Fassara

Tuesday, August 11, 2015

DAWAKIN-TOFA: Siyasa ko Masifa?

10 Ga Satumba, 2014.

Daga: Amir Abdulazeez

K
u yi m in  afuwa idan kalmar ‘masifa’ da na yi amfani da ita a wannan sharhi ta yi tsauri da yawa. Amma magana ta gaskiya,  da wahala a iya amfani da wata kalmar ba ita ba wajen kwatanta ko bayyana irin yanayin da masu juya akalar siyasar Dawakin-Tofa suka sanya ta a ciki.
Kimanin sati uku da suka gabata, wani bawan Allah da muka fara mu’amala da shi a shekarar bara ya tare ni a gidan wani ɗaurin aure. Bayan mun gaisa, sai ya bani haƙuri bisa ƙauracemin da ya yi na kwana biyu. Yace ya ƙauracemin  ne saboda dalili na siyasa, domin wai ya na tsoron kada waɗanda ya kira iyayen gidansa na siyasa a Jam’iyyar APC ta Dawakin-Tofa su gane ya na mu’amala da ni ko kuma mutane iri na, su saka ƙafar wando ɗaya da shi, wai tunda a cewarsa da ni da jaridar da na ke wallafawa, ana yi musu kallon masu adawa da Maigirma Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, Dakta Abdullahi Umar Ganduje da kuma wasu masu juya akalar APC a Dawakin-Tofa.

Da farko dai na so na tsare shi sai ya bayyana min abin da ni na yi ko jaridar wanda ya ke nuna ana adawa da Gandujen ko kuma da su iyayen gidan nasa, to amma sai na ga hakan ɓata lokaci ne, ba lallai ne in samu wata gamsuwa ba. Kawai sai na yi masa godiya , muka yi sallama, muka rabu ina jin tausayinsa bisa wannan hali da aka saka shi  ko kuma ya saka kansa a ciki.
Bayan ‘yan kwanaki da faruwar wannan sai na haɗu da wani mai riƙe da muƙami a gwamnatin ƙaramar hukumar Dawakin-Tofa ya na bayyana wa wani abokinsa (shi ma wani shahararraen ɗan siyasa) cewar iyayen gidansa sun shaida masa cewar kada ya ƙara alaƙa da wannan abokin nasa, idan ba haka ba zai ji a jikinsa. Waɗannan mutane biyu abokai ne shekara da shekaru kuma tare suka yi makaranta amma duk da wannan, wai ba a tunanin cewar wata hulɗar daban za ta iya haɗasu wadda ba ta siyasa ba. Kai in ma hulɗar siyasa za su yi tare, to sai me? Wai yaushe siyasa ta koma gaba ne. Wanna masifa da me ta yi kama?

Kwanakin baya aka dinga yaɗa labari cewar Honarabul Kawu Sumaila, ɗan takarar Gwamnan Jihar Kano, ya kira dukkan shugabannin mazaɓu na Jam’iyyar APC na ƙananan hukumomi 44 na Jihar Kano, amma wai sai aka hana na Dawakin-Tofa zuwa. Abin haushi da kunya, na ƙananan hukumomi 43 sun je amma ban da na Dawakin-Tofa.  Wannan ko mun ƙi ko mun so, saƙon da muke isar wa da duniya shi ne har yanzu Dawakin-Tofa siyasar gaba, duhun kai da jahilci muke yi ko da kuwa hakan ba gaskiya ba ne. Shin suna tsammanin da haka za a taimaki takarar Gandujen? Yanzu idan Maigirma, Dakta Ganduje ya kira shugabannin Sumaila suka ƙi zuwa, mu ‘yan Dawakin-Tofa ya za mu ji a ranmu? Idan kuma Kawu Sumailan Allah Ya ba wa Gwamnan Kano, ya ake tunanin zai ɗauki ‘yan Dawakin-Tofa misali? A siyasance don kana son wani, ba za ka yi mu’amala da kowa ba kenan?
Ya kamata Maigirma Mataimakin Gwamna ya tsawatarwa waɗannan mutane masu kiran kansu muƙarrabansa ko kuma masu sawa da hanawa a jam’iyyar APC ta Dawakin-Tofa, waɗanda su ake zargi da aikata irin waɗannan abubuwa. Idan kuma da yawunsa da yardarsa suke yin hakan , to sai a yi mana bayani domin mu san yadda abin ya ke. Ita dai gaskiya matuƙar ɗaci ne da ita, kusan kowa ba ya so a faɗa masa ita, amma idan ya daure ya karɓe ta ya yi amfani da ita, sakamakon ta zai zamo masa mai zaƙi.

