
Jam’iyyar ta gaji sauran matsaloli waɗanda suka haɗa da rashin ɗorarren samuwar man fetur, dogaron tattalin arziƙin ƙasa a kan man fetur, durƙushewar noma, rashin wadatacciyar wutar lantarki, rashin ingancin noma da masana’antu da dai sauransu.

A ina APC ta Samu Nasara Cikin Shekara Guda?
Duk da yake ba zai yiwu a ce an ga ƙwaƙƙwaran sauyi a cikin shekara guda ba, amma an ce wai Juma’ar da zata yi kyau, daga Laraba ake gane ta. Abu na farko muhimmi da gwamnatin APC ta fara yi shi ne wajen taimaka wa jihohi 27 da maƙudan kuɗaɗe a matsayin rance domin su samu su biya tarin albashin da ma’aikatansu suke binsu na wata da watanni. Wannan ta taimaka wajen ceto mafi yawan jihohin da ƙananan hukumominsu daga faɗawa mawuyacin hali.
Gwamnatin Tarayya ta APC ta taka rawar gani ta fuskar yaƙi da Boko Haram, duk da dai cewar har yanzu akwai matasalar a Arewa maso gabashin ƙasarnan amma nasarar da aka samu a bayyane take. Sai dai kuma a sauran matsalolin tsaro irinsu satar shanu, rikicin Fulani da manoma, garkuwa da mutane, har yanzu gwamnatin tana da sauran aiki a gabanta.
Jam’iyyar APC ta duƙufa gadan-gadan wajen yaƙi da cin hanci da rashawa musamman wajen tuhumar jami’an gwamnatin da suka gabata. Misali shine yadda gwamnatin ta bankaɗo badaƙƙalar sayen makamai a ofishin Sambo Dasuki da kuma yadda EFCC ta samu wani sabon ƙarfi wajen tuhuma da gurfanar da waɗanda ake tuhuma da satar dukiyar gwamnati a gaban kotu. Sai dai kuma wani hanzari ba gudu ba shine, gwamnatin har yanzu ba ta samu nasarar tabbatar da ko da mutum ɗaya a matasyin mai laifi ba a gaban kotu a tsawon sheka guda. Idan aka tafi a haka, mutum nawa zata samu damar kammala shari’unsu a cikin shekaru huɗu? Bayan haka, ana zargin gwamnatin da ƙyale wasu shafaffu da mai ‘yan jam’iyyar APC tare da maida hankali a kan ‘yan adawa kawai. Sannan kuma ana ganin gwamnatin a wasu lokuta ba ta yin biyayya ga umarnin kotu a wannan yaƙi da take yi.
Duk zaɓukan cike gurbi da aka gudanar a ƙarƙashin Hukumar Zaɓe ta mulkin APC, an kwatanta adalci. Ko jama’iyyar adawa ta PDP zata shaidi hakan. Wannan nasara ce babba.
Wata nasara kuma ita ce, yadda gwanatin take ƙoƙarin tsaftace al’amaura a dukkan matakai na gudanarwa. Banda haka, ƙimar Najeriya ta farfaɗo ƙwarai da gaske a idon duniya a ƙarƙashin jam’iyyar APC, duk da cewa wasu suna sukar Shugaba Buhari a kan yawan tafiye-tafiye da yake yi zuwa ƙasashen ƙetare.

A Ina Matsalolin APC Suke a Shekara Guda?
Gwamnatin jam’iyyar APC ta ɗauki sama da watanni shidan farkon mulkinta tana jan ƙafa da sanɗa; ta shafe tsawon wannan lokaci ba tare da ministoci da sauran jami’an gwamnati ba. Wannan ta taimaka ƙwarai wajen kawo wa gwamnatin cikas a kan tafiyar da aiyukanta. Har kawo yanzu akwai naɗe-naɗen masu muhimmanci da gwamnatin take ta jan ƙafa wajen yinsu.
Bayan haka, gwamnatin tarayya ta APC har yanzu bata yi wani yunƙuri ba a hukumance na ganin ta haɗa kan ‘yan Najeriya duba da yadda kawuna suka rarrabu a kan siyasa, addini, ƙabilanci da ɓangaranci dab da zaɓen shekarar 2015. Wannan rarrabuwar kai har yanzu tananan tana ƙara cigaba, kuma ɗaya daga cikin sakamakonta kuwa shine sabon yunƙurin kafa ƙasar Biafra da aka taso da shi ‘yan satattaki kaɗan bayan kafa sabuwar gwamnatin. Bugu da ƙari, ‘yan Kudu suna yi wa gwamnatin kallon kamar tana fifita ‘yan Arewa.
Babbar matasalar gwamnatin jam’iyyar APC ita ce yadda ta kasa shawo kan matsalar man fetur a Najeriya wacce ake ta fama da ita. Banda haka, ta kasa tsayawa a kan wata tartibiyar manufa dangane da sashen man fetur. Yau ta faɗi wani abu, gobe kuma sai ta canza, jibi kuma sai ta aikata wani abin daban.
Dangane da tattalin arziƙi, gwamnatin ta kasa shawo kan tashin farashin Dalar Amurka da sauran kuɗaɗen ƙara waje da muke tsananin buƙata domin sayo kayayyaki daga waje. A gefe ɗaya kuma, tsadar kayayyaki sai ƙara ta’azzara take yi.    
Kasafin kuɗin 2016 wanda shine na farko da jam’iyyar APC ta yi a mulkinta yazo da kura-kurai da aringizo da yawa-wani abu da ba a yi tsammaninsa a gurin gwamnati mai taƙama da gaskiya da riƙon amana ba.


