Fassara

Tuesday, August 11, 2015

Gwamnonin Najeriya da Mataimakansu: Wasa Tare, Ci Ban-Ban

20 ga Janairu, 2014

Daga: Amir Abdulazeez

L
okaci ya yi da ya kamata mu tambayi gwamnonin Najeriya a kan dalilin da ya sa ba sa so mataimakansu su gaje su. Ko kuma su mataimakan gwamnonin, mu tambaye su laifukan da su ka yi wa iyayen gidan nasu da har tsananinsu ya kai su ke ƙyamar su gaji kujerunsu.
Tun da aka kafa jamhuriya ta huɗu, bayan da mulkin dimokraɗiyya ya dawo a shekarar 1999 har zuwa yanzu, mataimakin gwamna ɗaya ne tak ya taɓa gadar kujerar gwamnansa kai tsaye tare da goyon bayan mai gidan nasa, wannan kuwa shi ne tsohon mataimakin gwamnan Jihar Zamfara kuma tsohon gwamnan Jihar, Alhaji Mahmuda Aliyu Shinkafi wanda ya karɓi mulki a hannun Sanata Ahmad Sani Yariman Bakura.

Akwai tsirarun mataimakan gwamnonin da su ka gaji gwamnonin nasu amma a cikin yanayi na rikicin siyasa ko baram-baram ko kuma a dalilin wani tsautsayi da ya ratsa. Misali, Goodluck Jonathan ya gaji Diepreye Alamasiegha a matsayin gwamna bayan da Majalisar Dokokin  Jihar Bayelsa ta tsige gwamnan kan zargin cin hanci da rashawa, Mukhtar Ramalan Yero na Kaduna ya zama gwamna bayan da Sir Patrick Yakowa ya rasa ransa a hatsarin jirgin sama, Adebayo Alo Akala na Jihar Oyo ya zama gwamna na ɗan wani lokaci bayan da  Majalisar Dokokin jihar ta tsige Gwamna Rashidi Ladoja kafin daga baya kotu ta dawo da shi kan kujerarsa, Michael Botmang na Jihar Plateau wanda ya rasu kwanannan, ya zama gwamna na ɗan wani taƙaitaccen lokaci bayan da Majalisar Dokokin Jihar ta tsige Gwamna Joshua Dariye kafin daga bisani kotu ta dawo da shi kan kujerarsa, Uwargida Virgin Etiaba ita ma ta zama gwamna bayan Majalisar Dokokin Jihar Anambra ta tsige Mr. Peter Obi kafin kotu ta rushe wannan tsigewa,  Aliyu Wammako ya zama gwamnan Sokoto sakamakon baram-baram ɗin da su ka yi da maigidansa Bafarawa inda ta kai shi ga komawa PDP shi kuma Bafarawan ya na sabuwar jam’iyyar da ya kafa ta DPP, Ibrahim Gaidam na Jihar Yobe ya zama gwamna bayan da Gwamna Mamman Ali ya yi mutuwar ba-zato-ba-tsammani. Babu wasu alamu da su ka nuna cewa waɗannan mutane za su samu sahalewar iyayen gidansu wajen zama gwamnoni kafin waɗancan dalilai. Yanzu haka a Jihar Taraba, ba a son ran Gwamna Suntai da mutanensa, Mataimakin Gwamna Garba Umar ya ke riƙe da ragamar Jihar ba, duk kuwa da cewa shi Suntai ɗin ya na can rai a hannun Allah.

Bayan wannan, mun ga irin yadda wasu gwamnoni su ka dinga zaman doya da manja da mataimakansu, a wasu lokutan, kawai saboda mataimakan sun nuna sha’awar su gaje su. Akwai Jihar da aka ce gwamnan ya hana mataimakinsa ko da takarar sanatan da ya nema ba ganin cewa ba za a ba shi takarar gwamna ba, bisa dailin cewa wai bai kamata a ce shi ya na sanata kuma mataimakinsa ma ya na sanata ba. Ƙiriiri ya ɗauko wani can ya ba shi takarar. Wani lokacin ma gwamnonin su kan tilasta wa mataimakan nasu barin kujerunsu a kan wannan dalili ko kuma a kan wani dalili daban kamar yadda mu ka gani kwanannan a Jihar Imo tsakanin Rochas Okorocha da mataimakinsa. Irin haka ta faru a Jihar Jigawa a lokacin Saminu Turaki wanda a shekara takwas, ya yi mulki da mataimaka kusan uku da kuma a Jihar Bauchi tsakanin Mallam Isa Yuguda da Garba Gadi. A wasu jihohin irin su Kano, mun ga yadda Mallam Shekarau ya ƙare zangunan mulkinsa cikin yanayain rashin jituwa da mataimakansa guda biyu.

