Fassara

Sunday, August 9, 2015

Bambamcin Ɗan Kauye da Ɗan Birni a Dawakin- Tofa: Gaske Ko Gangan?

                                                                                                                                                                             17th October, 2013.

Daga: Hamza Ibrahim Baba

Ƙ
aramar Hukumar Dawakin-Tofa na ɗaya daga cikin ƙananan hukumomi mafi daɗewa a Jihar Kano, kai har da ma Najeriya gabaɗaya domin kuwa tana daga cikin farkon ƙirƙirowa tun sanda aka fito da tsarin ƙananan hukumomi a ƙasarnan a shekarar 1976.
Allah (SWT) Ya albarkanci Dawakin-Tofa da ƙasar noma mai tarin yawa da kuma ƙwari domin kuwa girman ƙasar Dawakin-Tofa ya kai murabba’in kilomita ninki 479 ko kuma 479km2. Bayan haka tana maƙotaka da manya-manyan matattarar ruwa da aka fi sani da dam da ake ji da su a Kano kamar su Watari, Thomas da  Bagwai. Wannan ƙaramar hukuma tana da arzikin ƙasar laka wacce ake iya yin gini da ita kuma ake iya yin tukwane da sauran dangogin ta da ita banda kuma tarin ma’adinai a ƙarƙashin ƙasa waɗanda rashin maida hankali irin na gwamnatocin tarayya bai bari an ganosu ba.

Idan ka bar ɓangaren albarkatun ƙasa, ka koma siyasa da gwamnati, Dawakin-Tofa uwa ce ga Mataimakan Gwamnonin Jihar Kano guda uku wanda har a halin yanzu ma ɗan Dawaki ne ya ke riƙe da wannan kujera, kai a taƙaice ma tun da aka dawo dimokraɗiyya a shekarar 1999, mutum ɗaya ne (Abdullahi T. Gwarzo) wanda ba ɗan Dawaki ba da ya riƙe wannan kujera. Mutanen da suka riƙe wannan kujera sun haɗa da Alhaji Abdu Dawakin-Tofa a lokacin Abubakar Rimi, Injiniya Magaji Abdullahi a lokacin Mallam Shekarau da kuma Dakta Abdullahi Umar Ganduje a lokutan Mulkin Kwankwaso na farko da na yanzu. Bayan haka sau biyu ana ɗaukar Saleh Shehu Kwuidawa a matsayin  ɗan takarar Mataimakin Gwamna amma Allah bai sa an kai ga nasara ba. Bayan wannan , Abdu Dawakin-Tofa ya taɓa riƙe muƙamin Gwamna na wucin-gadi lokacin da Abubakar Rimi ya yi murabus, kun ga a taƙaice, mun taɓa samun Gwamna kenan. Sannan kuma akwai tsofaffin kwamishinoni da masu ci yanzu da muka taɓa samu tun ma lokacin mulkin soja. Wasu daga cikinsu sun haɗa da Injiniya Magaji Abdullahi, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, Alhassan Muhammad Dawaki da kuma Soveya Muhammad Yahaya Nadu. Kai a taƙaice, da wahala wata gwamnati ta zo ta ƙare ba tare da ɗan Dawaki ya samu kwamishina ba.

Idan muka duba cikin tarihi, ƙaramar hukumar Dawakin-Tofa tsohuwar cibiya ce ta mulki, al’ada, hukunci, addini da sauran aiyyukan nagarta. A ƙarshe-ƙarshen  shekarun 1960 da kuma farkon shekarun 1970, ƙananan hukumomi irin su Bichi, Tsanyawa, wani ɓangaren Gwarzo, Bagwai, Rimin-Gado da Tofa duk a ƙarƙashin Dawakin-Tofa suke. Don haka babu shakka waɗannan ƙananan hukumomi ba za su  iya rubuta tarihinsu ba, ba tare da sun ambaci muhimmancin Dawakin-Tofa ba.
A wancan lokaci, muhimman garuruwa a wannan yanki sune Bagwai, Ƙwa, Gogori, Dawaki,  Rimin-Gado, Shanono, Bichi, Doka, Tofa, Gadanya, da dai sauransu.