Me ya kamata APC ta Yi?
Har yanzu jam’iyyar APC tana da sauran shekaru uku a cikin huɗun da aka zaɓeta ta yi; akwai buƙatar ta yi waiwayen watannin da ta shafe  a kan mulki kuma ta yi wa kanta alƙalanci da kanta. Inda ta yi kurakurai, to ta yi ƙoƙari da gaggawar gyarawa, inda ta samu nasara sai ta yi ƙoƙarin ɗorawa a kai.
Maganganu da ƙulle-ƙullen siyasar 2019 da suka dabaibaye jam’iyyar tun kafin a je ko’ina, kamata ya yi a ajiye su waje ɗaya, ‘yan jam’iyyar su haɗa kai don ganin sun sauke nauyin da jama’ar Najeriya suka ɗora musu tukunna.
Yana da kyau jam’iyyar ta bar ƙofarta a buɗe wajen karɓar shawarwari komai ɗacinsu kuma koda daga wurin maƙiyansu ne. Bayan haka kuma ya kamata su sani cewar lokaci ba abokinsu bane a yanzu, dole sai sun zage damtse.


©Mujallar Mikiya 2016

Tuesday, April 5, 2016

Ko Tinubu Zai Tsaya Takarar Shugaban ƙasa?

04 Ga Afrilu, 2016


Daga: Amir Abdulazeez

A
gurin mafi yawan manazarta harkokin siyasar Najeriya, ba wai abin da Tinubu yake buƙata shine abin tambaya ba; wataƙila tambayar ita ce, ko Tinubu zai samu abin da yake buƙata? Kasancewar gwamnatin Shugaba Buhari ta kammala kusan dukkan wasu muhimman naɗe-naɗen muƙamai ba tare da an ji sunansa a ko ɗaya daga ciki ba, alama ce da take nuna cewar akwai wani abu daban kuma babba da Asiwajun yake hari.

Yunƙurin Bola Tinubu a kusan tsawon shekaru goma da suka gabata na ganin ya zama Mataimakin Shugaban ƙasar Najeriya, wani abu ne da kusan duk wani mai sanya idanu kan harkokin siyasa yake sane da shi. Wannan yunƙuri nasa, duk da ya jawo masa abubuwa daban-daban na cigaba da kuma cikas, amma ya yi sandiyyar zamansa wani ƙusa kuma jigo a matakin ƙasa. Labari ya yi ta kewayawa cewar, ƙoƙarin da Tinubu ya yi na zama ɗan takarar mataimaki ga tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa Atiku Abubakar a ƙarƙashin tsohuwar jam’iyyar Action Congress (AC)  a zaɓen Shugaban ƙasa na shekarar 2007 shi ya kawo rashin jituwa tsakaninsu wanda har ta kai ga Atikun ya bar jam’iyyar AC ɗin ya koma PDP a shekarar 2008-matakin da har yanzu yake bibiyarsa har kawo yau kuma wasu suke ganin ya taka wata ‘yar rawa wajen rashin nasarar Atikun wajen samun tutar takarar APC a shekarar 2015. An rawaito cewar shi Atiku yana ganin ba a yi adalci ba idan aka bai wa Bayerabe ko ɗan kudu maso yamma takarar mataimakin shugaban ƙasa a dai-dai lokacin da Shugaba Obasanjo wanda yake Bayerabe ne shima yake kammala shekaru 8 a kan mulki. Don haka Atiku sai ya bada mamaki wajen ɗaukar Sanata Ben Obi wanda ba a sani ba sosai daga kudu maso gabashin Najeriya a maimakon Tinubu wanda shi ya yi uwa yai makarɓiya wajen ganin shi Turakin Adamawa ɗin ya samu tikitin AC cikin sauƙi, bayan PDP ta yi masa wulaƙanci.

