Fassara

Tuesday, August 11, 2015

KANO 2015: Amfani da Rashin Amfanin Ganduje ko Takai a Mulkin Jihar

6 Ga Afrilu, 2015

Daga: Amir Abdulazeez

Idan dai ba wani ƙadaru na Ubangiji ba, Ranar Asabar mai zuwa, ɗaya daga cikin mutum biyu ne za a zaɓa a matsayin magajin Gwamnankwankwaso; wato Dakta Abdullahi Umar Ganduje ko Malam Salihu Sagir Takai.
To, amma kafin Ranar Asabar ɗin ta yi ‘yan Jihar Kano su yanke hukunci, ga wani hasashe a kan amfani da rashin amfanin zaɓar kowannensu;

Amfanin Zaɓar Ganduje
1. Idan aka zaɓi Ganduje a matsayin gwamnan Kano, to an zaɓi jam’iyyar APC sak tun daga tarayya har jiha. Mai yiwuwa wannan za ta bai wa Jihar Kano wata gagarumar damar amfanar aiyuka da alfarmomi masu yawa daga Gwamnatin Tarayya.
2. Gwamnati kamar wata mota ce kullum akan titi, take tafiya izuwa wani waje, idan an samu canjin direba, ana so ace ta ci gaba da tafiya akan wata kyakkyawar turba guda ɗaya har a cimma manufar ci gaban al’ummar da aka sa a gaba. Babu shakka Ganduje zai ci gaba da aiyukan Kwankwaso, wataƙila tamakar ma ba a samu wani canjin direba ba ma.
3. Ganduje dattijo ne wanda dukkan alamu na haƙuri da juriya suka bayyana a tattare da shi. A ko’ina an san dattijo da haɗa kan jama’a cikin hikima, dabara da nagarta, ina kuma ga idan an ba shi shugabancin su?
4. Ganduje ƙwararre ne kuma gogaggen ma’aikaci mai tarin ƙwarewa ta kusan shekaru 40 a kan ilimi, aikin gwamnati, siyasa, shugabanci da zamantakewa. In dai ƙwarewa dai-dai ta ke da aiki, to babu shakka, Ganduje zai kasance wanda ya fi kowa aiki a matasyin gwamna a Najeriya.

Matsalolin Zaɓar Ganduje
1. Idan aka zaɓi Ganduje, zai kasance jam’iyyar APC ta cinye komai aKano, babu sauran wata jam’iyyar adawa. Yanzu haka APC ita ta ke da Shugaban ƙasa, Sanatoci 3, ‘Yan majalisun tarayya 24 duka, Ciyamomi 44 da kansiloli 484 duka. Illa ce babba a ce babu adawa ko kaɗan; za a wayi gari jam’iyya mai mulki ta na yin abin da ta ga dama ba ta shayin komai kuma ba ta tsoron kowa.
2. Duk da nasarorin gwamnatin Kwankwaso, akwai wasu manyan kura-kurai da ta yi waɗanda bisa ga alama Ganduje zai iya ɗorawa a kansu. Babba daga cikinsu shi ne tauye ƙananan hukumomi, hanasu kuɗaɗensu da kuma mayar da su hoto.
3. Ganduje ya shafe kusan shekaru 20 (tun DPN 1996) ya na neman gwamna bai samu ba. A tsawon wannan lokaci, ya sadaukar da lokacinsa, ƙarfinsa, dukiyarsa, tunaninsa da sauran abubuwansa da yawa akan wannan buƙata. Babu tabbacin cewar idan ya samu nasara ba zai fi myar da hankali wajen ƙoƙarin mayar da gurbin abubuwan da ya rasa ba a tsawon wannan lokaci.
4. Bisa ga alamu, tsananin haƙuri da kawaicin Ganduje sun haifar masa da rauni, wanda zai iya yin illa ga irin salon shugabancinsa. Bayan haka, shekaru kusan 16 da ya shafe a ƙarƙashin Kwankwaso sun bayyana shi a matsayin tamkar wani mutum wanda ba shi da cikakken ra’ayin kansa ko ba zai iya tsayawa da ƙafafunsa ba.



Amfanin Zaɓar Takai
1. Idan aka zaɓi Takai, to an samar da canji a sama, canji a ƙasa. Hakan zai bayar da damar cewa kowanne ɓangare za su amfani mulki ba tare da ya tattare a waje ɗaya ba, balle har a samu shantakewa ko kama-karya.
2. Kano, yanzu a tamke ta ke tamau kuma ta na buƙatar a ɗan sassauta kaɗan. Gwamnatin Kwankwaso ta fi mayar da hankali akan gine-gine da manyan aiyuka. Takai, kamar yadda ya ke faɗa, ya na da burin ya karkatar da akalar manufar gwamnati domin ta fi mayar da hankali akan gina jama’a, sauƙaƙa musu da kuma taimaka musu, taimakawa ma’aikata, taimakawa marasa ƙarfi, kula da noma da kiwon lafiya da sauransu.
3. Ga dukkan alamu, Takai a matsayin gwamna zai sakarwa ƙananan  hukumomi mara su yi fitsari. Yanzu ƙananan hukumomi a mace suke murus, akwai buƙatar a farfaɗo da su in dai ana so ci gaba ya kai can ƙasa wajen jama’a da sauran marasa galihu.
4. Alamun nutusuwa, yakana da kirki sun bayyana a tattare da Takai. Bayan haka an shaideshi kan gaskiya da riƙon amana- duk waɗannan abubuwa jari ne a harkar shugabanci. Bayan haka, kasancewarsa mai matsakaicin shekaru  wanda ya ke da sauran siyasa a gaba, zai so ya yi abubuwan da zai kafa tarihi mai kyau.

Matsalolin Zaɓar Takai
1. Akwai alamun cewar iyayen gidan jam’iyyar PDP na Kano ba za su bar Takai ya sarara a mulkin Kano ba. Kasancewar sun rasa Gwamnatin Tarayya, duk za su iya dawowa Kano su tare akan ta da buƙatu iri-iri.
2. Akwai masu tsoron cewar Takai ba zai iya aikin gwamna yadda ya kamata ba, kasancewar gogewarsada ƙwarewarsa basu kai yadda ake so ba, musamman idan aka yi la’akari da cewar Kano ba ƙaramar jiha ba ce kamar Yobe, Zamfara, Ekiti ko Ebonyi ba.
3. Kwankwaso ya ɗora Kano akan wata miƙaƙƙiyar hanya, akwai tsoron cewar Takai zai iya karkacewa izuwa wata hanyar daban ko ya mayar da hannun agogo baya.
4. A siyasar wannan zamani, mun ga tasirin ɗaukar nagartaccen mataimaki. Saɓanin irin Mataimakin Ganduje, Mataimakin Takai ba shi da wata nagarta sosai. Abin Allah Ya kiyaye, idan wani tsautsayi ya samu gwamna, da yawa ba za su gamsu da Abba Risqua a mulkin Kano ba.


© Malam Amir Abdulazeez 2014. 

No comments:

Post a Comment