A ƙarshen shekarun 1950 da farkon shekarun 1960, lokacin da ake mulkin gundumomi wato native authority an ɗauki tsakiyar garin Dawaki saboda sauƙaƙa al’amuran mulki, shugabannin lokacin sun yi amfani da cikin garin Dawaki a matsayin babban birni domin mulkar ragowar garuruwan da na ambata a sama. Wannan shine dalilin da ya sa Dawaki ta kasance matattarar mahukunta, alƙalai da sauran masu mulki irinsu Makaman Kano, Madakin Kano da sauransu. 
Tunda iyaye da kakkanin Yolawa na yanzu da yawa, tushensu yana garuruwa irinsu Dawaki da Ƙwa sai aka dinga turosu aiki waɗannan garuruwa domin a ƙara samun  kyakkyawar alaƙa tsakanin talakawa da masu riƙe da mulkin gargajiya.

Tunda Dawaki itace cibiyar mulki, sai ya zamanto a cikinta akwai alƙalai da mahukunta waɗanda ba ‘yan asalin Dawakin ba kuma ba su da masaniya akan Dawakin-Tofa sosai. Waɗannan  mahukunta, su aka ɗorawa alhakin yin sulhu da hukunci a tsakanin mutane. Don haka dukkan wata rigima da ta shafi gona, aure ko sata da ta faru a ƙauyuka da garuruwa na kusa to a cikin garin Dawaki ake yin shari’arsu. Kuma wannan shine abinda ake yi a dukkan Arewacin Najeriya inda ake yin shari’a a kowacce cibiyar mulki.

Amma a nan Dawaki, akwai ƙorafe-ƙorafe na zalunci da aka zargi alƙalai waɗanda dama ba ‘yan asalin ƙaramar hukumar Dawakin-Tofa ba ne suna yiwa talakawa kamar ƙwace filaye da gonakai, azabtarwa, raba aure da dai sauransu. Waɗannan zarge-zarge waɗanda ma ba’a tabbatar da su ba, sune wasu ‘yan siyasa masu son zuciya marasa kishi suka fake da su wajen cimma manufarsu. Waɗannan zarge-zarge da ba’a magance ba tun a baya, su ne sannu a hankali suka kawo rabuwar da ta samar ta taken ƊAN BIRNI da ƊAN ƘAUYE.

Wannan take yana da ma’ana a siyasance, domin kuwa masu ganin cewa mutanen cikin Dawaki sun zalunci iyayensu saboda lokacin akwai dama a hannunsu sai suke kiran dukkan wani ɗan cikin garin Dawaki da Ɗan Birni sannan kuma wanda ba ɗan cikin garin Dawaki ba shi kuma>  Ɗan Ƙauye. To wai menene ma’anar > Ɗan Ƙauye da >  Ɗan Birni?
> A binciken da na yi a cikin kundin samar da ma’anar kalmomi na Encarta Dictionaries, ‘birni’ shine wani babban gari mai manya-manyan gine-gine da tarin jama’a, shi kuma ‘ƙauye’ shine wani guri mai ƙunshe da gidaje marasa yawa ko kuma ƙananan gidaje kuma babu tarin jama’a kamar birni. >kuma kauye shinekk

Daga wannan ma’anoni, sai mu ga cewa to menene bambancin cikin gari da kuma wajen Dawaki? Gine-ginemu, abincinmu, tufafinmu, sana’o’inmu, nomanmu, abincinmu, uwa uba addininmu duk iri ɗaya ne. To me ya maida ɗan cikin Dawaki Ɗan Birni? Menene birnin a > Dawaki? Maganar gaskiya ita ce dukkan mu mutanen ƙauye ne. Idan ka ɗauke cibiyar mulki ta ƙaramar hukuma, babu wani abu da Dawaki za tace wai tana mora fiye da garuruwan da suke kewaye da ita. Idan ma za’a faɗi gaskiya, a matsayin Dawaki da take a lungu sai dai ma a kirata ƙauye idan aka haɗa ta da garuruwa irin su > Dawanau, Bagadawa, Tumfafi, Ƙwa, Dungurawa da Gwamai domin su a sarari suke kuma akan manyan titunan tarayya. Don haka sun fi Dawakin damar zama birane a nan gaba.>