Rahotanni sun nuna cewar rashin amincewar Buhari na ya ajiye Fasto Tunde Bakare ya ɗauki Tinubu, ita ta kawo rugujewar ƙoƙarin haɗewa ko dunƙulewa tsakanin tsofaffin jam’iyyun CPC, ANPP da ACN a shekarar 2011 domin tunkarar Jonathan da PDP. Daga baya Buhari ya yi masa biyan bashi a 2015 inda ya yi wa Tinubu tayin bashi abinda bai samu damar bashi ba a 2011. To amma Jagaban Borgun yana sane da matsala da tarnaƙin da tsayar da Musulmai zalla za ta iya kawo wa damar da jam’iyyar APC take da shi na cin zaɓen shugaban ƙasa. Tinubu ya bai wa mutane mamaki wajen danne kwaɗayinsa tare da miƙa sunan tsohon kwamishinansa Farfesa Yemi Osinbajo a matsayin ɗan takarar mataimakin shugaban ƙasa. Mutane da yawa suna kallon Osinbajo a matsayin wanda kawai yake riƙe da waccan kujera a madadin jagoran APC ɗin na ƙasa.

Me yasa Tinubu ya dinga fafutukar zama mataimakin shugaban kasa, ba ji ba gani? A tarihin dimokraɗiyyar Najeriya, da wahala a samu wani wanda ya ƙaunaci zama mataimakin shugaban ƙasa kamar sa. Amsar ba wata mai wahala bace; magana ce ta dabarar siyasa, me yiwuwa yana son zama shugaban ƙasa kuma yana so ya bi ta hanya mafi sauƙi, wacce ita ce ya fara zama mataimakin shugabn ƙasa. Tinubu ya samu damar da zai tsayar da kansa ɗan takarar shugaban ƙasar jam’iyyar ACN a shekarar 2011, amma bai yi hakan ba, me yiwuwa saboda ya san ɓata lokaci ne kawai kuma ƙila ba kamar sauran ‘yan siyasa ba, shi ba burinsa kawai  ace ya taɓa takarar shugaban ƙasa ba. Bayan haka kuma bai yi wani yunƙuri na zama mataimakin Nuhu Ribaɗu ba, wanda jam’iyyar ACN ɗin ta bai wa takarar shugaban ƙasa a wancan lokaci. Kodayake hakan bai ba wa mutane mamaki ba.
Dukkan jama’a, ciki har da Tinubu shi kansa sun san cewar zai yi matuƙar wahala ga wani mutum ɗan kudu maso yamma ya zama shugaban ƙasa kai tsaye a nan kusa, duba da cewar Obasanjo ya riga ya yi mulki na tsawon shekaru 8 a cikin 16 ɗin da aka yi da dawowar dimokraɗiyya a madadin wannan yankin. Da alama dai Asiwaju ya sadaukar da burinsa na zama mataimakain shugaban ƙasa a shekarar 2015 domin tabbatar da nasarar jam’iyyar APC, sai dai kuma ba za a fitar da ran cewar kuma a ƙarshe zai tsaya takarar shugaban ƙasar kai tsaye ba a shekarar 2019. Idan Buhari ya yanke shawarar ba zai nemi zango na biyu ba, to tamkar ya share wa Tinubu hanyar zama ɗan takarar jam’iyyar APC ne a 2019.

Idan Tinubu ya samu nasarar zama shugaban ƙasa, hakan zai zamo wani sakamako ko lada na tsawon lokaci da aka ɗauka ana tsare-tsare, haƙuri, surƙullen siyasa, zuba jari da kuma sadaukarwa. Tushen kafuwar sansanin siyasa da ƙarfin faɗa-a-jin tsohon gwamnan Jihar Lagos ɗin wanda yake ƙara faɗaɗa a kullum, ya samo asali ne daga kasancewarsa gwamna ɗaya tilo wanda ba na PDP ba a yankin Kudu maso yamma da kuma ɗaya cikin biyu a yankin Kudancin Najeriya baki ɗaya bayan zaɓukan shekarar 2003 da kuma jajircewarsa da fafutuka wajen ganin an fatattaki PDP daga yankinsa na Yarabawa tare da tabbatar da siyasar adawa a ƙasa baki ɗaya.