Akwai buƙatar mu tuna cewar, shi goyon baya da haɗin kan jama’a, ba a samunsa ta ƙarfi, ana samunsa  ne a siyasance ta hanyar kyautatawa da laluma. Ko’ina sai ɓatawa Ganduje suna a ke yi da sunan tallata shi, kuma wannan ba ƙaramar mummunar illa ba ce ga wanda ya ke neman Gwamnan Kano ba wai Gwamnan Dawakin-Tofa, kuma a shekarar 2015 ba wai 2019 ba. Idan har muka ga shiru ba a samu gyara ba ko kuma ba a tsawatar ba, to za mu ƙaddara cewar Maigirma Ganduje shi ya ba su izinin duk wannan abu da suke yi.

Shi jagoranci da ɗaukaka, Allah Ne Ya ke ba da su, don haka mun yarda waɗannan mutane tauraruwarsu ita ta ke haskawa kuma lokacinsu ne, kuma su ne jagorori. To amma ya kamata su yi amfani da wannan dama don su bar kyakkyawan tarihi ta hanyar kawo gyara da cigaba, amma ba su dinga kama-karya, son zuciya tare da haddasa gaba a tsakanin jama’a ba.

Haka kawai yanzu an ɗauko wani salo, idan ka na neman wani muƙami na siyasa, sai a ce wai ai ba ka son Ganduje don haka a yaƙe ka, ko kuma a ce Ganduje ba kai ya ke so ba, don haka wai aikin banza ka ke, da kai da banza duk ɗaya,  ba za ka ci ba. To ko an manta cewar Allah Shi ya ke bayar da mulki? Duk wanda ya ke kan wata dama a yanzu, akwai wanda ya kai shi idan ba Allah ba? To ya kamata a sani, Ganduje uba ne, kuma mu a tunanin mu matsayinsa ya wuce a ce wai ya na son wane ko bay a son wane. Ya kamata a ce kowa na sa ne, kai har wanda ma ba ɗan jam’iyyarsa ba.
Dawakin-Tofa ƙaramar hukuma ce mai ɗumbin tarihi da daraja ba ma a Jihar Kano ba, a’a har a Najeriya baki ɗaya. Ta na daga cikin ƙananan hukumomi ƙirƙirar farko a Najeriya baki ɗaya kuma ita uwa ce da ta haifo kuma ta raini wasu ƙananan hukumomi irin su Bagawai, Tofa da Rimin-Gado. Amma abin takaici, yanzu dariya su ke mana suna cewar muna ƙarƙashin siyasar mulkin-mallaka, siyasar rashin ‘yanci da tsoro da danniya.

Wannan ƙaramar hukuma ba mallakin wani ba ce, ta mu ce baki ɗaya kuma haƙƙin mu ne  mu haɗu tare mu ga cewar mun ciyar da ita gaba. Amma idan wani ko wasu suna ganin cewa Dawakin-Tofa mallakar su ce kuma za su tilastawa mutane ta ƙarfin tsiya su yi abin da suke so, to ba kansu farau ba, kuma sai mu ce mu su: ‘Allah Ya bada sa’a’, gas u ga ‘yan Dawakin-Tofar nan, ai kowa ya san inda ya ke masa ciwo.

© Malam Amir Abdulazeez 2014.


No comments:

Post a Comment