Ni bana tare da dukkan wani ɗan Dawakin da yake kallon akwai bambancin birni da ƙauye a wannan ƙaramar hukuma tamu, wajibi ne mu da muke cikin Dawaki mu yi ƙoƙarin rungumar maƙotanmu> . Bayan haka kuma akwai wasu manya a Dawaki waɗanda ba su damu da haɗin kai ba kuma a baya sun taka muhimmiyar rawa wajen tarwatsa duk wani yunƙuri na sulhu domin su cimma manufofinsu na siyasa. Irin waɗannan manya su ne suke cin ribar siyasa ta hanyar yaɗa ƙiyayya a zuciyar mutane.
Halin da muka samu kanmu a yanzu shine, wasu ‘yan siyasa marasa kishi a ciki da wajen garin Dawaki suna amfani da wannan rauni na alaƙa dake tsakanin yaranmu da manyanmu domin cigaba da raba kawunanmu akan wata shiririta ta banza da hofi.
Wannan rashin hangen nesan namu, shi ya daɗe yana daƙile ƙoƙarin da mutanen kirki masu son kawo gyara musamman a siyasance. Waɗancan masu hana ruwa gudu, kullum aikinsu shine su raba kawunan mutanen>  Dawakin-Tofa.

Ƙananan hukumomi irinsu > > Bichi,Dambatta,Gwarzo da Wudil sun jima da wuce irin wannan shashancin, sun maida abin tarihi. Suna kallon kansu a matsayin uwa ɗaya uba ɗaya a duk inda suka samu kansu a > KanoKano, Abuja, Kaduna ko Lagos.>  
Tambayar da zanyi wa dukkan ‘yan ƙaramar hukumar>  nan ita ce: shin wannan rarrabuwar kawunan namu, taimakonmu ta yi ko kuma cutarmu? Wacce riba wani mai mulki ko daga cikin Dawaki ko daga wajenta zai ƙaremu da ita idan ya cika aljihunsa da kuɗaɗenmu, mu kuma muna can muna faɗan ƙabilanci? Shin za mu iya maganin wannan matsalar> ? Idan wannan rabuwar kan namu gangan ce, to mecece mafita wajen hana yaɗata?

Maganin waɗannan matsaloli ba waɗanda za su gagaremu ba ne. Dole ne mu ɗauki Dawakin-Tofa a matsayin ƙaramar hukumarmu wacce ba mu da wadda ta fi ta. Dole mu yi watsi da mutane masu son raba kanmu kuma mu nuna musu yanzu tunaninmu ya wuce da saninsu.>  kuma mu nuna musu yanzu tunaninmu ya wuce da s
Dole mu wa’azantar da kanmu akan kyakkyawan shugabanci kuma mu ƙalubalanci masu raba kanmu da su nuna mana cigaban da suka kawo mana yayin da suka samu dama?>

Abin da muke buƙata yanzu shine shugabanni nagari, masu gaskiya koma daga ina suke a > Dawakin-Tofa, waɗanda za su gina mana makarantu su cikasu da malamai da kayan aiki, waɗanda za su ciyar da mu gaba. Babu ruwanmu da inda shugabannin suka fito, daga>  Buruntumau ko Romi, > Jemomi ko ‘Yanrutu, Dandalama ko Gabari, Dawaki ko Gudau, babu ruwanmu.

Muna buƙatar shugabannin da za su zuba jari a ilimi. Bara na faɗa muku, ilimi haske ne kuma shine kaɗai zai cetomu daga wannan shashancin. Ilimi shi zai ‘yantamu da ‘ya’yanmu daga sharrin masu sace mana dukiyoyinmu da ranar Allah Ta’ala kuma su shigo cikinmu da dadare su ce da mu wai mu ‘yan ƙauye ne ko ‘yan birni.>

Cin kashin ya isa haka, dole mu taru mu jajirce muce ba mu yarda ba. Mu haɗa kanmu, mu yaɗa soyayya a tsakaninmu, mu matsa lamba har sai an bamu ruwan sha, makarantu, tituna da kuma asibitoci. 
>Haƙƙi ne a kan mu mu kashe wannan koma bayan na>  Ɗan Ƙauye da Ɗan Birni kuma mu ɗabbaka kyakkyawan shugabanci, gaskiya, riƙon amana da kuma haɗin kai.
>  Allah (SWT) Ya umarcemu a gurare daban-daban a cikin Alƙur’ani Mai Girma kan mu zama masu haɗin kai da taimakon juna.>  
Ko dai mu ɗauki mataki yanzu, ko kuma mu cigaba da tafiya a cikin wannan dambarwar.

Malam Amir Abdulazeez shi ya fassara daga Turanci zuwa Hausa.


No comments:

Post a Comment