Wani lokacin yanayin ya kan nuna tamkar laifin na mataimakan gwamnonin ne, to amma mun ga yadda wasu mataimakan su ka dinga biyayya sau da ƙafa har tsawon shekaru takwas ga ma su gidan nasu, wani lokacin wannan biyayya ba irin baƙin jinin da ba ta janyo mu su, amma sai biyayyar ta tashi a banza. Maimakon gwamnonin su bai wa mataimakan nasu damar su gaje su, sai ka ga sun ɗauko kwamishina, sakataren gwamnati ko shugaban jam’iyya su saka a gaba. A wasu lokutan ma sai su ɗauko wani can daban su kawo. Misali a nan, Marigayi Yakowa ya na nan zaune, amma Ahmed Makarfi na Kaduna ya ɗauki tsohon kwamishina Namadi Sambo ya ba shi takarar gwamna kuma aka sa Yakowan ya bi shi a matsayin mataimaki, Abdullahi Gwarzo na Kano na nan kuma ya na nema amma Shekarau ya ɗauko kwamishina Salihu Takai ya ba shi takara, Gwamna Abdulfatah Ahmed na Jihar Kwara tsohon kwamishinan Bukola Saraki ne, Gwamna Shettima na Jihar Borno tsohon kwamishinan Ali Modu Sheriff ne, Gabriel Suswam na Jihar Benue tsohon ɗan Majalisar Wakilai ta Tarayya ne kuma ya samu goyon bayan Gwamna George Akume, Gwamna Babangida Aliyu na Jihar Niger tsohon Babban Sakatare ne a Ma’aikatar Birnin Tarayya Abuja, Gwamna Liyel Imoke na Jihar Cross-Rivers tsohon sanata ne kuma ya samu goyon bayan Gwamna Donald Duke. Misalan su na nan birjik, amma ba za ka ji tsohon mataimakin gwamna ba. Da alama dai kwamishinoni sun ma fi ƙima a idon gwamnonin fiye da mataimakan nasu.

Sashe na 187 na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999 ya bayyana mataimakin gwamna a matsayin wanda kujerar gwamna ba ta samuwa da kuma tafiyuwa sai da shi. Hakan na nuna cewar a tsarin aiki, babu wani makusancin gwamnan kuma abin amincewarsa kamar mataimakinsa. Haka zalika, bayan gwamnan, babu wanda ya san sirrin gwamnatin kamar mataimakinsa. To, amma, me ya sa gwamnoni ba sa son ba su dama? Wani ma ya na karɓar kujerar mataimakin ne tun farko bisa tunanin cewa idan zangonsu ya ƙare, mai gidansa zai ba shi dama, amma ina. A tunaninmu irin na talakawa, mun ɗauka wanda ku ka yi aiki tare kafaɗa da kafaɗa na tsawon shekaru huɗu ko takwas, ai ba wanda zai ɗora a inda ka tsaya kamar sa.

To wai, ko shin mataimakan ne ba su da farin jinin cin zaɓe, shi ya sa gwamnonin su ke ƙin tsayar da su? Ko kuwa dama wani dalili ne irin na siyasa ya tilasta wa gwamnonin ɗaukar mataimakan nasu tun farko amma ba su ne zaɓin su ba? shin gwamnoni su na tunanin mataimakan nasu za su ci amanar su bayan sun gaje su?  Shin biyayya da mu ke gani a fili mataimakan na yi wa gwamnoninsu, a fili ta ke kawai, amma a ɓoye abin ba haka ya ke ba. Shin gwamnonin, mugunta da baƙin ciki su ke yi wa mataimakan nasu don kar su taka irin matasyinsu ko kuwa su na tsoron ba za su iya juya su ba ne bayan sun gaje su?

Ni dai, ba zan iya bayar da waɗannan amsoshi ba, wataƙila sai su gwamnonin da mataimakan nasu, amma na taɓa ji daga majiya mai tushe, lokacin da wani mataimakin gwamna ya ke miƙa mulki a ofishinsa ga wani sabon mataimakin gwamnan a wata jiha, sai ya ke ce ma sa: ‘ɗan uwana, babu aiki mai wahalar riƙewa a siyasance irin na mataimakin gwamna. Domin kuwa, idan gwamna ya yi bajinta sai jama’a su yabe shi shi kaɗai, amma idan ya yi kuskure, sai a zageku tare’.

Hasashen da manazarta siyasar ƙasar nan su ke yi shi ne, a wannan karo ma gwamnoni da dama ba za su bai wa mataimakansu damar su gaje su ba a zaɓen 2015. A wsu jihohin ma hakan ta fito fili ko kuma gwamnonin sun bayyana wa mataimakan nasu a baki ko a aikace cewar ba za su gaje su ba. Wannan abu dai ya na da ɗaure kai musamman idan aka yi la’akari da abin da ya ke faruwa a siyasun wasu ƙasashe. Mislali, tun a farkon mulkin Marigayi Nelson Mandela, ya fara assasawa a aikace cewa mataimakinsa Thabo Mbeki shi zai gaje shi, kuma shi ya gaje shi ɗin. A ƙasar Amurka, duk da cewa su ma mataimakan ba su fiya gadar masu gidan nasu ba, amma George Bush (babban) ya gaji shugaba Ronald Reagan bayan da ya yi masa mataimaki na tsawon shekaru takwas kuma tare da goyon bayan mai gidan nasa. Shugba Bill Clinton ya goya wa mataimakinsa Al-Gore baya inda har ya samu takara a jam’iyyarsu, duk da cewa bai lashe zaɓen ba a shekarar 2000. To amma mu a nan Najeriya, ba haka abin ya ke ba. Wasu gwamnonin ma da gangan su ke ɗaukar rarraunan mataimaki, a wasu lokutan ma tsoho ko rago wanda ba ma zai yi sha’awar ya gaje su ba.

Yanzu dai mun zuba ido a shekarar 2015 mu ga ko za ta canza zani duk da cewa babu alamun hakan. Idan har ba ta canza zani ba, to duk mai sha’awar zama gwamna a rayuwarsa, a yanzu ko a gaba, ya yi tunani mai zurfi kafin ya karɓi kujerar mataimakin gwamna idan an yi masa tayi tun da dai ƙarfin gwamnonin Najeriya a siyasance, idan ya na yawa, har ya yi yawa, su kuma ba su yarda mataimakinsu ya gaje su ba.

© Malam Amir Abdulazeez 2014.


No comments:

Post a Comment