Wasu na kallon rashin karɓar wani muƙami a gwamnatin Buhari kawo yanzu daga ɓangaren Tinubu, kamar wani abu ne da zai iya haifar masa da matasala; wasu kuwa suna ganin hakan ma ƙarfi zai ƙara masa. Masu kallon hakan a matsala suna ganin cewar waɗansu mutane da suke cikin gwamnatin Buhari zasu yi amfani da muƙamansu wajen yin aikace-aikacen da zasu birge Buharin ta yadda zai yi tunaninsu a matsayin waɗanda zasu gaje shi domin ɗorawa a kan manufofin gwamnatinsa, hakan kuwa zai kawar da Tinubu daga lissafi. A ɗaya ɓangaren, wasu na ganin cewar rashin karɓar wani muƙami zai sa Tinubu ya mayar da hankali kan siyasarsa kuma zai raba kansa da duk wata badaƙƙala mai alaƙa da aikin gwamnati. Sannan kuma jam’iyyar APC  zata cigaba da jin cewar har yanzu yana binta bashin da baza ta iya biyansa ba. Bayan haka matasayinsa na kafi-sarki zai ci gaba da ɗorewa.

Ko shakka babu, ƙudurin Tinubu na zama shugaban ƙasa, akwai yiwuwar ya gamu da ƙalubale daban-daban. Akwai muhimman mutane da mai yiwuwa su nemi yin takara da shi tun ma daga yankinsa na kudu maso yamma. Muhimman Yarabawa irinsu Babatunde Fashola, Kayode Fayemi ko ma Yemi Osinbajo, duk zasu iya nuna sha’awarsu ga kujerar shugaban ƙasa. Muhimman ‘yan jam’iyyar APC daga yankin kudu maso gabas na Inyamurai kamarsu Chris Ngige, Ogbonnaya Onu da Rochas Okorocha suma zasu iya cewar to idan har mulki zai dawo kudu ne, to kamata yayi a ce kudu maso gabas zai dawo ba kudu maso yamma ba. Duk da irin shahararren gangancin siyasa da ragon azancin da kudu maso gabas suka yi a zaben shekarar 2015, zasu iya kallon Tinubu a matsayin wanda ya hana a basu kujerar mataimakin Shugaban ƙasa kuma zasu tashi tsaye a kansa wajen ganin bai ƙara hanasu wata damar ta samun kujerar mataimakin shugaban ƙasar ba, da ma ƙila ta shugaban ƙasar baki ɗungurugum a shekarar 2019. Wata mishkila da Tinubu zai iya fuskanta ita ce yankin Arewa wanda zai iya cewa idan har Buhari ba zai yi zango na biyu ba, to dole a ƙyale wani daga yankin aƙalla ya ƙarashe mulkin na tsawon shekaru huɗu. Mutane irinsu Atiku Abubakar, Bukola Saraki, Rabi’u Kwankwaso, Nasir El-Rufa’i da kuma wasu gwamnonin APC ɗin da suka gama zangonsu na biyu duk zasu yi yunƙurin gwada damarsu idan hakan ta faru.

Kasancewar mafi yawan jam’iyyar APC a aljihun Tinubu take, zai zamo riba a gareshi sosai, to amma kuma zai iya zamo masa matsala. Ya tara maƙiya da yawa a ƙoƙarinsa na baza ƙarfin ikonsa zuwa ko’ina a cikin jam’iyyar. Babu wani mutum da ya cicciɓa kuma ya sassaka yawan mutane a cikin shugabancin jam’iyya da gwamnati kamarsa, kuma bisa ga dukkan alamu, zai iya samun goyon bayan Buhari. Sai dai kuma, kankanewarsa da babbakewarsa a kowanne bangare da kuma ƙoƙarin zama mai ruwa da tsaki a kan duk wani abu zai iya kawo masa tarnaƙi. Yanzu haka rahotanni sun fara kewayawa cewar, wasu jiga-jigan APC sun fara tunanin barin jam’iyyar saboda irin ƙarfin da Tinubu yake da shi. Kwanakin baya, an kawo masa cikas a yunƙurinsa na ƙaƙaba wa Majalisun Tarayya shugabanci; idan bai bi a hankali ba, ɓangarori da yawa a cikin APC zasu dunƙule waje ɗaya domin su yi masa taron dangi a 2019.

©Mujallar Mikiya, 2016.

Twitter: @AmirAbdulazeez